Falasdinawa da dama ne suka yi shahada tare da jikkata sakamakon hare-haren bama-bamai da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gidan abinci da wata shahararriyar kasuwa a Gaza

Akalla Falasdinawa 20 ne aka kashe tare da raunata wasu da dama a jiya Laraba a wani sabon kisan kiyashi da jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai a wani gidan cin abinci na kasar Thailand da wata shahararriyar kasuwa a yammacin birnin Gaza.

Sannan suka ci gaba da kai wasu hare-haren wuce gona da iri kan yankunan zirin Gaza a rana ta 213 a jere.

Majiyoyi watsa labarai a Gaza sun rawaito cewa: Jiragen saman yakin mamayar Isra’ila sun kai wani hari kai tsaye kan gidan cin abinci na kasar Thailand da wata kasuwa mai farin jini da ke kusa, lamarin da ya yi sanadin shahadan mutane da dama da kuma jikkata wasu na daban yawancinsu fararen hula, a wani mummunan yanayi da ke nuni da yadda sojojin mamayar Isra’ila ke nuna rashin kula da rayukan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

Wannan kisan kiyashi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tabarbarewar zubar da jini, inda adadin wadanda suka mutu sakamakon hare-haren bama-baman da sojojin mamaya suka kai kan wasu makarantu uku a sansanin ‘yan gudun hijira na Bureij da kuma gabashin birnin Gaza a cikin ‘yan sa’o’in da suka gabata suka kai mutane 49, wadanda akasarinsu yara ne, mata da kuma tsofaffi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

Akalla mutane 11 ne aka kashe a harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a unguwannin Kagara da San-Isa da ke karamar hukumar Kaura-Namoda a jihar Zamfara. Majiyoyi daga yankunan biyu sun shaida wa wakilinmu cewa an kai hare-haren ne a unguwannin Kagara da San-Isa tare da wasu kauyukan da ke kewaye. Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu? Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi Wata majiya daga dan garin Kagara wanda ya bayyana sunansa da Abubakar Sani ya shaidawa LEADERSHIP cewa ya rasa ‘yan uwansa guda biyu a harin wanda ya afku a ranar Asabar din da ta gabata. Ya ce, ‘yan fashin da suka yiwa kauyen su kawanya da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Asabar, sun yi awon gaba da shanu da sauran kayayyakin mutane tare da yin garkuwa da maza da mata zuwa cikin daji. Da yake zantawa da LEADERSHIP ta wayar tarho, wani mazaunin garin, Ahmed Dan-Isa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun kashe akalla mutanen kauyen 9 a ranakun Asabar da Lahadi da safe tare da yin garkuwa da wasu da dama da suka hada da maza da mata. Ahmed wanda ya ce ya tsere daga hare-haren ‘yan bindigar, amma ya ce, maharan sun mamaye kauyukan ba tare da fargabar jami’an tsaro ba. Ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta tarayya da su taimaka ta hanyar kubutar da daukacin Kaura-Namoda daga mummunan halin da take ciki. Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda (PPRO) na rundunar, Yazid Abubakar ya ci tura, domin lambar wayarsa a kashe take a lokacin hada wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Malaman Jami’o’in Isra’ila Sun Nemi Jamus Ta Tilasta Dakatar Da Yakin Gaza
  • Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
  • Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Yankin Jaffa Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • ’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa
  • Ɗaruruwan Tsaffin Jami’an Tsaron Isra’ila Sun Roki Trump Ya A Dakatar Da Yakin Gaza
  • Afirka ta Kudu ta zayyana matakan tallafi ga ‘yan kasuwa na cikin gida a matsayin martani ga harajin Trump
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Sojojin Isra’ila Sun Kashe Falasɗinawa A Wurin Rabon Abinci A Gaza