HausaTv:
2025-06-24@04:03:05 GMT

Rasha Da China Sun Sha Alwashin Fuskantar Amurka

Published: 9th, May 2025 GMT

Shugabannin kasashen Rasha da China Sun yi alkawalin fuskantar siyasar Amurka akansu,a yayin wani taro da su ka yi a birnin Moscow a daidai lokacin bikin tunawa da zagayowar cikar shekaru 80 da samun galaba akan ‘yan Nazi na kasar Jamus.

Shugaba Vladmir Putin na Rasha da takwaransa na China Xi Jing Ping sun yi tattaunawa ta fiye da sa’oi 3, sun rattaba hannu akan yarjeniyoyi a tsakaninsu da su ka kunshi kara yawan hannunu jarin da su ka zuba a cikin kasashen junansu, haka nan kuma yin aiki a tsakaninsu domin tabbatar da zaman lafiya a duniya sannan kuma da zurfafa girman alaka a tsakaninsu.

Bayanin bayan taron kasashen biyu ya kunshi nuna damuwa akan yadda Amurka take kara ayyukanta na soja da kuma kera makaman kare dangi, tare da jaddada aniyarsu ta kalubalantar siyasar Amurkan akan kasashen nasu.

Haka nan kuma Putin da Xi sun bayyana kin amincewarsu da Shirin da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da shi wanda ya shafi mayar da sararin samaniya filin yaki.

Haka nan kuma sun yi ishara da kokarin Amurka da kawayenta na tayar da rikici a Asiya da yankin tekun “Pacific”,  sun kuma bayyana cewa da akwai yiyuwar barkewar yakin Nukiliya a duniya saboda yadda alaka a tsakanin kasashen da su ka mallakin wadannan makaman ta tabarbare.

A kan yakin kasar Ukiraniya kuwa, kasashen biyu sun jaddada goyon bayansu ga dukkanin kokarin da ake yi da zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya.

A karshe kasashen biyu sun ce, karfafa alakarsu da suke yi baya da nufin fada da wata kasa a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Yi
  • Babu dalilin kai wa Iran farmaki — Putin
  • Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha
  • Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz
  • Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna
  • Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa
  • Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa