Majalisar Dokokin Kaduna Ta Amince Da Kudirin Dokar Hukumar Kula Da Manyan Makarantun Sakandire
Published: 15th, May 2025 GMT
Majalisar dokokin jihar Kaduna ta amince da dokar hukumar kula da manyan makarantu ta jihar Kaduna, ta shekarar 2025, ya zama doka. Dokar dai na da nufin daidaita harkokin gudanar da manyan makarantun sakandire a fadin jihar domin daidaita tsarin ilimin zamani.
Da yake jagorantar zaman majalissar, mataimakin kakakin majalisar Mista Henry Magaji Danjuma ya bayyana cewa sabuwar dokar za ta inganta yadda ake gudanar da manyan makarantun sakandire a jihar.
Kudirin dokar ya biyo bayan gabatar da rahoton Barr. Mahmud Lawal Isma’ila, shugaban kwamitin hadin gwiwa kan ilimi da shari’a, kuma wakilin mazabar birnin Zaria. Ya bayyana cewa dokar ta zama dole ne ta hanyar gyare-gyaren nan a tsarin ilimin Najeriya.
“A da, mun gudanar da tsarin ilimi na 6-3-3-4 – na makarantar firamare na shekara shida, kowace shekara uku na kanana da babbar sakandire, sannan a kammala karatun gaba da sakandare na shekara hudu, amma yanzu majalisar dokokin kasar ta sake duba wannan tsarin zuwa tsarin 9-3-4. Wannan ya bukaci shekaru tara na karatun farko (wanda ya hada da firamare da karamar sakandare), sannan kuma na kammala karatun sakandare na shekara 3.” Inji shi.
Ya jaddada cewa tsarin da aka yi wa kwaskwarima ya bukaci kowace jiha ta kafa wata kungiya mai kwazo da za ta kula da manyan makarantun gaba da sakandare, wanda hakan ya sa aka bullo da sabuwar dokar a Kaduna.
Dangane da batun kula da hukumomi kuwa, Isma’ila ya lura cewa hukumar kula da ayyukan malamai ta kasa (TSB) wacce a da ta ke kula da kananan makarantun gaba da sakandare, ba za ta kara kula da manyan makarantun gaba da sakandire ba. Sabuwar Hukumar Ilimi ta Manyan Makarantun Sakandare za ta dauki wannan nauyi.
Ya kara da cewa samar da hukumar ya sa jihar Kaduna ta cancanci samun tallafin daga gwamnatin tarayya. “Ba tare da wata kungiya mai zaman kanta ba, jihohi ba su cancanci samun kudaden shiga tsakani na tarayya ba, da wannan doka jihar Kaduna yanzu ta cika sharuddan tallafi daga hukumar kula da manyan makarantu ta kasa.” Inji shi.
Ana sa ran kafa hukumar za ta karfafa bangaren ilimi na jihar da inganta samar da ingantaccen ilimin sakandare.
Shamsuddeen Mannir Atiku/KSHA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: da manyan makarantun hukumar kula da kula da manyan jihar Kaduna
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na jagorantar taron Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC) a ɗakin taro na Majalisar da ke Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja.
Kafin a fara taron, Shugaban Ƙasa ya rantsar da Farfesa Dakas James Dakas da Dakta Uchenna Eugene a matsayin Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki ta Ƙasa da Kwamishina.
Majalisar ta kuma dakatar da taron na minti ɗaya domin girmama marigayi Cif Audu Ogbe, wanda ya kasance memba a majalisar a lokacin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa Shehu Shagari, haka kuma a ƙarƙashin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari. Cif Ogbe ya rasu a ranar Asabar, 9 ga watan Agusta, yana da shekaru 78.
Daga Bello Wakili