Falasdinawa Sun Yi Shahada A Hare-Haren Da Sojojin Isra’il Suka Kai Gidan Cin Abinci Da Kasuwa A Gaza
Published: 8th, May 2025 GMT
Falasdinawa da dama ne suka yi shahada tare da jikkata sakamakon hare-haren bama-bamai da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gidan abinci da wata shahararriyar kasuwa a Gaza
Akalla Falasdinawa 20 ne aka kashe tare da raunata wasu da dama a jiya Laraba a wani sabon kisan kiyashi da jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai a wani gidan cin abinci na kasar Thailand da wata shahararriyar kasuwa a yammacin birnin Gaza.
Majiyoyi watsa labarai a Gaza sun rawaito cewa: Jiragen saman yakin mamayar Isra’ila sun kai wani hari kai tsaye kan gidan cin abinci na kasar Thailand da wata kasuwa mai farin jini da ke kusa, lamarin da ya yi sanadin shahadan mutane da dama da kuma jikkata wasu na daban yawancinsu fararen hula, a wani mummunan yanayi da ke nuni da yadda sojojin mamayar Isra’ila ke nuna rashin kula da rayukan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.
Wannan kisan kiyashi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tabarbarewar zubar da jini, inda adadin wadanda suka mutu sakamakon hare-haren bama-baman da sojojin mamaya suka kai kan wasu makarantu uku a sansanin ‘yan gudun hijira na Bureij da kuma gabashin birnin Gaza a cikin ‘yan sa’o’in da suka gabata suka kai mutane 49, wadanda akasarinsu yara ne, mata da kuma tsofaffi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
’Yan tawayen Houthi na Yemen sun yi barazanar cewa Amurka za ta gamu da fushinsu muddin ta kai wa Iran hari a rikicin da ya ɓarke tsakaninta da Isra’ila.
’Yan tawayen sun ce za su kai wa jiragen ruwan Amurka hare-hare a Tekun Bahar Rum, idan har Washington ta yi kuskuren shiga yaƙin da Isra’ila ta ƙaddamar wa Iran, duk kuwa da yarjejeniya tsagaita wuta da aka cimma a baya-bayan nan.
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — AbbaA cikin wani faifan bidiyo, kakakin ’yan tawayen Houthi Yahya Saree ya bayyana cewa, muddin Amurka ta kai wa Iran hari ko kuma ta shiga cikin wannan rikici, mayankansu za su ƙaddamar da farmaki kan muradun Amurkar da suka haɗa da jiragen yaƙi da kuma jiragen dakon kaya da ke zirga-zirga a Tekun Bahar Rum.
Wannan barazana ta ’yan tawayen Houthi na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donad Trump ya saka wa’adin makonni biyu domin yanke shawara a game da yiwuwar shiga rikicin da ya ɓarke tsakanin Isra’ila da Iran inda aka shiga mako na biyu suna yi wa juna ruwan bama-bamai.
Sai dai kuma tuni Amurkan ta ƙaddamar da hare-hare kan wasu cibiyoyin nukiliyar Iran kamar yadda Shugaba Donald Trump ya bayyana a daren Asabar wayewar gari Lahadi.