Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce shirin makamashin Nukliyar kasar Iran, na zaman lafiya ne, kuma babu wani shiri na samar da makaman Nukliya a cikinsa, sannan ya kara da cewa Iran ba za ta taba shiga tattaunawa da kasar Amurka mai cin zalin wasu kasashe ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi ya na fadar haka a shafinsa na X a yau Litinin, ya kuma ce wannan ita ce martanin Iran a kan sakon da Amurka ta ce aikawa jami’an gwamnatin kasar Iran, na cewa su zabi tattaunawa ko yaki.

Kafin haka Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana hakan, ya kuma kara da cewa, kasashen yamma musamman Amurka ba su tuhumi Iran da kokarin mallakan makaman Nukliya ba, sai dai suna nufin tursasawa kasar ne, don ta mika kai garesu a kan dukkan al-amura.

Imam Khaminai ya kara da cewa, da Iran za ta mika kai dangane da shirinta na makamashin nukliya, da gobe kuma zasu ce, yaya batun makamanki masu linzami idan ta amin ce, sai su kawo batun siyasarta a gabasa ta tsakiya da sauransu. Don  haka bukatunsu ba za su kare ba sai sun mamaye kasar gaba daya.

Ministan ya kammala da cewa, tattaubawan ta Trump yake kiran Iran zuwa gareshi tursasawa ne. idan da tana batun tattaunawa ne, da gaske. To da yarjeniyar JCPOA ya wadatar. Sai tunda wani abu ne daban, take amfani da tursasawa, wanda kuma yake iya kaiwa ga yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewar an ceto dukkanin mutanen da mahara suka sace a wata coci a yankin Eruku na Jihar Kwara.

’Yan bindigar sun sace masu ibadar ne a ranar Talata, lokacin da suka kai hari cocin Christ Apostolic Church (CAC) da ke Oke Isegun a Eruku, wani gari da ke iyaka da Kogi a Karamar Hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.

ISWAP ta sace ’yan mata 13 a Borno Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji

A cikin wani sako da Tinubu ya wallafa a X a ranar Lahadi, ya ce yana bibiyar yanayin tsaro a fadin kasar nan, kuma zai tabbatar da cewa gwamnatinsa ta kare ’yan Najeriya.

An yada bidiyon yadda maharan suka shiga cocin suka yi awon gaba da masu ibada yayin da suke tsaka da addu’a.

Lokacin da maharan suka dinga harbe-harbe a ciki cocin, wani Fasto ya jagoranci jama’a inda suka nemi mafaka.

Ya kuma ce an ceto dalibai 51 da aka sace a Jihar Neja.

Tinubu ya kara da cewa: “’Yan uwana ’yan Najeriya, za ku iya tuna cewa na soke zuwa taron G20 da aka yi a Afirka ta Kudu domin na mayar da hankali kan sha’anin tsaro a gida.

“Ina yi wa jami’an tsaro godiya kan aiki tukuru da suka cikin kwanaki biyun da suka wuce, an ceto dukkanin masu ibada 38 da aka sace a Eruku, a Jihar Kwara.

“Ina kuma farin ciki cewa an gano dalibai 51 daga cikin wadanda aka sace a wata makaranta a Jihar Neja.

“Ina bibiyar sha’anin tsaro sosai kuma ina samun rahotanni kai-tsaye. Ba zan yi kasa a gwiwa ba. Kowane dan Najeriya yana da ’yancin samun tsaro, kuma a karkashin jagorancina, za mu kare wannan kasa da mutanen ciki.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya
  • Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen
  • Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • Iran Da Omman Sun Tattauna Kan Al-Amuran Yankin Da Kuma Dangantaka Tsakaninsu
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji
  • An Fitar Da Kudurin Bayan Taron Kungiyar G20 Ba Tare Da Halartar Kasar Amurka Ba