Leadership News Hausa:
2025-06-23@05:54:51 GMT

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Published: 8th, May 2025 GMT

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Tsohon ministan kudin kasar Amurka John Connally ya ce, dala kudi ne na Amurka, amma matsala ce ga sauran kasashen duniya. Yanzu haka tsarin kudin na haifar da karin radadi ga kasashe daban daban, sakamakon matakan kasar Amurka na kashin kai, lamarin da ya sanya dimbin kasashe neman kauracewa tsarin dalar Amurka.

Misali, a rubu’in farkon bana, darajar cinikin da kasar Sin ta yi tare da kasashen Malaysia da Cambodia da kudin RMB, ta karu da kaso 27%, da 24%, bisa makamancin lokacin bara. Kana a nata bangare, kasar Najeriya za ta kulla yarjejeniyar musayar kudin Naira zuwa kudin Sin RMB kai tsaye, tare da kasar Sin, bisa wani labarin da jaridar Vanguard ta kasar Najeriya ta gabatar.

Kudi wani nau’in kayan aiki ne. Idan ana iya amfani da shi cikin sauki, kuma za a iya dogaro a kan sa ba tare da samun hasara ba, to, za a so a yi amfani da shi. Amma idan wani kudi ya kan haifar da matsaloli, to, tabbas za a guji yin amfani da shi. Wannan batu yana cikin tsarin gudanar tattalin arziki, ba wani abu ne da za a iya sauya shi ta karfin siyasa ba. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya ce Sin ta yi matukar Allah wadai da hare-haren da Amurka ta kai kasar Iran, tare da jefa bama-bamai kan cibiyoyin sarrafa nukiliyar kasar, dake karkashin kulawar hukumar lura da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ko IAEA a takaice.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana hakan ne a Lahadin nan, lokacin da yake tsokaci kan sanarwar da shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar, cewa Amurka ta kaddamar da hare-hare kan cibiyoyi uku na nukiliyar kasar Iran. Jami’in ya ce matakin Amurka ya yi matukar keta makasudi, da ka’idojin MDD da dokokin kasa da kasa, ya kuma ruruta yanayin rashin tabbas da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya.

Daga nan sai jami’in ya ce Sin na kira ga sassa masu ruwa da tsaki a tashin hankalin dake wakana, musamman ma Isra’ila, da su gaggauta cimma matsayar dakatar da bude wuta, tare da tabbatar da tsaron rayukan fararen hula, da fara tattaunawa da shawarwari. Ya ce Sin a shirye take, ta yi aiki da sauran kasashe wajen aiwatar da matakan tabbatar da adalci, da aiki tukuru wajen dawo da yanayin zaman lafiya da daidaito a Gabas ta Tsakiya. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi
  • Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna
  • Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa
  • An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
  • Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya
  • Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani