Tawagar jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta haɗa da sakataren gwamnatin jihar, da masu ba da shawara na musamman guda biyu, da babban sakataren ZITDA, tare da Siobhan Wilson, shugaban Oracle na Ingila da kuma babban mataimakin shugaban EMEA.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa: “Gwamnatin jihar Zamfara ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya mai muhimmanci tare da Oracle don bunƙasa fasahar dijital a faɗin jihar, wanda aka samu ta hanyar Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), haɗin gwiwar za ta yi amfani da ƙwarewa da ayyukan koyo na makarantar Oracle da jami’ar Oracle a ƙoƙarinsu na kawo sauyi.

“Haɗin gwiwar yana nuna sadaukar da kai ga ilimi da saka hannun jari a makomar matasan Zamfara, ma’aikata, da tattalin arzikin dijital.

 

“Makarantar Oracle, shirin ilimi na taimakon jama’a na duniya yana koyar da ilimin fasaha, gami da manhaja da samun damar sanin ilimin fasahar software na kwamfuta ga malamai da ɗalibai a duk duniya.

 

“Tare da tallafin Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), za a samar da waɗannan albarkatun ga ingantattun manyan makarantu a faɗin Zamfara.”

 

“ZITDA za ta taimaka wajen jagorantar ayyukan makarantar Oracle Academy a cikin babbar manhajar karatu ta Zamfara, tana ba wa malamai kayan aiki da albarkatun da suke buƙata don koyar da ɗalibai dabarun fasaha da kuma samun takardun ƙwarewa na Oracle.

 

“Bugu da ƙari, Shirin Jami’ar Oracle (SDI), shiri ne na duniya wanda ke koyar da abubuwa na musamman a duniya ba tare da kashe ko kobo ba ga ɗaliban da suka cancanta, kuma zai ƙara faɗaɗa damarmaki ga ɗalibai a Zamfara.

 

“Ta hanyar haɗin gwiwar Learning Portal tare da ZITDA, Jami’ar Oracle na shirin ba da damar samun hanyoyin ilmantarwa kyauta da takardun shaida ga mahalartan da suka cancanta a faɗin Zamfara. Wannan ya haɗa da tafiye-tafiye na ilmantarwa wanda ke ba da horo na ƙwarewa na sama da sa’o’i 200 a fannonin da ake buƙata kamar Cloud, Ƙirƙirarriyar Basira ta AI, Data Science da APEX.”

A jawabinsa a wajen rattaba hannu kan muhimmiyar yarjejeniyar, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa haɗin gwiwa da Oracle na daga cikin ƙudirin gwamnatinsa na mayar da jihar Zamfara wata cibiya ta ƙirƙire-ƙirƙire, ilimi, da fasahar zamani.

 

Ya ce, “A madadin gwamnati da na al’ummar jihar Zamfara, ina miƙa godiya ta ga Oracle bisa yadda ta yi imani da manufofinmu da kuma haɗin kai da mu kan wannan tafiya ta kawo sauyi.”

 

“Abin da muke yi a yau ya wuce fasaha, samar wa al’umma madogara ne, samar da hanyoyi, da kuma buɗe damarmakin da ke gaba. Ta hanyar saka hannun jari a ilimin dijital, muna ba neman ƙore talauci, rashin aikin yi, da kuma hana yanke ƙauna.”

 

“Ina godiya ga Oracle don tsayawa tare da mu – yarda da ƙarfin haɗin gwiwa da sanin manufar mu. A yau, ba kawai muna sanya hannu kan takarda ba ne; amma muna yin alƙawari: “Alƙawarin cewa kowane yaro a Zamfara zai samu dama mai kyau don ƙaddanar da burin sa na rayuwa, koyo, da kuma samun nasara. Alƙawarin cewa fasaha za ta zama gadar mu ta zuwa ta samun tattalin arziki mai ƙarfi. Kuma alƙawarin cewa Zamfara ba za ta shiga cikin juyin juya halin dijital kawai ba – a’a mu za mu jagoranci shi.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

Haka zalika, Gwamnatin Jihar Kebbi ba ta bayar da tallafi ga mahajjantanta 3,800 daga jihar ba. Amma a kasar Saudiyya, Gwamnan Nasir Idris ya amince da bayar da Riyal 200 ga kowane alhaji daga jihar.

Gwamnatin Jihar Lagos ba ta tallafi ga mahajjatanta a wannan shekara ba, yayin da kowane daga cikin masu aikin hajji 1,315 daga jihar ya biya kimanin naira miliyan 9.

Amma kuma, Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya ba kowane daga cikin mahajjatan kyauta Riyal 180, wanda ya kai naira 98,454,050 gaba dayansu.

Gwamnatin Jihar Jigawa, wacce ma ba ta bayar da tallafi ga mahajjatanta ba a wannan shekarar, amma ta ba su kyautar Riyal 100 (kimanin naira 43,000) ga kowanne daga cikin mahajjatanta 930.

Dukkanin alhazai Jihar Sakkwato 3,200 sun karbi Riyal 1,000 (wanda ya kai kimanin naira 450,000) a matsayin kyautar sallah daga Gwamna Ahmed Aliyu.

Gwamnan ya sanar da hakan a ranar Asabar yayin ziyararsa ga tawagar alhazan jihar a Mina da ke kasar Saudiyya, inda ya taya su murnar kammala aikin hajj cikin nasara.

Mataimakin gwamnan Jihar Borno, Umar Usman Kadafur, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta biya kudin hadiyya ga kowane alhazi daga jihar. Adadin alhazan sun kai 2,174, da suka yi aikin hajji a wannan shekara daga jihar.

Wani masani kan harkokin al’umma, Farfesa Yahaya Tanko, a cikin wata hirar, ya bayyana cewa kashe kudin da gwamnonin suka yi kan aikin hajji ba matsala ba ce, amma sun manta da asalin abin da al’ummarsu suka fi bukata.

Ya ce ya kamata gwamnonin su fi mai da hankali kan magance matsalar tsaro da inganta jin dadin ‘yan kasa.

Da yake jawabi kan lamarin, babban limanin Al-Habibiyah Islamic Society (AIS), Sheikh Fuad Adeyemi, ya ce ba laifi ba ne ga gwamnatin tarayya da na jihohi su tallafa wa masu alhazai, amma ya kamata a yi amfani da kudaden wajen abubuwan da mutane suka fi bukata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna
  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka
  • Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
  • Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
  • Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya