Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a yau Alhamis cewa, a yayin da ake fuskantar sauye-sauyen da ba a taba ganin irinsu ba a duniya, kasashen Sin da Rasha sun ci gaba da zurfafa amincewa da juna ta fuskar siyasa, da hadin kai bisa manyan tsare-tsare, da kiyaye daidaito da hadin gwiwa a harkokin kasa da kasa, da sanya kwanciyar hankali da kyakkyawan kuzari a duniyar mai fuskantar sauyi da tashe-tashen hankula.

Xi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin yayin ziyarar da ya kai kasar ta Rasha. Yana mai cewa, dangantakar dake tsakanin Sin da Rasha ta samu ci gaba mai dorewa, cikin koshin lafiya kuma a babban mataki, sakamakon kokarin hadin gwiwa daga bangarorin biyu. Ya kuma yaba da kyakkyawar makwaftaka da kawance na dogon lokaci, da hadin gwiwar moriyar juna a matsayin wani muhimmin yanayi na dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Xi ya kara da cewa, kasar Sin ta kasance babbar mai bayar da gudummawa da daidaita ci gaban tattalin arzikin duniya tsawon shekaru, kana kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasar Rasha wajen kiyaye tsarin cinikayyar duniya bisa ra’ayin bangarori daban daban, da kiyaye tsarin masana’antu da samar da kayayyaki cikin kwanciyar hankali ba tare da cikas ba. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya

Wata ɗaliba ’yar shekara 15 daga Jihar Yobe, Rukayya Muhammad Fema, ta zama Gwarzuwar Shekarar 2025 a Gasar Muhawara ta Duniya ta Teen Eagle.

Rukayya ta yi zarra ne a wannan babbar gasa da ta gudana a birnin Landan na ƙasar Birtaniya, inda zaƙaƙuran ɗalibai daga ƙasashe 69 a faɗin duniya suka fafata a tsakaninsu.

Jami’in Sadarwar Zamani na Gwamnatin Jihar Yobe, Yusuf Ali, ya bayyana cewa Rukayya ta samu kafa wannan tarihi ne a dalilin zurfin tunani da kuma kaifin basirarta da kuma fahimtar al’amuran duniya, duk kuwa da ƙarancin shekarunta.

Ɗalibar daga Kwalejin Nigerian Tulip International (NTIC), Rukayya, ta ɗauki hankalin alƙalan gasar da sauran jama’a saboda ƙarfin hujjojinta da ta gabatar da kuma iya bayani mai ganawarsa cikin natsuwa, lamarin da ya ba ta damar doke duk abokan karawarta.

Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami NAJERIYA A YAU: Yadda Ayyuka Suka Ragu A Jihohi Bayan Kudin Shiga Ya Karu

Ita ce mutum ya biyu daga Jihar Yobe kuma daga makaranta tare da Nafisa Abdullah Aminu wadda ta zama gwarzuwa a ɓangaren Harshen Turanci a yayin gasar, inda suka wakilci Najeriya, ƙasa mai yawan al’umma sama da miliyan 200.

Nasararta nuna irin basirar da Allah Ya yi wa matasan Najeriya inda suke yin zarra a sassan duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
  • Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
  • An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu
  • Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
  • Yadda sabbin takunkuman Trump za su shafi tattalin arziƙin duniya
  • Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
  • Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi  Na Tabbatar Da Karfi Da Ci gaba
  • Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya
  • ’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya