Iran Ta Ce Shirinta Na Makamashin Nukliya Na Zaman Lafiya Ne, Kuma Ba Zata Tattauna Da Amurka Karkashin Barazana Ba
Published: 10th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce shirin makamashin Nukliyar kasar Iran, na zaman lafiya ne, kuma babu wani shiri na samar da makaman Nukliya a cikinsa, sannan ya kara da cewa Iran ba za ta taba shiga tattaunawa da kasar Amurka mai cin zalin wasu kasashe ba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi ya na fadar haka a shafinsa na X a yau Litinin, ya kuma ce wannan ita ce martanin Iran a kan sakon da Amurka ta ce aikawa jami’an gwamnatin kasar Iran, na cewa su zabi tattaunawa ko yaki.
Kafin haka Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana hakan, ya kuma kara da cewa, kasashen yamma musamman Amurka ba su tuhumi Iran da kokarin mallakan makaman Nukliya ba, sai dai suna nufin tursasawa kasar ne, don ta mika kai garesu a kan dukkan al-amura.
Imam Khaminai ya kara da cewa, da Iran za ta mika kai dangane da shirinta na makamashin nukliya, da gobe kuma zasu ce, yaya batun makamanki masu linzami idan ta amin ce, sai su kawo batun siyasarta a gabasa ta tsakiya da sauransu. Don haka bukatunsu ba za su kare ba sai sun mamaye kasar gaba daya.
Ministan ya kammala da cewa, tattaubawan ta Trump yake kiran Iran zuwa gareshi tursasawa ne. idan da tana batun tattaunawa ne, da gaske. To da yarjeniyar JCPOA ya wadatar. Sai tunda wani abu ne daban, take amfani da tursasawa, wanda kuma yake iya kaiwa ga yaki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya yi Allawadai da harin da HKI ta kai wa Iran, wanda ya bayyana shi da cewa; Yana da hatsarin gaske, kuma ‘yan sahayoniyar sun yi hakan ne bisa cikakken goyon bayan Amurka.
Sheikh Na’im Kassim ya kuma bayyana cewa; Harin na ‘yan sahayoniya ba shi da wani dalili da ya wuce a rufe bakin gaskiya wanda yake taimakawa al’ummar Falasdinu a Gaza da ake yi wa kisan kiyashi, haka nan kuma taimakawa da goyon bayan gwgawarmayar Lebanon da dukkanin wannan yankin.
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa; Wannan harin da wuce gona da irin za iyi tasiri mai girma a cikin wannan yankin, sannan ya kara da cewa: Wannan harin ba zai wuce ba tare da fuskantar martani daga jamhuriyar musulunci ta Iran.
Haka nan kuma Na’im Kassim ya kara da cewa; Isra’ilawa makiya tare da Amurka ba za su taba yin tasiri akan hanyar da Iran ta zabarwa kanta ba ta gwgawarmaya ko kuma rawar da take takawa a cikin wannan yankin.
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya ce; Hizbullah da magoya bayanta, suna ci gaba da riko da tafarkin gwagwarmaya da kuma goyon bayan jamhuriyar musulunci ta Iran wajen kare hakkokinta.