Rasha Da China Sun Sha Alwashin Fuskantar Amurka
Published: 9th, May 2025 GMT
Shugabannin kasashen Rasha da China Sun yi alkawalin fuskantar siyasar Amurka akansu,a yayin wani taro da su ka yi a birnin Moscow a daidai lokacin bikin tunawa da zagayowar cikar shekaru 80 da samun galaba akan ‘yan Nazi na kasar Jamus.
Shugaba Vladmir Putin na Rasha da takwaransa na China Xi Jing Ping sun yi tattaunawa ta fiye da sa’oi 3, sun rattaba hannu akan yarjeniyoyi a tsakaninsu da su ka kunshi kara yawan hannunu jarin da su ka zuba a cikin kasashen junansu, haka nan kuma yin aiki a tsakaninsu domin tabbatar da zaman lafiya a duniya sannan kuma da zurfafa girman alaka a tsakaninsu.
Bayanin bayan taron kasashen biyu ya kunshi nuna damuwa akan yadda Amurka take kara ayyukanta na soja da kuma kera makaman kare dangi, tare da jaddada aniyarsu ta kalubalantar siyasar Amurkan akan kasashen nasu.
Haka nan kuma Putin da Xi sun bayyana kin amincewarsu da Shirin da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da shi wanda ya shafi mayar da sararin samaniya filin yaki.
Haka nan kuma sun yi ishara da kokarin Amurka da kawayenta na tayar da rikici a Asiya da yankin tekun “Pacific”, sun kuma bayyana cewa da akwai yiyuwar barkewar yakin Nukiliya a duniya saboda yadda alaka a tsakanin kasashen da su ka mallakin wadannan makaman ta tabarbare.
A kan yakin kasar Ukiraniya kuwa, kasashen biyu sun jaddada goyon bayansu ga dukkanin kokarin da ake yi da zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya.
A karshe kasashen biyu sun ce, karfafa alakarsu da suke yi baya da nufin fada da wata kasa a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Harin Amurka ya bayyana karara kan Venezuela
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa: Barazanar da ake yi wa Venezuela ba ta dace da al’ummar duniya ba, yana mai jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kasance kuma za ta ci gaba da kasancewa cikin hadin kai da gwamnati da al’ummar Caracas.
Da yake jawabi a bikin rantsar da ofishin wakilin Ma’aikatar Harkokin Waje a Lardin Hamadan, Araqchi ya bayyana cewa: Wannan ofishin zai taimaka wajen karfafa alakar tattalin arziki, kimiyya, da al’adu ta lardin, da kuma sauƙaƙe hulɗar jakadanci da gudanarwa ga ‘yan ƙasar.
Ya lura cewa: Baba’i Ragheb, wani jami’in ma’aikatar da ya ƙware, zai jagoranci sabon ofishin, kuma ya gode wa gwamnan Hamadan saboda haɗin gwiwarsa wajen samar da wurin zama na wucin gadi a cikin ginin gwamnatin. Ya ƙara da cewa a halin yanzu ana shirya wani gini daban, wanda nan ba da jimawa ba za a mayar da ofishin can.
Da yake amsa tambaya game da kalaman da jami’an Amurka suka yi kwanan nan game da Venezuela, Araqchi ya ce tsarin girman kai da kuma halayen Amurka sun bayyana a ko’ina cikin duniya. Ya bayyana cewa Amurka tana hulɗa ne kawai da ƙasashen da ke biyan muradunta kuma tana ƙiyayya da kowace ƙasa da ke ƙoƙarin samun ‘yancin kai, “kamar yadda ya kasance a Jamhuriyar Musulunci tsawon shekaru da dama.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu November 6, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza November 6, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku A Kudancin Lebanon November 6, 2025 Sayyid Muqtada al-Sadr Ya Fadakar Da Magoya Bayansa Kwanaki Kafin Zabe A Iraki November 6, 2025 Araghchi : Yakin kwanaki 12 ya bamu babban darasi November 6, 2025 Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya November 6, 2025 Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Gwamnonin IAEA November 6, 2025 Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho November 6, 2025 Najeriya Ta Sake Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar November 6, 2025 Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya November 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci