Leadership News Hausa:
2025-11-08@18:51:28 GMT

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Published: 9th, May 2025 GMT

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

A yau, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Rasha Vladimir Putin sun gana tare da manema labarai bayan tattaunawa a fadar Kremlin dake birnin Moscow. Inda Xi ya jaddada cewa, a yayin da yanayin kasa da kasa ke fuskantar sauye-sauye da hargitsi, kamata ya yi kasashen Sin da Rasha su yi riko da ruhin kyakkyawar makwaftaka kuma na dindindin, da hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni, da hadin gwiwar samun moriyar juna da nasara tare, da habaka girma, fadi da juriyar dangantakar Sin da Rasha daga dukkan fannoni, da sanya karin kwanciyar hankali ga zaman lafiya da tsaro a duniya, da samar da kuzari ga ci gaban duniya da wadata.

(Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata

Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Hajiya Asma’u Muhammadu Inuwa Yahaya, ta jagoranci wani yunƙuri na ganin an tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata daga watanni uku zuwa shida.

Ta jagoranci manyan jami’an lafiya zuwa majalisar dokokin jihar domin neman goyon bayan doka kan wannan shiri.

Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar Najeriya Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu — Tinubu

A yayin taron wayar da kai a majalisar, Hajiya Asma’u ta bayyana cewa shayar da jarirai nono har watanni shida yana da matuƙar amfani wajen rage mace-macen jarirai, inganta garkuwar jikinsu, da bunƙasa ƙwaƙwalwarsu.

Uwargidan ta roƙi majalisar, ƙarƙashin jagorancin Kakakin Majalisar, Abubakar Mohammed Luggerewo, da su samar da doka da za ta tabbatar da wannan shiri.

Kakakin Majalisar, ya yaba da ƙoƙarin Uwargidan Gwamnan, inda ya ce wannan ziyarar “ta tarihi ce” kuma ya tabbatar da goyon bayan majalisar wajen ganin an aiwatar da ƙudirin.

Haka kuma, wakiliyar Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF), Miss Omowumi Gbamis, ta ce wannan doka zai taimaka wa mata su ci gaba da aiki lafiya tare da inganta lafiyar jarirai.

Kodinetan CS-SUNN a Gombe, Misis Comfort Mukollo, ta bayyana cewa suna aiki tare da UNICEF da ma’aikatun gwamnati don tallafa wa shirye-shiryen kula da abincin uwa da jariri tare da wayar da kan jama’a kan muhimmancin shayar da nono.

Daga cikin manyan jami’an da suka nuna goyon baya akwai Kwamishiniyar Harkokin Mata, Asma’u Mohammed Iganus, da Shugaban Kwamitin Lafiya na Majalisar, Siddi Buba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata
  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya