Jakadan kasar Rasha na din din din a cibiyoyin MDD da suke Vienna, ya bayyana cewa dakatar da aiwatar da yarjeniyar shirin Nukliya na kasar Iran wanda ake kira JCPOA, wacce kuma aka samar da shi a shekara ta 2015, da kasashen yamma suka yi, shi ne ya haddasa dukkan matsalolin da suka biyo baya.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto, Mikhail Awliyonov yana fadar haka a hirar da ta hada shi da jaridar Ezustiyo na kasar Rasha.

Jakadan ya kara da cewa a tsakanin shekara ta 2021 da kuma 2022 an tattauna da kasashen yamma kan yadda za’a aiwatar da yarjeniyar JCPOA da kasashen bayan da kasar Amurka ta fice daga yarjeniyar a shekara ta 2018, amma sai kasashen yamma suka yi watsi da  ita sannan suka dorawa kasar Iran sabbin takunkuman tattalin arziki. Jakadan ya kuma kara da cewa a halin yanzu ba za’a warware wadannan matsalolin da suke tasowa kan shirin Nukliyar kasar Iran ba, sai an dawo kan yarjejeniyar ta JCPOA, sannan wadannan kasashen su mayarwa Iran hakkokinta da suka take a cikinta, wadanda suka kaita ga maida martanin da ta yi.

Ya ce, a halin yanzu shekaru ukku sun gabata da yin watsi da yarjeniyar, sannan har yanzun kasar Iran bada sabawa yarjeniyar ba, wanda ya kai ga yarjeniyar zata mutu a cikin watan Octoban shekara ta 2025 da muke ciki. Jakadan ya ce har yanzun ba’a da wani abu da zai maye gurbin yarjeniyar ta JCPOA. Wanda ke samun goyon bayan kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2231.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14

Ministan ayyuka da sufuri na kasar Lebanon Yusuf Rasamani ya bayyana cewa; Asarar da HKI ta jazawa kasar Lebanon a lokacin yaki ta kai dalar Amurka biliyan 14, tare da bayyana cewa kasar Rasha ta bijiro da cewa za ta taimaka.

Rasamani ya fada wa Radiyon “Sputnik” na Rasha cewa; Suna ci gaba da aiki tare da babban bankin duniya, domin tantance barnar da yakin Isra’ila ya haddasa a Lebanon.”

Bugu da kari ministan ayyukan na kasar Lebanon ya kuma ce; Ma’aikatar ta fara aikin debe baraguzai a cikin garuurwan da za su iya isa, wadanda babu sojojin HKI a cikinsu.”

Haka nan kuma ya ce; Kasar ta Lebanon da kuma Bankin Duniya da Asusun bayar da Lamuni suna aiki domin fito da tsarin aiki na sake gina wuraren da yakin ya rusa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Baka’i: Za Mu Mayar Da Martani Akan Wasikar Trump Bayan Yin Nazari
  • Iran Ta Yaba Da Yarjeniyar  Zaman Lafiya Da Aka Cimma Tsakanin Kasashen Armenia Da Azerbaijan
  • Kasar Habasha Ta Bukaci Kasashen Afirka Su Bunkasa Ciyar Yaki Da Cututtuka CDC Da Kungiyar
  • Kofar JMI A Bude Take Don Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen JMI Ta Yi Allawadai Da Kungiyar G7 Wacce Ta Zargin Kasar Da Abubuwa Da Dama
  • An kama malama tana lalata da ɗalibinta
  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  • Amurka Ta Ba Jakadan Afirka ta Kudu Sa’o’i 72 Ya fice daga kasar
  • Rasha Za Ta Kara Yawan Alkamar Da Take Kai Wa Kasashen Afirka
  •  Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14