Janar Salami: Muna Cikin Shirin fuskantar Yaki A Duk Yadda Ya Zo
Published: 9th, May 2025 GMT
Kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran Janar Husaini Salami ya bayyana cewa; Dangane da Shirin Nukiliyar Iran, muna bai wa diplomasiyya fifiko, amma kuma a lokaci daya muna cikin Shirin fuskantar kowane irin yaki duk yadda ya zo.
Janar Salami wanda ya gabatar da jawabi a wurin karrama shahidan yi wa kasa hidima, a hubbaren Imam Ridha ( a.
Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musuluncin na Iran ya kuma zargi Amrukawa da cewa su, ba masu cika alkawali ba ne, saboda yadda su ka yi wa Iran barazana da kuma kakaba mata sabbin takunkumai.
Janar Salami ya kuma ce; Jamhuriyar musulunci ba ta da azamar kera makamin Nukiliya bisa zabinta, ta kuma cire shi daga cikin akidarta ta tsaro.
Kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya kuma ce; Muna gargadin abokan gaba akan cewa idan har su ka tafka wani kuskure, to za a bude musu kofofin jahannama.
Janar Salami ya yi ishara da hare-haren “Wa’adussadiq 1, da na 2 da Iran ta kai wa HKI,sannan ya kara da cewa: Idan har ba za ku iya jurewa makami mai linzami guda daya daga Ansarullah jarumai daga Yemen ba, to yaya za ku yi da daruruwa da kuma dubban makamai masu linzami da za a harbo muku ?
Kwamandan na dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran ya yi jawabi akan cikar shekara da rasuwar shugaban kasa Ayatullah Ra’isi yana mai cewa; Ya kasance mutum wanda ya tattara soffofi na kamala, don haka ya cancanci yin shahada domin ita ce ta dace da shi.
Haka nan kuma ya yi jinjina ga shahidai irin su Kassim Sulaimani, Isma’ila Haniyyah, Yahya Sinwar, Sayyid Hassan Nasrallah, Safiyuddin, Zahidi, Musawi, ali-Hashim da kuma Rahmati.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin Janar Salami
এছাড়াও পড়ুন:
Sharhin bayan Labarai: Mahangar Iran Dangane Da Tattaunawa Kan Shirinta na Makamashin Nukliya Na Zaman lafiya
Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayana labarummu na yau zai yi magana dangane da ‘Mahangar Jumhuriyar Musulunci na Iran ta yadda za’a kai ga fahintar juna a tattaunawanta da kasar Amurka da suke yi wanda ni tahir amin zan karanta.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi a wata tattaunawa ta wayar tarho da tokwaransa na kungiyar tarayyar turai wato Kaja Kallas, ya bayyana mata yadda bangarorin Amurka da Iran za su kai ga cimma yarjeniya dangane da shirin makamashin nukliya na kasarsa.
Ministan ya kara da cewa tun kimani shekaru 20 da suka gabata ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran bangaren tattaunawa dangane da shirin nukliyar kasar ta zaman lafiya. Kuma batun shirin nukliyar kasar Iran tana daga cikin ayyuka masu muhimmanci wadanda ma’aikatar harkokin wajen ta aiwatar a cikin wannan lokacin.
Kasashen ya mamma karkashin jagorancin Amurka suka dorawa kasar Iran takumkuman tattalin arziki masu yawa, saboda hana JMI amfani da hakkinta na amfani da fasahar makamashin nukliya, da sunan wai iran tana shirin gina makaman Nukliya.
Don biyan wannan bukatarsu wadannan azzaluman kasashe suka sanya mafi yawan mutanen kasar Iran cikin matsaloli na rayuwa daban-daban. Amma jami’an gwamnatin JMI don tabbatarwa duniya da kuma wadannan kasashe kan cewa ba ta da wani shiri na mallakar makaman nukliya, ta bude tattaunawa da wadannan kasashe na tsawon shekaru biyu, har sai da bangarorin biyu daga ciki har da Amutka, suka cimma yarjeniya ta ganin JMI ta amfana da fasaha da kuma makamashin nukliya wanda yarjenyar NPT ta amincewa ko wace kasa a duniya ta yi amfani da shi. Wannan ya kaiga samar da yarjeniyar JCPOA a shekara 2015.
Inda JMI ta aiwatar da dukkan alkawulan da ta dauka a cikin yarjeniyar. Banda haka hukumar makamashin nukliya ta duniya IAEA ta bada rahoto har 16 kan cewa shirin makamashin nukliya na kasar Iran bai karkata daga yarjeniyar JCPOA ba,
Ana cikin wannan halin ne sai shugaban kasar Amurka mai ci ya hau kan kujerar shugabancin kasar Amurka, ya kuma fidda Amurka daga cikin yarjeniyar a shekara ta 2018, tare da dalilin cewa yarjeniyar bata yi masa ba.
Sai dai a dole JMI ta sake dawowa kan teburin tattaunawa dangane da shirin ta na makamashin nukliya. Sannan ta kara yawan takunkuman tattalin arzikin da ta dorawa JMI, don tursasa mata ta yi abinda take bukata. Banda haka ta sha alwashin sai ta maida cikinin danyen man fetur na JMI a kasuwar duniya ya zama sifir.
Amma bukatar kasar Amurka a lokacin bata ga rana ba har wata gwamnati ta maye gurbinta, sannan a dayan bangaren kasashen turai wadanda tare da su aka kulla yarjeniyar JCPOA a shekara ta 2015 suma sun saba alkawalunsu a wannan yarjeniyar suka ci gaba da dorawa JMI takunkuman tattalin arziki ba iyaka. Wadanda duk wanda ya nazarcesu zai fahinci cewa suna son faduwar gwamnatin JMI ne. Amma har yanzun basu ga hakan ya auku ba. Kuma da yardar All…ba zasu taba gani ba.
Don haka bayan ficewar Trump daga yarjeniytar JCPOA da kuma sabawa sauran kasashen Turai alkawulan da suka dauka a yarjeniyar, yarjeniyar ta zama babu wani amfani da JMI.
Amma bayan da Donal Trump ya sake komawa Fadar white House a farkon wanan shekara ta 2025 ya sake da ta wannan maganar sannan ya farfado da dukkan takunkuman tattalin arzikin da ya dorawa JMI a shugabancinsa na farko sannan yana kara wasu, daga lokaci zuwa lokaci. A wannan karon har da baraza na farwa kasar da yaki idan ta ki amincewa da sake tattauna shirin nukliyar kasar.
Ganin cewa JMI ta san cewa Amurka musamman Donal Trump ba mai cika alkawali ne ba, sai ta zabi tattaunawa ba kai tsaye ba da ita, saboda yaki zabi ne na karshe.
Don haka aka gudanar da zagaye na farko na tattaunawar a ranar 5 ga watan Afrilun da ya gabata a birnin Mascat na kasar Omman, sannan zagaye na biyu da na uku a ranar 12 da kuma 19 na watan Afrilu a biranen Roma da maskat, amma sai aka dage zaman a 4, wanda yaka mata a gudanar da ita a ranar 26 ga watan a birnin Roma.
Amma dan dan tsakanin nan sai muka fara jin maganganu daga jami’an gwamnatin kasar Amurka na cewa manufarsu ita ce hana JMI sarrafa makamashin nukliya kwatw-kwata, al-hali a zaman tattaunawa guda uku da aka gudanar Amuka bata kawo wannan batun ba. Amma an ji Trump da sakataren harkokin wajensa Rubio suna maganar hana JMI mu’amala da makamashin nukaliya kwata-kwata ne.
Sai dai wannan ketare jan layi ne, ga JMI, don ba zata taba amincewa da hakan ba, ko da za ta ga shiga yaki ne da wadannan kasashe.
Sayyid Abbas Aragchi ya fadawa Kajal Kallas jami’a mai kula da al-amuran harkokin waje na tarayyar Turai kan cewa bangarorin biyu zasu kai ga fahintar juna ne kawai idan dayan baranagren bai gabatar da wani abu wanda ya tabbatar da dayan bangaren ba zai taba amincewa ba. Ko kuma wani abu wanda ba zai taba yiyuwa ba.
Ya kammala da cewa Iran tana da tarjuba na saba alkalin Amurka, don haka idan ta kuskra da shigar da wani abu wanda ta san cewa JMI ba zata amince ba, ba inda tattaunawar zai je.