Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce shirin makamashin Nukliyar kasar Iran, na zaman lafiya ne, kuma babu wani shiri na samar da makaman Nukliya a cikinsa, sannan ya kara da cewa Iran ba za ta taba shiga tattaunawa da kasar Amurka mai cin zalin wasu kasashe ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi ya na fadar haka a shafinsa na X a yau Litinin, ya kuma ce wannan ita ce martanin Iran a kan sakon da Amurka ta ce aikawa jami’an gwamnatin kasar Iran, na cewa su zabi tattaunawa ko yaki.

Kafin haka Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana hakan, ya kuma kara da cewa, kasashen yamma musamman Amurka ba su tuhumi Iran da kokarin mallakan makaman Nukliya ba, sai dai suna nufin tursasawa kasar ne, don ta mika kai garesu a kan dukkan al-amura.

Imam Khaminai ya kara da cewa, da Iran za ta mika kai dangane da shirinta na makamashin nukliya, da gobe kuma zasu ce, yaya batun makamanki masu linzami idan ta amin ce, sai su kawo batun siyasarta a gabasa ta tsakiya da sauransu. Don  haka bukatunsu ba za su kare ba sai sun mamaye kasar gaba daya.

Ministan ya kammala da cewa, tattaubawan ta Trump yake kiran Iran zuwa gareshi tursasawa ne. idan da tana batun tattaunawa ne, da gaske. To da yarjeniyar JCPOA ya wadatar. Sai tunda wani abu ne daban, take amfani da tursasawa, wanda kuma yake iya kaiwa ga yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Rashin Bincike Ke Haifar Da Yawaitar Mutuwar Aure

Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor) daga Jihar Kano:

Laifi ai na iyayenta ne me ya sa basu yi bincike ba kafin azo wannan gabar. Ya kamata ace ana yin buncike kamar yadda a baya al’adar Malam bahushe ce buncike kafin Aure daga bangaren mijin har na matar. Wani yana gudun kar ya fadi aibin dansa ko ‘yarsa a karshe su rasa masu Aurensu, wanda hakan babbar matsala ce. Ka fadi gaskiya idan mutum ya ga zai iya to, shikenan in ba zai iya ba Allah ya kawo wani.

 

Sunana Khadija Auwal Koki, A Jihar Kano:

Eh to, gaskiya laifin mijin ne da kuma danginsa tunda an san maganar aure ba wasa bace ya kamata ace an fadawa juna gaskiya. Ya kamata iyaye su yi bincike da yawa, wajan tabbatar da nagarta da kuma mutuncin dan da za su bawa ‘yarsu, haka shi ma ayi bincike sosai akan yarinyar da zai aura. Da yawan mutane wasu da dama suna zabar su boye gaskiya sun fi san su fito da garya, suna ganin kamar za su fi karbuwa. Bacin ita kuma gaskiya daya ce ramin karya kuma kurarre ne. Idan har ba wani dalili ne mara kyau ba wanda ko da an yi auran za a yi da-na-sani ya sa za a fasa auran ba. To, a ganina a daina soke aure kawai ayi addu’a da fatan alkairi.

 

Sunana Hafsat Sa’eed

Tun farkon da suka fara soyayya zai aure ta, kamata yayi ayi bincike akai aga shi wane ne, kuma daga ina yake. Wani lokacin matsala daga iyaye ne, basa tsayawa su yi bincike, wani lokacin sukan dauki abin da yarinya ta zo da shi, wani lokacin akan sami akasarin matsala daga mazaje, su zo su yi maka karya su ce ga yadda suke, alhalin ba hakan suke ba. Ko kuma inda za a je a yi binciken su yi karya akan abin da za su fada, sai ka shiga gidan sai ka ga ba haka ba.

 

Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos a Jihar Filato:

Kamar yadda addinin Musulunci yake koyarwa, bincike yana da matukar muhimmanci, yayin neman aure. Ba kawai binciken tushe ko asalin zuriya da tsatson wanda ake nema da mai nema ba ne, har ma da abin da ya shafi lafiya. Ma’aikin Allah (SAW) a wani hadisi ya tsawatar da sahabbansa daga auren mace daga gidan da bashi da tarbiyya ko tarihi mai kyau, komai kyanta. Don haka za mu fahimci cewa, lallai binciken dangin mata ko miji wajibi ne a addini, kodayake sau da dama soyayya da gaggawa tana rufe mana ido, da hana mu tsayawa mu yi bincike kan wadanda za mu aura. A irin haka ne ake samun zuriya da za su taso da wasu irin bakin al’amura, kamar sata, shaye-shaye, zinace-zinace da ta’addanci, wadanda masana suka ce duk ana gadonsu ne daga iyaye da kakanni. Lallai yana da kyau iyaye da masu shirin aure su natsu su daina gaggawa, su tabbatar sun zabawa ‘ya’yansu abokan zama nagari, da samun zuriya masu albarka.

 

Sunana Princess Fatima Mazadu, Goben Nigeria:

Cab! Babbar magana, da farko dai Allah ya kyauta ya kuma kawo mana karshen wannan fashe-fashen auren da ake yi a zamanin nan, dan abu ne mai ciwo bayan iyaye sun gama shiryawa ‘ya’yansu, na ta yata jalje da yi mata addu’ar ubangiji ya bata wanda ya fi shi alkairi. Gaskiya mafi akasarin fasa auren zamanin nan gwajin jini, rashin amincewar zuriyoyi guda biyu, rashin yarda da juna wato zuciya na kokonto, da rashin tauhidi na arziki ko wadata. Za ki ga mutum ko gobe ne in wata asara ta hau masa sai an yi canfi ta fannin mace ko namiji. Dukka sunada laifi, Fannin makota da ‘yan’uwa, saboda soyayya ko biyan bukata da gajiyarwa zaman gwaurantaka. Shawara subi a hankali gudun rikicewar al’amari ana tsaka da yi.

 

Sunana Fatima Nura kila, A Jihar Jigawa:

A ganina laifi ne na bangaren amarya, domin matukar an yi kyakkaywan bincike komai zai bayyana, sabida bincike a aure yana da matukar amfani. Iyaye ya kama su tsananta bincike musamman wajen aikinsa da kuma garinsu da guraren da yake yawan ziyarta. Kwadayi da kuma san duniya matukar mace ko namiji tana da kudi wasu sukan ki bincike, koda wani a dangi yace ayi sai a fara hassada yake ku rabu da shi. Shawara ita ce a kodayaushe muna zurfafa bincike, musamman lamari na aure, domin rayuwa ne ake san ginawa har karshen rayuwa.

 

Sunana Aisha T. Bello, daga Jihar Kaduna:

Wanan matsalar na faruwa sosai wasu ba sa bincike su san wanda za su bawa auren diyar su, mafi yawanci idan mai kudi ya zo babu wani bincike sai kawai ya bashi. Yanzu kuma duniya ta canza duk in da za ka je bincike babu wanda zai gaya maka gaskiya ko an sani kuwa. Wasu suna jin tsoron yin haka saboda in tayi dadi kada ace sune. Gaskiya haka ta faru a gidanmu da muka tura bincike sai da a ka fada masa an zo bincike. Shawarata dan Allah mutane in an zo bincike kan aure su fadi tsakani su da Allah abun da suka sani kan mutun ban da karya, kada su fadi abu da ba halinsa bane. Su kuma iyayenmu Allah ya basu damar duba wanda yaransu za su aura. Bsnce basa kokari ba, amma su wara sosai, Allah ya shige mana gaba (Amin).

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Taskira Matsalar Rashin Yarda Tsakanin Ma’aurata December 7, 2025 Taskira Yadda Wasu Mahukunta Ke Amfani Da Muƙamansu Wajen Musguna Wa Al’umma November 22, 2025 Taskira Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba November 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tayi Tir Da Hare-Haren Sydney Na Kasar Austaralia
  • Yadda Rashin Bincike Ke Haifar Da Yawaitar Mutuwar Aure
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji