Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-30@02:12:01 GMT

Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Jirgin Alhazan Kano Na Farko

Published: 15th, May 2025 GMT

Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Jirgin Alhazan Kano Na Farko

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da jirgin farko na maniyyatan jihar Kano da ke niyyar gudanar da aikin hajjin bana.

 

Gwamna Abba Kabir Yusif, wanda ya samu wakilcin mataimakin gwamna, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya bukaci maniyyatan da su kasance jakadu na gari a jihar, su kuma yi addu’ar zaman lafiya, ci gaba, da hadin kan jihar Kano da Nijeriya baki daya.

 

Ya jaddada kudirin gwamnati na tallafa wa duk maniyyata a duk tsawon zamansu a kasa mai tsarki.

 

Tun da farko, Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammad Sanusi II, ya shawarci alhazai da su kwantar da hankulansu, su kuma maida hankali wajen gudanar da ibada.

 

 

A nasa jawabin babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya bayyana cewa jirgin na farko ya hada da mahajjata daga kananan hukumomi goma sha daya (11):

 

Ajingi: Mahajjata 15 (maza 10, mata 5)

 

Tofa Mahajjata 17 (maza 12, mata 5)

 

Tudun Wada: Mahajjata 115 (maza 84, mata 31)

 

Karamar Hukumar Doguwa: Mahajjata 94 (maza 73, mata 21)

 

Karamar Hukumar Bebeji: Mahajjata 82 (maza 67, mata 15)

 

Garin Malam: alhazai 47 (maza 33, mata 14)

 

Gaya: Mahajjata 14 (maza 10, mata 4)

 

Karamar Hukumar Madobi: Mahajjata 36 (maza 21, mata 15)

 

Karamar Hukumar Kabo: Mahajjata 18 (maza 13, mata 5)

 

Wudil 36 Alhazai

(Maza 30, mata 6)

 

Rimin Gado: Mahajjata 33

 

Karin bayani: Jami’an gwamnati 15 da jami’an kasa 10 ne ke raka mahajattan domin kula da ayyukan alhazai.

 

 

Alhazai 560 ne ake jigilarsu a wannan jirgi na Max Air zuwa filin jirgin saman Yarima Mohammed Bin Abdulaziz dake Madina, wanda ya tashi da misalin karfe 12:11 na rana laraba.

 

Alh. Lamin Rabi’u Danbappa ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Alhaji Abba Kabir Yusif ta yi duk wani shiri da ya dace domin tabbatar da walwala da jin dadin alhazai.

 

Taron ya samu halartar wasu daga cikin manyan jami’an gwamnati da suka hada da shugaban hukumar gudanarwar hukumar Alhaji Yusif Lawan, da ‘yan kwamitin, kwamishinoni, da masu ba da shawara na musamman.

 

 

Abdullahi jalaluddeen Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD

Gwamnatin kasar Iran ta kai korafi a gaban hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD dangane da yakin da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar na tsawon kwanaki 12, wanda yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane fiye da 600.

Nasir Siraj wani jami’in ofishin jakadancin Iran a MDD ya mikawa kwamitionan hukumar Volker Türk  a jiya Jumma’a .

Kafin haka dai ministan kiwon lafiya na kasar Iran ya bayyana cewa mutane 627 suka rasa rayukansu a yayinda wasu 4,870 suka ji rauni a yakin kwanaki 12 wanda wadannan kasashe biyu suka keta hurumin sararin samaniyar kasar.  Yakin ya zo karshe ne bayan da HKI ta shelanta tsaida yaki ita kadai.

Korafin ya bayyan cewa abinda wadannan kasashe biyu suka yi ya sabawa dokokin kasa da kasa da dama, daga ciki har da dokar kasa da kasa ta kare hakkin bil’adama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
  •  Iran: Babu Wani Alfanu A Ci Gaba Da Bai Wa IAEA Hadin Kai
  • An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
  • Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
  • WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
  • NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 
  • Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
  • NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?