Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Jirgin Alhazan Kano Na Farko
Published: 15th, May 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da jirgin farko na maniyyatan jihar Kano da ke niyyar gudanar da aikin hajjin bana.
Gwamna Abba Kabir Yusif, wanda ya samu wakilcin mataimakin gwamna, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya bukaci maniyyatan da su kasance jakadu na gari a jihar, su kuma yi addu’ar zaman lafiya, ci gaba, da hadin kan jihar Kano da Nijeriya baki daya.
Ya jaddada kudirin gwamnati na tallafa wa duk maniyyata a duk tsawon zamansu a kasa mai tsarki.
Tun da farko, Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammad Sanusi II, ya shawarci alhazai da su kwantar da hankulansu, su kuma maida hankali wajen gudanar da ibada.
A nasa jawabin babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya bayyana cewa jirgin na farko ya hada da mahajjata daga kananan hukumomi goma sha daya (11):
Ajingi: Mahajjata 15 (maza 10, mata 5)
Tofa Mahajjata 17 (maza 12, mata 5)
Tudun Wada: Mahajjata 115 (maza 84, mata 31)
Karamar Hukumar Doguwa: Mahajjata 94 (maza 73, mata 21)
Karamar Hukumar Bebeji: Mahajjata 82 (maza 67, mata 15)
Garin Malam: alhazai 47 (maza 33, mata 14)
Gaya: Mahajjata 14 (maza 10, mata 4)
Karamar Hukumar Madobi: Mahajjata 36 (maza 21, mata 15)
Karamar Hukumar Kabo: Mahajjata 18 (maza 13, mata 5)
Wudil 36 Alhazai
(Maza 30, mata 6)
Rimin Gado: Mahajjata 33
Karin bayani: Jami’an gwamnati 15 da jami’an kasa 10 ne ke raka mahajattan domin kula da ayyukan alhazai.
Alhazai 560 ne ake jigilarsu a wannan jirgi na Max Air zuwa filin jirgin saman Yarima Mohammed Bin Abdulaziz dake Madina, wanda ya tashi da misalin karfe 12:11 na rana laraba.
Alh. Lamin Rabi’u Danbappa ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Alhaji Abba Kabir Yusif ta yi duk wani shiri da ya dace domin tabbatar da walwala da jin dadin alhazai.
Taron ya samu halartar wasu daga cikin manyan jami’an gwamnati da suka hada da shugaban hukumar gudanarwar hukumar Alhaji Yusif Lawan, da ‘yan kwamitin, kwamishinoni, da masu ba da shawara na musamman.
Abdullahi jalaluddeen Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe, Dokta Aishatu Umar Maigari, ta ce talauci da nuna bambanci na daga cikin manyan dalilan da ke hana yara mata damar samun ilimi a jihar.
Ta bayyana hakan ne a wajen bikin Ranar Yara Mata ’Yan Makaranta ta Duniya ta shekarar 2025, wanda Shirin AGILE tare da Access Initiative Africa da Nudge Initiative suka shirya a Gombe.
Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a BornoA wajen bikin, Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Asma’u Inuwa Yahaya, ta yaba da yadda gwamnatin jihar ke ƙoƙarin tabbatar da cewa ba a bar wata yarinya a baya wajen samun ilimi.
Ta ce Gwamnan jihar, ya bai wa ilimin yara mata muhimmanci, wanda hakan ya sa ake samu ƙaruwa yara mata da ke zuwa makaranta.
Kwamishiniyar, ta ƙara da cewa ma’aikatar ilimi tana aiki wajen samar da sabbin manufofi da tsare-tsare da za su taimaka wajen rage waɗannan matsaloli da tabbatar da damar ilimi ga kowa cikin adalci.
A nata jawabin, Kodinetan Shirin AGILE, Dokta Amina Haruna Abdul, ta ce bikin na bana an shirya shi ne don ƙarfafa gwiwar yara mata wajen ci gaba da neman ilimi duk da ƙalubalen da suke fuskanta.
Ta gode wa Uwargidan Gwamnan da ma’aikatar ilimi bisa goyon bayansu.
Haka kuma, Akawun Majalisar Dokokin Jihar Gombe, Barista Rukayyatu Jalo, ta shawarci yara mata da su dage wajen yin karatu, inda ta bayyana cewa ilimi ne hanyar da za ta gina rayuwarsa.
Wasu daga cikin ɗaliban da suka halarci bikin, sun bayyana farin ciki da godiya kan shirya taron saboda yadda ya ƙara musu ƙwarin gwiwa.
Ɗalibai da dama sun gudanar da muhawara da wasan kwaikwayo a wajen taron.