Rasha Ta Ce Babu Wani Abinda Zai Maye Gurbin Yarjejeniyar JCPOA Ta Shirin Nukliyar Kasar Iran
Published: 10th, March 2025 GMT
Jakadan kasar Rasha na din din din a cibiyoyin MDD da suke Vienna, ya bayyana cewa dakatar da aiwatar da yarjeniyar shirin Nukliya na kasar Iran wanda ake kira JCPOA, wacce kuma aka samar da shi a shekara ta 2015, da kasashen yamma suka yi, shi ne ya haddasa dukkan matsalolin da suka biyo baya.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto, Mikhail Awliyonov yana fadar haka a hirar da ta hada shi da jaridar Ezustiyo na kasar Rasha.
Jakadan ya kara da cewa a tsakanin shekara ta 2021 da kuma 2022 an tattauna da kasashen yamma kan yadda za’a aiwatar da yarjeniyar JCPOA da kasashen bayan da kasar Amurka ta fice daga yarjeniyar a shekara ta 2018, amma sai kasashen yamma suka yi watsi da ita sannan suka dorawa kasar Iran sabbin takunkuman tattalin arziki. Jakadan ya kuma kara da cewa a halin yanzu ba za’a warware wadannan matsalolin da suke tasowa kan shirin Nukliyar kasar Iran ba, sai an dawo kan yarjejeniyar ta JCPOA, sannan wadannan kasashen su mayarwa Iran hakkokinta da suka take a cikinta, wadanda suka kaita ga maida martanin da ta yi.
Ya ce, a halin yanzu shekaru ukku sun gabata da yin watsi da yarjeniyar, sannan har yanzun kasar Iran bada sabawa yarjeniyar ba, wanda ya kai ga yarjeniyar zata mutu a cikin watan Octoban shekara ta 2025 da muke ciki. Jakadan ya ce har yanzun ba’a da wani abu da zai maye gurbin yarjeniyar ta JCPOA. Wanda ke samun goyon bayan kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2231.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano
Yunƙurin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, na kafa wata rundunar tsaro mai kama da Hisbah ya jawo ce-ce-ku-ce a faɗin jihar.
Wannan shiri da ya kira Hisbah mai zaman kanta, an tsara shi ne domin ɗaukar ma’aikata 12,000 waɗanda gwamnatin Kano mai ci ta sallama daga a Hukumar Hisbah.
Sanarwar ta haifar da ra’ayoyi mabambanta, inda wasu ke goyon baya, wasu kuma na adawa, yayin da wasu ke taka-tsantsan.
Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — Turaki Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno EFCC na ƙoƙarin daƙile muradin Malami na yin takarar gwamna — ADCKazalika, mutane da dama na tambayar sahihancin kafa rundunar a bisa doka, manufar shirin da kuma tasirinsa ga tsaro da shugabanci a jihar.
Tushen taƙaddamarHukumar Hisbah ta Jihar Kano, wacce gwamnati ta kafa a jihar, tun da daɗewa ita ce take da alhakin inganta tarbiyyar mutanen jihar bisa tsarin addinin Musulunci, umarni da kyawawan ayyuka da hani da munana, da kuma aiwatar da wasu sassa na dokar Shari’ar Musulunci.
A baya, Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta sallami ’yan Hisbah 12,000, bisa hujjar cewa akwai matsaloli a yadda aka ɗauke su aiki da kuma yadda suke gudanar da ayyukan nasu.
Ganduje, wanda shi ne tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, ya bayyana korar a matsayin rashin adalci. Don haka, ya kafa kwamitin da tsohon Shugaban Hukumar Kula da Ababen Hawa ta jihar (KAROTA) a zamanin mulkin na Ganduje, Baffa Babba Ɗan Agundi ya jagoranta domin tantance sunayen ma’aikatan da abin ya shafa.
Ɗan Agundi yayin gabatar da rahoton, ya ce kwamitin ya yi nasarar tantance ma’aikatan da aka sallama.
“Ranka ya daɗe, ga rahoton ma’aikata 12,000 da gwamnatin Kano ta sallama. Mun tabbatar da su da bayanansu. Dukkansu suna tare da kai a wannan tafiya,” in ji Baffa ga Ganduje.
Dalilin kafa ‘Hisbah mai zaman kanta’Ganduje ya sanar da kafa sabuwar runduna da za ta yi aikin da ya kira na ƙungiya mai zaman kanta, ba wai wata hukumar gwamnati ba.
“Za a kira ta Hisbah mai zaman kanta. Na san akwai wasu da dama da za su so shiga banda waɗannan 12,000. Nan gaba kaɗan za a ba ku wani aikin na ƙaro wasu mutanen da ke ƙoƙarin shiga,” in ji shi.
An tsara rundunar za ta kasance ƙarƙashin jagorancin Sheikh Muhammad Harun Ibn Sina, tsohon Babban Kwamandan
Hukumar Hisbah a zamanin mulkin Ganduje a Kano.
Ibn Sina ya bayyana cewa za a kira rundunar da suna ‘Khairun Nas’, kuma za ta kasance ƙungiyar sa kai mai ayyuka makamantan na Hisbah, amma ba tare da zama hukuma ta gwamnati kamar Hisbar ba.
Ya ce: “Ma’aikata 12,000 da aka ɗauka a lokacin [Ganduje] kuma wannan gwamnatin ta sallama sun koka. Ya ce za a iya kafa ƙungiya mai zaman kanta, amma ba hukuma ba, domin gwamnati ce kaɗai za ta iya kafa hukuma. Don haka aka kafa kwamitin da muka jagoranta tare da Ɗan Agundi da wasu mutum huɗu domin tantance mutanen da kuma shirinsu na shiga.”
Ya ƙara da cewa ba a kai ga kammala ƙungiyar ba tukuna, kuma za ta kasance a buɗe ga duk mai sha’awar shiga. Dangane da alawus ɗin dakarun ƙungiyar, Ibn Sina ya ce ƙungiyar za ta kasance ta sa kai, sai dai idan an sami tallafi daga ɗaiɗaikun mutane ko ƙungiyoyi sannan za a iya ba su ɗan kuɗin alawus.
A cewarsa, manufar ƙungiyar za ta haɗa da “umarni da kywawan ayyuka da hani da mummuna, bayar da taimakon gaggawa, nasiha da taimakon jama’a.”
An fara ɗaukar dakarun a ƙarƙashin Gidauniyar GandujeSai dai ƙasa da mako biyu bayan sanarwar, Gidauniyar Ganduje ta ƙaddamar da ɗaukar ma’aikatan rundunar da aka sanya wa suna ‘Independent Hisbah Fisabilillah’.
A wajen ƙaddamarwa a Kano, Ɗan Agundi da Ibn Sina sun jaddada cewa sabuwar Hisbar ba hukuma ba ce ta gwamnati, illa dai ƙungiyar sa kai ce domin ayyukan addini da jin ƙai.
Ana sa ran ɗaukar ma’aikatan zai ƙunshi tsofaffin ’yan Hisbar da aka sallama tare da buɗe ƙofa ga sabbin masu son shiga daga dukkan ƙananan hukumomin jihar 44.
Matakin ya saɓa doka — Gwamnatin KanoA nata ɓangaren, gwamnatin Kano ta nuna damuwa kan yunƙurin. Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’amuran Cikin Gida na jihar, Ibrahim Waiya, ya zargi Ganduje da yin maganganun tunziri, musamman kan hare haren ’yan bindiga a jihar.
Waiya ya ce ’yan bindiga sun fara kai hare-hare a jihar kasa da sa’o’i 48 bayan maganganun Ganduje, yana mai danganta lamarin da “maganganun tayar da hankali” na tsohon gwamna Ganduje da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin.
Kwamishinan ya kuma buƙaci hukumomin tsaro da su binciki Ganduje tare da kama shi bisa zargin ƙoƙarin nasa na kafa wata rundunar ba bisa ƙa’ida ba.
Amma Ganduje ya yi watsi da zarge zargen a matsayin “marasa tushe” da “rashin kan gado,” yana mai jaddada cewa ba a taɓa danganta shi da tashin hankali ko wani abu da zai iya tayar da zaune tsaye a Kano ba.
Ganduje na da ’yancin kafa rundunar… — LauyaWani lauya a Kano, Barista Kamilu Ahmad, ya ce doka ta ba da dama ga mutum ya kafa rundunar tsaro ta ƙashin kansa, amma dole ne a yi hakan bisa tsarin doka.
Ya Dokar Kafa Kamfanonin Tsaro Masu Zaman Kansu ta 1986, inda ya ce “duk wani ɗan Najeriya na da ’yancin kafa kamfanin tsaro a Nijeriya ta hanyar bin tsarin da doka ta tanada.”
Sai dai ya jaddada cewa bai kamata ayyukan irin wannan rundunar su yi iri ɗaya da ayyukan ’yan sanda ko wata hukumar tsaro ba.
Lauyan ya ce Ganduje na iya yin rajistar kamfanin tsaro a Kano a matsayin ƙungiya mai zaman kanta, amma ya gargaɗe shi da kada ya yi amfani da sunaye ko alamomi da za su yi kama da na gwamnatin da doka ta kafa.
“Ba zai yiwu ya yi amfani da sunan Hisbah ba, kuma manufar kamfaninsa ba za ta yi kama da ta Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ba. Ba za a yi amfani da kayan sawa da suka yi kama da na kowace rundunar tsaro ba, kuma ayyukan rundunar na asali ba su kamata su yi iri ɗaya da na ’yan Hisbah ko sauran jami’an tsaro ba,” in ji lauyan.
Barista Kamilu ya ƙara da cewa Hukumar Kula da yi wa Kamfanoni Rajista (CAC) da dokar NSCDC sun fayyace matakai da sharuɗɗan yin rajista da kamfanonin tsaro masu zaman kansu.
Ya ce CAC ba za ta yi rajista ga kowace ƙungiya mai ɗauke da sunan Hisbah ba, saboda kawai hukuma mai sunan haka a Kano.
Ya kuma kafa hujjar cewa shirin na Ganduje na iya fuskantar manyan ƙalubale, musamman a lokacin da yanzu haka ake ci gaba da muhawara kan kafa ’yan sandan jihohi.
Kanawa sun bayyana mabambantan ra’ayoyiWasu mazauna Kano da suka zanta da Aminiya sun bayyana mabambantan ra’ayoyi kan batun. Yayin da wasu suka yi maraba da shirin a matsayin hanyar samar da ayyukan yi da kuma gyara ɗabi’un mutane, wasu kuma sun nuna tsoron cewa batun zai iya ƙara rarrabuwar kai irin ta siyasa ko kafa wata hukuma mai kama da ta gwamnati.
A cewar Abdulaziz Ibrahim, ba shi da matsala da kafa ƙungiyar muddin ba za ta wuce gona da iri ba. “Sun ce kawai domin umarni da kyakkyawa da hani da mummuna ne, ban ga matsala a hakan ba. Amma idan suka yi wani abu daban, to a nan ne matsalar take,” in ji shi.
A nasa bangaren, Abdullahi Hassan ya ce lokacin da ake ƙoƙarin kafa ƙungiyar da kuma manufarta ne ke sa mutane ɗariɗari da ita.
“Me ya sa sai yanzu da zaɓe ya ƙarato za a kafa ta kuma me ya sa ɗan siyasa ne zai kafa ta? Mutum 12,000 ba ƙaramin adadi ba ne, za su iya ƙirƙirar wata hukuma mai kama da ta gwamnati,” in ji shi.
Amma ga Habiba Musa, tun da batun ya riga ya jawo muhawara da shakku a tsakanin jama’a, ya fi dacewa a dakatar da shi domin maslahar zaman lafiya da haɗin kan jihar.