Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce shirin makamashin Nukliyar kasar Iran, na zaman lafiya ne, kuma babu wani shiri na samar da makaman Nukliya a cikinsa, sannan ya kara da cewa Iran ba za ta taba shiga tattaunawa da kasar Amurka mai cin zalin wasu kasashe ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi ya na fadar haka a shafinsa na X a yau Litinin, ya kuma ce wannan ita ce martanin Iran a kan sakon da Amurka ta ce aikawa jami’an gwamnatin kasar Iran, na cewa su zabi tattaunawa ko yaki.

Kafin haka Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana hakan, ya kuma kara da cewa, kasashen yamma musamman Amurka ba su tuhumi Iran da kokarin mallakan makaman Nukliya ba, sai dai suna nufin tursasawa kasar ne, don ta mika kai garesu a kan dukkan al-amura.

Imam Khaminai ya kara da cewa, da Iran za ta mika kai dangane da shirinta na makamashin nukliya, da gobe kuma zasu ce, yaya batun makamanki masu linzami idan ta amin ce, sai su kawo batun siyasarta a gabasa ta tsakiya da sauransu. Don  haka bukatunsu ba za su kare ba sai sun mamaye kasar gaba daya.

Ministan ya kammala da cewa, tattaubawan ta Trump yake kiran Iran zuwa gareshi tursasawa ne. idan da tana batun tattaunawa ne, da gaske. To da yarjeniyar JCPOA ya wadatar. Sai tunda wani abu ne daban, take amfani da tursasawa, wanda kuma yake iya kaiwa ga yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka

Gwamnatin Tarayya ta ɗora alhakin dawowar hare-haren ta’addanci, ciki har da sace dalibai mata a jihar Kebbi da kai hari a coci a jihar Kwara, kan kalaman da Amurka ta yi kwanan nan a kan Najeriya.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya ce sakonnin da Shugaban Amurka Donald Trump ya wallafa, inda ya zargi Najeriya da “kisan kiyasin Kiristoci” tare da barazanar tura sojojin kasarsa, sun kara wa wasu ƙungiyoyin ’yan ta’adda kaimin kai hare-hare.

Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano

“Kalaman da Amurka ta yi kwanan nan sun kara wa wasu ƙungiyoyin masu tayar da kayar baya da ke son amfani da labaran ƙasashen waje kai hare-hare kan wuraren da ba su da kariya kaimi,” in ji Akume a ranar Laraba.

Yayin da yake magana kan yadda ta’addanci, hare-haren ’yan bindiga da matsalolin tsaro ke ci gaba da sauyawa a ƙasar, Sakataren Gwamnatin ya ƙara da cewa: “Kafin waɗannan kalaman, an riga an raunana ƙungiyoyin ta’addanci sosai, kuma sun rage kai kananan hare-haren daji. Wannan dawowa ya nuna muhimmancin haɗin gwiwa, ba wai Magana kawai ba, tsakanin Najeriya da Amurka.”

Trump, a jerin sakonnin da ya wallafa a shafin X tsakanin 30 ga watan Oktoba da 1 ga Nuwamba, 2025, ya ayyana Najeriya a matsayin “Ƙasa mai Matsala ta Musamman” saboda zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi.

Shugaban Amurka ya yi gargadin cewa zai iya tura sojojin Amurka zuwa Najeriya idan kisan da ake zargin bai tsaya ba.

Ya ce tuni ya umarci Ma’aikatar Yaƙi ta kasar da ta fara shirin yiwuwar daukar matakin soja idan tashin hankali ya ci gaba.

Trump ya kuma yi barazanar dakatar da dukkan taimakon Amurka ga Najeriya idan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta kasa magance abin da ya kira zaluntar Kiristoci.

A cikin jawabin da SGF ya yi a ranar Laraba, ya ce an riga an raunana cibiyoyin ta’addanci sosai kuma sun rage zuwa kananan hare-haren daji kafin waɗannan kalaman.

“Wasu ƙungiyoyi yanzu suna ƙoƙarin amfani da waɗannan kalaman don samun suna,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa a cikin makon nan ne dai wasu ’yan bindiga suka sace dalibai 25 a makarantar sakandaren kwana ta GCGSS Maga da ke jihar Kebbi.

Kazalika, a cikin makon kuma ta wasu maharani sun farmaki wasu masu ibada a wani coci da ke Eruku a jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Wani Tsohon Ma’aikacin CIA Ya Ce HKI Ta Yi Barazanar Amfani Da Makaman Nukliya Kan Iran
  • Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara
  • IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Amurka ta Shawarci Ukraine ta amince da yankunan da Rasha ta mamaye mata
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: A Yanzu Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Daraktar Hukumar IAEA Ya Ce: Suna Tuntubar Juna Da Iran Kuma Masu Bincikensu Sun Kamo Kasar