Gwamnatin Siriya Tana Neman Tattaunawa Da Gwamnatin Mamayar Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Published: 8th, May 2025 GMT
Fira ministan kasar Siriya ya bayyana cewa: Kasar Siriya zata gudanar da tattaunawa ba na kai tsaye ba da haramtacciyar kasar Isra’ila!
Shugaban gwamnatin rikon kwarya na kasar Siriya Abu Mohammed al-Julani ya sanar a jiya Laraba cewa: Kasar Siriya zata gudanar da zaman tattaunawa ba na kai tsaye ba da gwamnatin mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila ta hanyar masu shiga tsakani domin kwantar da hankulan al’amura da kuma hana bullar rashin kwanciyar hankali a yankin.
Al-Julani ya yi nuni da cewa: “Shisshigin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi ba bisa ka’ida ba ne, kuma sun bayyana cewa: Siriya ta amince da yarjejeniyar kawo karshen rikici ta shekara ta 1974,” yana mai cewa “Tsarin mulkin kasar Siriya zai tantance ‘yancin mayakan kasashen waje da iyalansu na samun takardar zama ‘yan kasa.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Isra ila kasar Siriya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
Kwamandan Ƙungiyar sa kai ta Vigilante Group of Nigeria (VGN) reshen Jihar Kaduna, Abdulwahab Muhammed ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta amince da Ƙungiyar a matakin ƙasa ta hanyar sanya hannu a kan ƙudurin da aka gabatar.
A cewar ƙungiyar bisa la’akari da irin rawar da take takawa wajen daƙile ayyukan miyagu da samar da tsaro a sassan ƙasar nan.
An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawaYa ce lokaci ya yi da gwamnati za ta sa hannu kan kudurin amincewa da kungiyar domin kasancewa cikin jerin hukumomin tsaro na kasa, la’akari da irin jajircewar da suke nunawa musamman a Jihar Kaduna.
Abdulwahab ya bayyana hakan ne yayin taron ƙarin girma da ƙungiyar ta shirya ga wasu jami’anta a Ƙaramar hukumar Jama’a, inda kuma aka karrama wasu fitattun mutane da ke ba da gudunmawa wajen tallafa wa ayyukan tsaro.
Kwamandan ya ce, suna da kyakkyawar fahimta da haɗin kai da sauran jami’an tsaro, inda suke miƙa waɗanda suka kama ga ’yan sanda don gudanar da bincike da yin hukunci bisa doka. Ya roƙi gwamnatin jihar Kaduna da ta ƙara tallafa musu da kayan aiki domin sauƙaƙa gudanar da ayyukansu.
Shi ma Shugaban karamar hukumar Jama’a Peter Tanko Dogara wanda sakataren Ƙaramar hukumar Jama’a, Dakta Shehu Usman Danbala ya wakilta, ya yaba da ƙoƙarin ƙungiyar wajen tabbatar da tsaro a matakin sa kai, tare da kiran al’umma da su riƙa basu cikakken goyon baya.