HausaTv:
2025-08-08@08:51:29 GMT

Janar Salami: Muna  Cikin Shirin fuskantar Yaki A Duk Yadda Ya Zo

Published: 9th, May 2025 GMT

Kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran Janar Husaini Salami ya bayyana cewa; Dangane da Shirin Nukiliyar Iran, muna bai wa diplomasiyya fifiko, amma kuma a lokaci daya muna cikin Shirin fuskantar kowane irin yaki duk yadda ya zo.

Janar Salami wanda ya gabatar da jawabi a wurin karrama shahidan yi wa kasa hidima, a hubbaren Imam Ridha ( a.

s) ya kuma kara da cewa;  Ya kamata Amurkawa su kwana da sanin cewa, idan su ka yi mana barazana, to a shirye muke domin fuskantar kowane irin yaki, a duk yadda ya zo.

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musuluncin na Iran ya kuma zargi Amrukawa da cewa su, ba masu cika alkawali ba ne, saboda yadda su ka yi wa Iran barazana da kuma kakaba mata sabbin takunkumai.

Janar Salami ya kuma ce; Jamhuriyar musulunci ba ta da azamar kera makamin Nukiliya bisa zabinta, ta kuma cire shi daga cikin akidarta ta tsaro.

Kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya kuma ce; Muna gargadin abokan gaba akan cewa idan har su ka tafka wani kuskure, to  za a bude musu kofofin jahannama.

Janar Salami ya yi ishara da hare-haren “Wa’adussadiq 1, da na 2 da Iran ta kai wa HKI,sannan ya kara da cewa: Idan har ba za ku iya jurewa makami mai linzami guda daya daga Ansarullah jarumai daga Yemen ba, to yaya za ku yi da daruruwa da kuma dubban makamai masu linzami da za a harbo muku ?

Kwamandan na dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran ya yi jawabi akan cikar shekara da rasuwar shugaban kasa Ayatullah Ra’isi yana mai cewa; Ya kasance mutum wanda ya tattara soffofi na kamala, don haka ya cancanci yin shahada domin ita ce ta dace da shi.

Haka nan kuma ya yi jinjina ga shahidai irin su Kassim Sulaimani, Isma’ila Haniyyah, Yahya Sinwar, Sayyid Hassan Nasrallah, Safiyuddin, Zahidi, Musawi, ali-Hashim da kuma Rahmati.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin Janar Salami

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Umurci A Bada Kulawar Lafiya Kyauta Ga Tsofaffin Ma’aikata Masu Karamin Fansho

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin gaggauta aiwatar da shirin bayar da kulawar lafiya kyauta ga tsofaffin ma’aikata masu ƙaramin albashi da ke ƙarƙashin tsarin fansho na haɗin gwiwa (Contributory Pension Scheme – CPS), yana mai bayyana shirin a matsayin muhimmin bangare  da zai taimaka wa rayuwarsu.

A wata sanarwa da mai ba Shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya kuma bada umarnin a gaggauta aiwatar da karin fansho da aka dade ana jiran shi, tare da kafa mafi ƙarancin adadin fansho domin kyautatawa tsofaffin ma’aikata mafi rauni a tsarin CPS.

Wannan umarni ya biyo bayan bayani da Daraktar Janar ta Hukumar Kula da Fansho ta Ƙasa (PenCom), Ms. Omolola Oloworaran, ta gabatar wa Shugaban ƙasa.

Shugaba Tinubu ya kuma umurci Daraktar Janar ta PenCom din da ta gaggauta warware matsalar fanshon ’yan sanda da ta daɗe tana ci gaba, yana mai jaddada cewa ’yan sanda samar da tsaro a ƙasa suna da hakkin samun fansho cikin mutuntawa da kwanciyar hankali.

Daraktar Janar din ta kuma sanar da Shugaban ƙasa yadda ake ƙoƙarin kare darajar asusun fansho duba da hauhawar farashi da matsin tattalin arziki, da kuma shirin kaddamar da tsarin ba da gudummawar fansho da kudin waje domin bai wa ’yan Najeriya mazauna ƙasashen waje damar shiga tsarin fansho.

Shugaba Tinubu ya nuna cikakken goyon bayansa ga waɗannan gyare-gyare, yana mai sake jaddada aniyar gwamnatinsa na bunƙasa ci gaba mai ɗorewa da kare rayuwar talakawan Najeriya.

 

Daga Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
  • Manjo Janar Mousawi: Martanin Iran Nan Gaba Zai Kasance Mafi Muni Kan Makiya  
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Jaddada Shirinsu Na Tunkarar Duk Wata Barazana
  • Gwamnatin Kwara Ta Horar Da Manoma Sama Da 500 Tare Da Basu Tallafi
  • Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
  • Tinubu Ya Umurci A Bada Kulawar Lafiya Kyauta Ga Tsofaffin Ma’aikata Masu Karamin Fansho
  • Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
  • Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus
  • Sheikh Qassem: Tsaron Isra’ila zai ruguje cikin sa’a 1 idan ta shelanta yaki a kan Lebanon  
  • Nafisa ta cancanci kyautar Dala 100,000 da gida da OON — Pantami