Kasar Yemen ta jaddada cewa: Ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kai munanan hare-hare kan Amurka idan ta dawo da kai hari a kan kasarta

Sojojin Yemen sun sanar da aiwatar da hare-haren soji guda uku kan tashar jiragen sama na Ramon, wani muhimmin wuri ne na makiya yahudawan sahayoniyya, da a wurin akwai jirgin ruwan Amurka Truman mai dauke da dauke da jiragen saman yakin Amurka da kuma wasu kayayyakin yakinta.

Majiyar sojojin Yemen ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa, sojojin samanta sun gudanar da ayyukan soji guda biyu, na farko a kan filin jirgin saman “Ramon” na haramtacciyar kasar Isra’ila da ke yankin Umm al-Rashrash a kudancin kasar Falasdinu da aka mamaye da jiragen sama masu saukar ungulu guda biyu, yayin da hari na biyun an kai harin ne kan wani muhimmin yanki a Jaffa da aka mamaye da wani jirgin sama maras matuki ciki, nau’in “Jaffa”, don tallafawa al’ummar Falastinu da ake zalunta.

A cikin wata sanarwa da kakakinta Birgediya Janar Yahya Sari’e ya fitar ya tabbatar da cewa: “A cikin yanayin tunkarar hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen da kuma mayar da martani kan laifukan da suke yi kan al’ummar kasar, sojojin ruwa da na sama sun gudanar da wani farmaki na musamman na soji kan jirgin Amurka Truman da kuma wani adadi mai yawa na jiragen yakinta a tekun Bahar Maliya da wani makami mai linzami.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mata 400 sun amfana da kayan haihuwa a Gombe

Ƙaramar Hukumar Gombe, ta raba wa mata masu juna guda 400 kayan haihuwa kyauta, domin kare lafiyarsu da rage mace-mace a yankin.

An gudanar da rabon ne a Cibiyar Haihuwa ta Gombe a ranar Alhamis, inda shugaban Ƙaramar Hukumar, Barista Sani Ahmad Haruna, ya jagoranci rabon.

Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 4, 16 sun jikkata a Yobe Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro

Shugaban ya ce shirin ya yi daidai da umarnin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, na bunƙasa kiwon lafiya a matakin farko, musamman ga mata masu juna biyu daga lokacin ɗaukar ciki har zuwa haihuwa.

Ya kuma bayyana cewa an fara gwajin jini kyauta ga mata masu juna biyu a dukkanin cibiyoyin haihuwa, domin gano matsalolin lafiya tun da wuri.

Wasu daga cikin matan da suka amfana sun gode wa gwamnati, inda suka bayyana cewa shirin zai rage musu kashe kuɗi tare da tabbatar da lafiyarsu da ta jariransu.

Wata mata mai suna Sa’adatu Garba, ta bayyana jin daɗinta game rabon kayan.

“Wannan kaya da aka ba mu tabbas za su taimaka, musamman duba da halin matsi da ake ciki,” in ji ta.

Ita kuwa Rabi Mustapha cewa ta yi: “Wannan babban tagomashi ne, muna godiya Allah Ya saka da alheri. Wannan shiri zai sauƙaƙa mana wajen rage kashe kuɗaɗe.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  •  Kasar Afirka Ta Kudu Ta Jaddada Yin Kiran A Bai Wa Falasdinawa Kasarsu
  • Hindi: Amurka Da Kasashen Yamma Ba Sa Son A Dakatar Da Bude Wuta A Gaza.
  • Kasar Sin Za Ta Shirya Taron Mata Na Duniya A Beijing Yayin Cika Shekaru 30 Da Taron Mata Na 1995
  • Jirgin Ruwan “Umar Mukhtar” Na Agaji Ya Kama Hanyar Zuwa Gaza Daga Kasar Libya
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen: ‘Yan Koren Amurka Da Isra’ila Suke Neman Wargaza Hadin Kan Larabawa Da Na Musulmi                         
  • Mahara sun kashe ’yan sanda a shingen bincike a Kogi
  • Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI
  • Mata 400 sun amfana da kayan haihuwa a Gombe
  • Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram