Iran Ta Ce Shirinta Na Makamashin Nukliya Na Zaman Lafiya Ne, Kuma Ba Zata Tattauna Da Amurka Karkashin Barazana Ba
Published: 10th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce shirin makamashin Nukliyar kasar Iran, na zaman lafiya ne, kuma babu wani shiri na samar da makaman Nukliya a cikinsa, sannan ya kara da cewa Iran ba za ta taba shiga tattaunawa da kasar Amurka mai cin zalin wasu kasashe ba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi ya na fadar haka a shafinsa na X a yau Litinin, ya kuma ce wannan ita ce martanin Iran a kan sakon da Amurka ta ce aikawa jami’an gwamnatin kasar Iran, na cewa su zabi tattaunawa ko yaki.
Kafin haka Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana hakan, ya kuma kara da cewa, kasashen yamma musamman Amurka ba su tuhumi Iran da kokarin mallakan makaman Nukliya ba, sai dai suna nufin tursasawa kasar ne, don ta mika kai garesu a kan dukkan al-amura.
Imam Khaminai ya kara da cewa, da Iran za ta mika kai dangane da shirinta na makamashin nukliya, da gobe kuma zasu ce, yaya batun makamanki masu linzami idan ta amin ce, sai su kawo batun siyasarta a gabasa ta tsakiya da sauransu. Don haka bukatunsu ba za su kare ba sai sun mamaye kasar gaba daya.
Ministan ya kammala da cewa, tattaubawan ta Trump yake kiran Iran zuwa gareshi tursasawa ne. idan da tana batun tattaunawa ne, da gaske. To da yarjeniyar JCPOA ya wadatar. Sai tunda wani abu ne daban, take amfani da tursasawa, wanda kuma yake iya kaiwa ga yaki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kuɗin Cizo ya tilasta rufe fitacciyar sinima a Faransa
Wata fitacciyar sinima a Faransa, Cinematheque Francaise, ta rufe ɗakunan kallonta na tsawon wata guda saboda yaɗuwar kuɗin cizo da aka gano a cikinta
Cibiyar wadda ke gabashin birnin Paris ta ce rufe sinimar zai ba ta damar tabbatar da cewa masu kallo sun samu “aminci da kwanciyar hankali” bayan ƙorafe-ƙorafen da aka yi na cewa ƙwarin suna cizon mutane a lokacin kallon fina-finai.
Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32 Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — AtikuA farkon watan Nuwamba, wasu daga cikin masu kallo sun shaida wa kafafen yada labarai cewa ƙwarin sun cije su bayan wani taro da aka yi da shahararriyar ’yar fim ɗin Hollywood, Sigourney Weaver.
Wani daga cikinsu ya ce an ga kuɗin cizon yana yawo a kujeru da kuma jikin tufafi.
Cinematheque ta bayyana cewa za a cire dukkan kujerun ɗakunan kallo, a kuma bi su da busasshen tururi mai zafin digiri 180 a ma’unin selshiyus. Haka kuma kafet da sauran wurare za su sami irin wannan tsaftacewa.
Duk da rufewar ɗakunan kallo huɗu, sauran sassan ginin cibiyar za su ci gaba da aiki, ciki har da wani baje kolin da ake yi game da fitaccen ɗan wasan Amurka, Orson Welles.
A shekarar 2023, Faransa ta fuskanci yaɗuwar kuɗin cizo a manyan birane, musamman a gidajen sinima, asibitoci da motocin jama’a, lamarin da ya ta da hankalin jama’a kafin Gasar Olympics ta Paris 2024.