Rasha Da China Sun Sha Alwashin Fuskantar Amurka
Published: 9th, May 2025 GMT
Shugabannin kasashen Rasha da China Sun yi alkawalin fuskantar siyasar Amurka akansu,a yayin wani taro da su ka yi a birnin Moscow a daidai lokacin bikin tunawa da zagayowar cikar shekaru 80 da samun galaba akan ‘yan Nazi na kasar Jamus.
Shugaba Vladmir Putin na Rasha da takwaransa na China Xi Jing Ping sun yi tattaunawa ta fiye da sa’oi 3, sun rattaba hannu akan yarjeniyoyi a tsakaninsu da su ka kunshi kara yawan hannunu jarin da su ka zuba a cikin kasashen junansu, haka nan kuma yin aiki a tsakaninsu domin tabbatar da zaman lafiya a duniya sannan kuma da zurfafa girman alaka a tsakaninsu.
Bayanin bayan taron kasashen biyu ya kunshi nuna damuwa akan yadda Amurka take kara ayyukanta na soja da kuma kera makaman kare dangi, tare da jaddada aniyarsu ta kalubalantar siyasar Amurkan akan kasashen nasu.
Haka nan kuma Putin da Xi sun bayyana kin amincewarsu da Shirin da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da shi wanda ya shafi mayar da sararin samaniya filin yaki.
Haka nan kuma sun yi ishara da kokarin Amurka da kawayenta na tayar da rikici a Asiya da yankin tekun “Pacific”, sun kuma bayyana cewa da akwai yiyuwar barkewar yakin Nukiliya a duniya saboda yadda alaka a tsakanin kasashen da su ka mallakin wadannan makaman ta tabarbare.
A kan yakin kasar Ukiraniya kuwa, kasashen biyu sun jaddada goyon bayansu ga dukkanin kokarin da ake yi da zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya.
A karshe kasashen biyu sun ce, karfafa alakarsu da suke yi baya da nufin fada da wata kasa a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas ta bukaci kasashen duniya da MDD su mayar da Isra’ila saniyar ware
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi maraba da amincewar da kasashen Birtaniya, Australia, da Canada suka yi wa kasar Falasdinu, tana mai bayyana hakan a matsayin wani muhimmin mataki na tabbatar da hakkin al’ummar Palasdinu na kasarsu.
A cikin wata sanarwa da ta fitar jiya Lahadi, kungiyar ta yi kira ga kasashen duniya da MDD da su mayar da Isra’ila saniyar ware tare da dakatar da duk wani nau’i na hadin gwiwa da ita.
Hamas ta yaba da wannan amincewa da ita a matsayin wani muhimmin mataki na tabbatar da ikirarin da al’ummar Falastinu ke yi na neman kare filayensu da wuraren ibadarsu masu tsarki, tare da fatan samun kasa mai cin gashin kanta wacce take da Quds a mastayin babban birni.
Har ila yau kungiyar ta yi kira da a kara daukar matakan ladabtarwa kan Isra’ila tare da hukunta shugabanninta kan laifukan cin zarafin bil’adama.
Sanarwar ta soki gwamnatin Isra’ila kan yadda take ci gaba da yin watsi da dokokin kasa da kasa da kuma ka’idojin jin kai, tare da bayyana “mummunan cin zarafi” da ake yi wa Falasdinawa.
An fitar da wannan sanarwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da takun sakar diflomasiyya tsakanin kasashen dake amincewa da Falasdinu a matsayin kasa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran : Dakatar da kisan kiyashi a Gaza, ‘’zakaran gwajin dafi ‘’ne ga MDD” September 22, 2025 Italiya: An yi gagarimar zanga-zangar tir da kisan kiyashi da ake yi a Gaza September 22, 2025 Iran ta la’anci harin da aka kai kan wani masallaci a Sudan September 22, 2025 Ana Ci Gaba Da Kidayar Kuri’aun Zaben Shugaban Kasa A Guinea September 22, 2025 Kwamandan Sojan Iran: Ba Za Mu Taba Wasa Da Manufofinmu Na Kasa Ba September 22, 2025 Korea Ta Arewa Ta Sanar Da Kera Wani Sabon Makami Na Sirri September 22, 2025 Jirgin Ruwan “Umar Mukhtar” Na Agaji Ya Kama Hanyar Zuwa Gaza Daga Kasar Libya September 22, 2025 Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jinjinawa Tawagar Kokawar Greco-Roma Ta Iran Murnar Lashe Gasar Cin Kofin Duniya September 22, 2025 Pezeshkian: Kasashen Da Ba Su Cika Alkawura Da Suka Dauka Ba Suke Zargin Iran Kan Rashin Mutanta Yarjejeniyar Nukiliya September 22, 2025 Dakarun IRGC: Iran Za Ta Tarwatsa Makiya Tare Da Mayar Da Martani Kan Duk Wani Zalunci September 22, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci