Jakadan kasar Rasha na din din din a cibiyoyin MDD da suke Vienna, ya bayyana cewa dakatar da aiwatar da yarjeniyar shirin Nukliya na kasar Iran wanda ake kira JCPOA, wacce kuma aka samar da shi a shekara ta 2015, da kasashen yamma suka yi, shi ne ya haddasa dukkan matsalolin da suka biyo baya.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto, Mikhail Awliyonov yana fadar haka a hirar da ta hada shi da jaridar Ezustiyo na kasar Rasha.

Jakadan ya kara da cewa a tsakanin shekara ta 2021 da kuma 2022 an tattauna da kasashen yamma kan yadda za’a aiwatar da yarjeniyar JCPOA da kasashen bayan da kasar Amurka ta fice daga yarjeniyar a shekara ta 2018, amma sai kasashen yamma suka yi watsi da  ita sannan suka dorawa kasar Iran sabbin takunkuman tattalin arziki. Jakadan ya kuma kara da cewa a halin yanzu ba za’a warware wadannan matsalolin da suke tasowa kan shirin Nukliyar kasar Iran ba, sai an dawo kan yarjejeniyar ta JCPOA, sannan wadannan kasashen su mayarwa Iran hakkokinta da suka take a cikinta, wadanda suka kaita ga maida martanin da ta yi.

Ya ce, a halin yanzu shekaru ukku sun gabata da yin watsi da yarjeniyar, sannan har yanzun kasar Iran bada sabawa yarjeniyar ba, wanda ya kai ga yarjeniyar zata mutu a cikin watan Octoban shekara ta 2025 da muke ciki. Jakadan ya ce har yanzun ba’a da wani abu da zai maye gurbin yarjeniyar ta JCPOA. Wanda ke samun goyon bayan kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2231.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta jaddada cewa Ta’addancin yahudawan sahayoniyya kan Iran laifi ne na yaki da ya zama wajibi duniya ta yi mata hukunci a kai

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya yi kira da a dorawa mahukuntan yahudawan sahayoniyya alhakin munanan laifukan da suka aikata a kan al’ummar Iran, musamman a lokacin da ake ci gaba da kai hare-hare a birnin Tehran fadar mulkin kasar da sauran garuruwan kasar ta Iran.

A wani sakon da ya wallafa a dandalin X a yau Asabar, Baqa’i ya ce, “Harin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a asibitoci da kurkukun Evin a ranar 24 ga Yunin wannan shekara ta 2025, wanda ya yi sanadin shahadar fararen hula da ma’aikata da kuma masu shigewa  da yawansu ya kai mutane 79, yana cikin laifukan yaki da kuma keta dokar jin kai ta kasa da kasa.”

Ya yi nuni da cewa, harin ya afku ne a daidai lokacin da iyalan fursunonin ke taruwa domin ziyartar ‘yan uwansu, kuma sun makale a karkashin baraguzan ginin inda suka yi shahada sakamakon harin wuce gona da iri na jirgin saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
  • Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu
  • An Gudanar Da Taron Girmama Shahidan Yakin Kwanaki 12 A Nan Tehran