Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce shirin makamashin Nukliyar kasar Iran, na zaman lafiya ne, kuma babu wani shiri na samar da makaman Nukliya a cikinsa, sannan ya kara da cewa Iran ba za ta taba shiga tattaunawa da kasar Amurka mai cin zalin wasu kasashe ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi ya na fadar haka a shafinsa na X a yau Litinin, ya kuma ce wannan ita ce martanin Iran a kan sakon da Amurka ta ce aikawa jami’an gwamnatin kasar Iran, na cewa su zabi tattaunawa ko yaki.

Kafin haka Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana hakan, ya kuma kara da cewa, kasashen yamma musamman Amurka ba su tuhumi Iran da kokarin mallakan makaman Nukliya ba, sai dai suna nufin tursasawa kasar ne, don ta mika kai garesu a kan dukkan al-amura.

Imam Khaminai ya kara da cewa, da Iran za ta mika kai dangane da shirinta na makamashin nukliya, da gobe kuma zasu ce, yaya batun makamanki masu linzami idan ta amin ce, sai su kawo batun siyasarta a gabasa ta tsakiya da sauransu. Don  haka bukatunsu ba za su kare ba sai sun mamaye kasar gaba daya.

Ministan ya kammala da cewa, tattaubawan ta Trump yake kiran Iran zuwa gareshi tursasawa ne. idan da tana batun tattaunawa ne, da gaske. To da yarjeniyar JCPOA ya wadatar. Sai tunda wani abu ne daban, take amfani da tursasawa, wanda kuma yake iya kaiwa ga yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN

Babbar Mai Shari’ar ta kasa , Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta jaddada cewa alkalai suna da nauyin tabbatar da adalci cikin gaskiya da daidaito a lokacin da matsalolin tattalin arziki ke kara tsananta wa al’umma.

Ta bayyana haka ne a Taron Alkalai na Shekara-shekara Karo na 26, wanda Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci ta Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ta shirya tare da haɗin gwiwar Cibiyar Koyar da Ayyukan Shari’a ta Kasa (NJI), a harabar Jami’ar da ke Kongo, Zariya.

Mai Shari’a Kekere-Ekun, wadda Sakatare na NJI, Barista Abdulazeez Aluwo ya wakilta, ta ce dole ne kotuna su yi hukunci da ke la’akari da yanayin tattalin arziki da kuma hakkokin masu nema da wadanda ake binsu hukunci.

Ta ce hakan ne kadai zai tabbatar da zaman lafiya da daidaiton al’umma.

Barista Abdulazeez Aluwo

CJN ta yi nuni da cewa rikice-rikicen harkokin kuɗi na zamani kamar hauhawar farashi da faduwar darajar naira, da canjin musayar kuɗi suna buƙatar tsantsar fassarar hukunce-hukuncen Shari’a bisa ilimi na zamani.

Ta yi kira da a kafa Kwamitin Tuntuba da zai kunshi Alkalai na kotu daukaka kara da Khadi da Manyan malamai na Shari’a da Kwararru a fannin kuɗi na zamani.

A cewarta, wannan kwamiti zai taimaka wajen ba kotuna jagoranci kan sabbin al’amuran da ke tasowa, tare da wayar da kan jama’a a kan dokokin kuɗin Shari’a.

Tun da farko, Daraktan Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci, Dakta. Sa’ad Abubakar, ya ce faduwar darajar kuɗi da hauhawar farashi suna barazana ga mu’amalar kasuwanci da aiwatar da shari’a.

Ya ce wannan al’amari na kara jefa kotunan Shari’a cikin matsaloli, musamman wajen tabbatar da adalci kan batutuwa masu alaƙa da mu’amaloli.

A sakonsa Mai martaba, Sarkin Zazzau, Mal. Ahmed Nuhu Bamalli wanda Wazirin Zazzau Khadi Muhammad Inuwa Aminu ya wakilta, ya bukaci a hanzarta gyare-gyare a fannin Shari’a, musamman saboda yadda matsalar tattalin arziki ke shafar shari’o’in hul’i, da sadaki da dai sauransu.

Ana Shi bangare, Shugaban NJI, Mai Shari’a Babatunde Adejumo wanda Barista Zainab Salim ta wakilta ya yabawa sabon MOU da aka kulla tsakaninsu da ABU a fannin horaswa da bincike, da jagoranci da kuma inganta cancanta.

Ya ce taken taron na bana ya dace matuka, domin ya shafi manyan hakkoki na Shari’a kamar bashi da gado da sadaki, da mu’amaloli na yau da kullum.

Da yake Jawabi, Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Adamu Ahmad, Wanda Mataimakinsa a fannin Sha’anin Mulki Farfesa Suleiman Sabo ya wakilta ya ce taron alkalai na shekara–shekara muhimmin mataki ne da ke zurfafa tattaunawar shari’a da bunkasa bincike a fannin Shari’a a Najeriya.

A jawabinsa, tsohon Daraktan Cibiyar, Farfesa Muhammad Bello Usman, ya jaddada cewa adalci ba zai samu ba sai an dora nauyi da alhaki a kan mutanen da suka cancanta da kwarewa.

Taken Taron Shi ne : Shari’a a Yanayin Tattalin Arzikin Zamani: Tasirin Darajar Kuɗi da Canjin Musayar Kuɗi a Kan dokokin Shari’a.

Daga Ibrahim Suleiman 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon  Dake Takawa Makiya Birki
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Larijani Iran Tana Maraba Da Tattaunawa Ta Gaskiya Amma Ba Tsararren Sakamako Ba
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya