Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta
Published: 8th, May 2025 GMT
Tawagar jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta haɗa da sakataren gwamnatin jihar, da masu ba da shawara na musamman guda biyu, da babban sakataren ZITDA, tare da Siobhan Wilson, shugaban Oracle na Ingila da kuma babban mataimakin shugaban EMEA.
Sanarwar ta ƙara da cewa: “Gwamnatin jihar Zamfara ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya mai muhimmanci tare da Oracle don bunƙasa fasahar dijital a faɗin jihar, wanda aka samu ta hanyar Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), haɗin gwiwar za ta yi amfani da ƙwarewa da ayyukan koyo na makarantar Oracle da jami’ar Oracle a ƙoƙarinsu na kawo sauyi.
“Haɗin gwiwar yana nuna sadaukar da kai ga ilimi da saka hannun jari a makomar matasan Zamfara, ma’aikata, da tattalin arzikin dijital.
“Makarantar Oracle, shirin ilimi na taimakon jama’a na duniya yana koyar da ilimin fasaha, gami da manhaja da samun damar sanin ilimin fasahar software na kwamfuta ga malamai da ɗalibai a duk duniya.
“Tare da tallafin Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), za a samar da waɗannan albarkatun ga ingantattun manyan makarantu a faɗin Zamfara.”
“ZITDA za ta taimaka wajen jagorantar ayyukan makarantar Oracle Academy a cikin babbar manhajar karatu ta Zamfara, tana ba wa malamai kayan aiki da albarkatun da suke buƙata don koyar da ɗalibai dabarun fasaha da kuma samun takardun ƙwarewa na Oracle.
“Bugu da ƙari, Shirin Jami’ar Oracle (SDI), shiri ne na duniya wanda ke koyar da abubuwa na musamman a duniya ba tare da kashe ko kobo ba ga ɗaliban da suka cancanta, kuma zai ƙara faɗaɗa damarmaki ga ɗalibai a Zamfara.
“Ta hanyar haɗin gwiwar Learning Portal tare da ZITDA, Jami’ar Oracle na shirin ba da damar samun hanyoyin ilmantarwa kyauta da takardun shaida ga mahalartan da suka cancanta a faɗin Zamfara. Wannan ya haɗa da tafiye-tafiye na ilmantarwa wanda ke ba da horo na ƙwarewa na sama da sa’o’i 200 a fannonin da ake buƙata kamar Cloud, Ƙirƙirarriyar Basira ta AI, Data Science da APEX.”
A jawabinsa a wajen rattaba hannu kan muhimmiyar yarjejeniyar, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa haɗin gwiwa da Oracle na daga cikin ƙudirin gwamnatinsa na mayar da jihar Zamfara wata cibiya ta ƙirƙire-ƙirƙire, ilimi, da fasahar zamani.
Ya ce, “A madadin gwamnati da na al’ummar jihar Zamfara, ina miƙa godiya ta ga Oracle bisa yadda ta yi imani da manufofinmu da kuma haɗin kai da mu kan wannan tafiya ta kawo sauyi.”
“Abin da muke yi a yau ya wuce fasaha, samar wa al’umma madogara ne, samar da hanyoyi, da kuma buɗe damarmakin da ke gaba. Ta hanyar saka hannun jari a ilimin dijital, muna ba neman ƙore talauci, rashin aikin yi, da kuma hana yanke ƙauna.”
“Ina godiya ga Oracle don tsayawa tare da mu – yarda da ƙarfin haɗin gwiwa da sanin manufar mu. A yau, ba kawai muna sanya hannu kan takarda ba ne; amma muna yin alƙawari: “Alƙawarin cewa kowane yaro a Zamfara zai samu dama mai kyau don ƙaddanar da burin sa na rayuwa, koyo, da kuma samun nasara. Alƙawarin cewa fasaha za ta zama gadar mu ta zuwa ta samun tattalin arziki mai ƙarfi. Kuma alƙawarin cewa Zamfara ba za ta shiga cikin juyin juya halin dijital kawai ba – a’a mu za mu jagoranci shi.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniya
Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, ya shirya da wani gagarumin biki domin karrama Nafisa Abdullah ’yar shekara 17 da Rukayya Muhammad Fema ’yar shekara 15, wadandan ’yan asalin jihar ne, bayan sun lashe gasar duniya da aka gudanar da kasar Birtaniya.
Nafisa ta lashe Gashar Iya Turanci ta Duniya a yayin da Rukayya ta lashe Gasar Muhawar ta duniya, inda suka doke kasashe 69 a Gasar TeenEagle na shekarar 2025 da aka gudanar a birnin Landan.
Bayan doke dalibai sama da 20,000 da suka fafata a gasar inda suka wakilci Najeriya daga Kwalejin Nigerian Tulip (NTIC) da ke Jihar Yobe.
Nafisa da Rukayya dukkansu sun ci gajiyar shirin tallafin karatu na Gwamna Mai Mala Buni wanda ya kunshi cikakken dawainiyar karatun dalibai 890 a NTIC.
Gwamna Buni ya bayyana wannan nasara da ’yan matan suka samu a matsayin babban abin alfahari ga jiha da kuma Najeriya baki daya.
“Wadannan manyan ayyuka ne da ke sa mu yi alfahari da kuma tabbatar da saka hannun jarin gwamnati a fannin ilimi,” in ji Gwamna Buni.
Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da bayar da tallafin karatu ga kowane yaro a jihar domin samun damar zuwa makaranta, ya kuma yi qira ga iyaye da su ba su haxin kai.
A halin yanzu, akwai kimanin daliban jihar Yobe 40,000 da ke samun tallafin karatu na gwamnati da ke karatun kwasa-kwasai daban-daban a jami’o’i da sauran manyan makarantu a Najeriya da kasashen ketare.
Idan dai ba a manta ba a ’yan watannin da suka gabata jihar ta yi bikin yaye dalibai 167 da suka ci gajiyar shirin tallafin karatu da jihar ta samu wadanda suka kammala karatunsu a fannin likitanci da kwamfuta da kimiyyar injiniyanci daga jami’o’in kasar Indiya.