Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Jirgin Alhazan Kano Na Farko
Published: 15th, May 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da jirgin farko na maniyyatan jihar Kano da ke niyyar gudanar da aikin hajjin bana.
Gwamna Abba Kabir Yusif, wanda ya samu wakilcin mataimakin gwamna, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya bukaci maniyyatan da su kasance jakadu na gari a jihar, su kuma yi addu’ar zaman lafiya, ci gaba, da hadin kan jihar Kano da Nijeriya baki daya.
Ya jaddada kudirin gwamnati na tallafa wa duk maniyyata a duk tsawon zamansu a kasa mai tsarki.
Tun da farko, Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammad Sanusi II, ya shawarci alhazai da su kwantar da hankulansu, su kuma maida hankali wajen gudanar da ibada.
A nasa jawabin babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya bayyana cewa jirgin na farko ya hada da mahajjata daga kananan hukumomi goma sha daya (11):
Ajingi: Mahajjata 15 (maza 10, mata 5)
Tofa Mahajjata 17 (maza 12, mata 5)
Tudun Wada: Mahajjata 115 (maza 84, mata 31)
Karamar Hukumar Doguwa: Mahajjata 94 (maza 73, mata 21)
Karamar Hukumar Bebeji: Mahajjata 82 (maza 67, mata 15)
Garin Malam: alhazai 47 (maza 33, mata 14)
Gaya: Mahajjata 14 (maza 10, mata 4)
Karamar Hukumar Madobi: Mahajjata 36 (maza 21, mata 15)
Karamar Hukumar Kabo: Mahajjata 18 (maza 13, mata 5)
Wudil 36 Alhazai
(Maza 30, mata 6)
Rimin Gado: Mahajjata 33
Karin bayani: Jami’an gwamnati 15 da jami’an kasa 10 ne ke raka mahajattan domin kula da ayyukan alhazai.
Alhazai 560 ne ake jigilarsu a wannan jirgi na Max Air zuwa filin jirgin saman Yarima Mohammed Bin Abdulaziz dake Madina, wanda ya tashi da misalin karfe 12:11 na rana laraba.
Alh. Lamin Rabi’u Danbappa ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Alhaji Abba Kabir Yusif ta yi duk wani shiri da ya dace domin tabbatar da walwala da jin dadin alhazai.
Taron ya samu halartar wasu daga cikin manyan jami’an gwamnati da suka hada da shugaban hukumar gudanarwar hukumar Alhaji Yusif Lawan, da ‘yan kwamitin, kwamishinoni, da masu ba da shawara na musamman.
Abdullahi jalaluddeen Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayar da gargadi game da hawan keken masu kananan shekaru da rashin biyayya ga fitilun ababen hawa a cikin babban birnin Kano.
Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.
Gargadin na zuwa ne bayan an samu munanan hadurran kan tituna guda 16 a cikin watan Agustan 2025, wanda ya yi sanadin jikkata da asarar dukiyoyi.
Rundunar ta lura cewa hawan keken ƙananan yara yana haifar da babban haɗari ga mahaya da sauran masu amfani da hanyar.
An shawarci iyaye da masu kula da su da su guji barin ‘ya’yansu da ba su da shekaru su yi amfani da keken mai kafa uku, domin hakan zai jawo hukunci mai tsanani a karkashin dokar.
Rundunar ta kuma lura da yanayin rashin biyayya ga fitilun ababen hawa da kuma dokokin hanya daga wasu masu amfani da hanyar.
“Wannan dabi’a tana haifar da cunkoson ababen hawa da ba dole ba, da kuma hadurran da za a iya kaucewa, da jefa rayukan mutane cikin hadari da kuma kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa.”
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kebe jami’an tsaro domin tabbatar da bin ka’idojin zirga-zirga.
Rundunar ta bukaci duk ‘yan kasar da su bi dokokin hanya da kuma bayar da rahoton duk wani abu na hawan keken kanana, tukin ganganci, ko wasu keta haddi.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaro na rayuka da dukiyoyi a jihar.
Abdullahi jalaluddeen/Kano