HausaTv:
2025-05-09@13:11:18 GMT

Rasha Da China Sun Sha Alwashin Fuskantar Amurka

Published: 9th, May 2025 GMT

Shugabannin kasashen Rasha da China Sun yi alkawalin fuskantar siyasar Amurka akansu,a yayin wani taro da su ka yi a birnin Moscow a daidai lokacin bikin tunawa da zagayowar cikar shekaru 80 da samun galaba akan ‘yan Nazi na kasar Jamus.

Shugaba Vladmir Putin na Rasha da takwaransa na China Xi Jing Ping sun yi tattaunawa ta fiye da sa’oi 3, sun rattaba hannu akan yarjeniyoyi a tsakaninsu da su ka kunshi kara yawan hannunu jarin da su ka zuba a cikin kasashen junansu, haka nan kuma yin aiki a tsakaninsu domin tabbatar da zaman lafiya a duniya sannan kuma da zurfafa girman alaka a tsakaninsu.

Bayanin bayan taron kasashen biyu ya kunshi nuna damuwa akan yadda Amurka take kara ayyukanta na soja da kuma kera makaman kare dangi, tare da jaddada aniyarsu ta kalubalantar siyasar Amurkan akan kasashen nasu.

Haka nan kuma Putin da Xi sun bayyana kin amincewarsu da Shirin da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da shi wanda ya shafi mayar da sararin samaniya filin yaki.

Haka nan kuma sun yi ishara da kokarin Amurka da kawayenta na tayar da rikici a Asiya da yankin tekun “Pacific”,  sun kuma bayyana cewa da akwai yiyuwar barkewar yakin Nukiliya a duniya saboda yadda alaka a tsakanin kasashen da su ka mallakin wadannan makaman ta tabarbare.

A kan yakin kasar Ukiraniya kuwa, kasashen biyu sun jaddada goyon bayansu ga dukkanin kokarin da ake yi da zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya.

A karshe kasashen biyu sun ce, karfafa alakarsu da suke yi baya da nufin fada da wata kasa a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Janar Salami: Muna  Cikin Shirin fuskantar Yaki A Duk Yadda Ya Zo

Kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran Janar Husaini Salami ya bayyana cewa; Dangane da Shirin Nukiliyar Iran, muna bai wa diplomasiyya fifiko, amma kuma a lokaci daya muna cikin Shirin fuskantar kowane irin yaki duk yadda ya zo.

Janar Salami wanda ya gabatar da jawabi a wurin karrama shahidan yi wa kasa hidima, a hubbaren Imam Ridha ( a.s) ya kuma kara da cewa;  Ya kamata Amurkawa su kwana da sanin cewa, idan su ka yi mana barazana, to a shirye muke domin fuskantar kowane irin yaki, a duk yadda ya zo.

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musuluncin na Iran ya kuma zargi Amrukawa da cewa su, ba masu cika alkawali ba ne, saboda yadda su ka yi wa Iran barazana da kuma kakaba mata sabbin takunkumai.

Janar Salami ya kuma ce; Jamhuriyar musulunci ba ta da azamar kera makamin Nukiliya bisa zabinta, ta kuma cire shi daga cikin akidarta ta tsaro.

Kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya kuma ce; Muna gargadin abokan gaba akan cewa idan har su ka tafka wani kuskure, to  za a bude musu kofofin jahannama.

Janar Salami ya yi ishara da hare-haren “Wa’adussadiq 1, da na 2 da Iran ta kai wa HKI,sannan ya kara da cewa: Idan har ba za ku iya jurewa makami mai linzami guda daya daga Ansarullah jarumai daga Yemen ba, to yaya za ku yi da daruruwa da kuma dubban makamai masu linzami da za a harbo muku ?

Kwamandan na dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran ya yi jawabi akan cikar shekara da rasuwar shugaban kasa Ayatullah Ra’isi yana mai cewa; Ya kasance mutum wanda ya tattara soffofi na kamala, don haka ya cancanci yin shahada domin ita ce ta dace da shi.

Haka nan kuma ya yi jinjina ga shahidai irin su Kassim Sulaimani, Isma’ila Haniyyah, Yahya Sinwar, Sayyid Hassan Nasrallah, Safiyuddin, Zahidi, Musawi, ali-Hashim da kuma Rahmati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Janar Salami: Muna  Cikin Shirin fuskantar Yaki A Duk Yadda Ya Zo
  • Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
  • Aragchi: Muna Bukatar Rage Zaman Daradar Da Kuma Tabbatar Da Zaman Lafiya A Tsakanin Pakisatan Da Indiya
  • An Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasara A Yakin Duniya Na Biyu
  • Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki
  • Amurka ta matsa wa ƙasashe da ke fuskantar haraji su amince da Starlink
  • Yemen Ta Jaddada Cewa: Idan Amurka Ta Kai Mata Hari, Tabbas Yarjejeniyar Kawo Karshen Bude Wuta Tsakaninsu Zata Ruguje  
  • Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Tattaunawar Cinikayya Da Za A Yi Tsakanin Babban Jami’inta Da Na Amurka