Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce shirin makamashin Nukliyar kasar Iran, na zaman lafiya ne, kuma babu wani shiri na samar da makaman Nukliya a cikinsa, sannan ya kara da cewa Iran ba za ta taba shiga tattaunawa da kasar Amurka mai cin zalin wasu kasashe ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi ya na fadar haka a shafinsa na X a yau Litinin, ya kuma ce wannan ita ce martanin Iran a kan sakon da Amurka ta ce aikawa jami’an gwamnatin kasar Iran, na cewa su zabi tattaunawa ko yaki.

Kafin haka Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana hakan, ya kuma kara da cewa, kasashen yamma musamman Amurka ba su tuhumi Iran da kokarin mallakan makaman Nukliya ba, sai dai suna nufin tursasawa kasar ne, don ta mika kai garesu a kan dukkan al-amura.

Imam Khaminai ya kara da cewa, da Iran za ta mika kai dangane da shirinta na makamashin nukliya, da gobe kuma zasu ce, yaya batun makamanki masu linzami idan ta amin ce, sai su kawo batun siyasarta a gabasa ta tsakiya da sauransu. Don  haka bukatunsu ba za su kare ba sai sun mamaye kasar gaba daya.

Ministan ya kammala da cewa, tattaubawan ta Trump yake kiran Iran zuwa gareshi tursasawa ne. idan da tana batun tattaunawa ne, da gaske. To da yarjeniyar JCPOA ya wadatar. Sai tunda wani abu ne daban, take amfani da tursasawa, wanda kuma yake iya kaiwa ga yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran

Wani manazarci na Amurka ya bayyana sansanonin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da Iran ta kaiwa hare-hare

Wani manazarci Ba’amurke ya tattara jerin sansanonin da Iran ta kai wa hare-harer a wata makala inda ya bayyana cewa: Iran ta samu nasara a yakin da ta yi da ‘yan sahayoniyya.

Wani mai sharhi kan harkokin siyasa da ke zaune a birnin Washington Mike Whitney ya yi nazari kan dalilan da ba a bayyana dalilan da suka sa Iran ta yi nasara kan haramtacciyar kasar Isra’ila ba a yakin kwanaki 12 a wani bincike da ya gudanar.

Yana mai cewa; “Me yasa ba zato ba tsammani gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta amince da tsagaita bude wuta da Iran?” Whitney ta rubuta a cikin wannan bincike a cikin mujallar Bincike ta Duniya. “Wannan tambaya ce da kafafen yada labarai na Yamma ba su amsa ba, da ke sanya al’ummar Amurka cikin duhu. Watakila kun ji cewa tsaron sararin samaniyar Isra’ila na gab da rugujewa, lamarin da ya bar ta cikin hadari ga hare-haren Iran, amma wannan wani bangare ne na labarin kawai.

Ya kara da cewa: Kasa da makonni biyu da fara wannan rikici, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta mika wuya, Iran tana lalata muhimman wuraren a Isra’ila daya bayan daya bisa zurfin tunani da karfi, ba tare da nuna wata alamar ja da baya ba, don haka Isra’ila ba ta da wani zabi illa amincewa da shan kaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Yahudawan Iran Ya Tuhumi Isra’ila Da Fakewa A Karkashin Addini
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Iran Ta Musanta Neman Ci Gaba Da Gudanar Da Tattaunawa Da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliyar Kasar Idan Tanaso
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliya Kasar Idan Tanaso
  • Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi