Aminiya:
2025-03-28@10:07:01 GMT

El-Rufa’i ya fice daga APC ya koma SDP

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i ya tabbatar da sauya sheƙa daga jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar zuwa jam’iyyar SDP.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da a wallafa ranar Litinin ne a shafukansa na sada zumunta.

El-Rufai ya ce, “yanzu na yanke shawarar komawa jam’iyyar Social Democratic Party, kuma zan kasance a cikin ta wajen tafiyar da al’amurana na siyasa a nan gaba.

Kwanakin baya a lokacin tattaunawarsa da kafar talabijin ta Arise, El-Rufa’i ya bayyana cewa “jam’iyyar APC ta sauka daga kan manufofin da aka assasa ta tun fil-azal.”

Ya yi zargin cewa jam’iyyar ta gaza kiran taron shugabanninta na ƙasa tsawon shekaru, wanda ya ce hakan ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

A yanzu dai wannan ya kawo ƙarshen raɗe-raɗin da ake yi na inda tsohon gwamnan zai nufa bayan raba gari da jam’iyyar APC.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Halin Da Matasa Suka Tsinci Kansu A Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yau, da dama daga cikin matasan Najeriya na fama da matsaloli masu tarin yawa, musamman wajen ciyar da kansu da biyan buƙatunsu na yau da kullum.

Wannan na faruwa ne sakamakon halin da tattalin arziƙin ƙasa ke ciki, rashin aikin yi, da kuma tsadar rayuwa.

NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da Lafiyarmu

Wasu daga cikin matasan sun kammala karatu, wasu kuma suna da sana’o’in hannu, amma duk da haka, rashin samun aikin da zai biya musu buƙatunsu yana ƙara jefa su cikin mawuyacin hali.

Wannan matsala na ci gaba da haddasa damuwa ga matasan ƙasar, inda da dama daga cikinsu ke fuskantar ƙuncin rayuwa sakamakon rashin tabbas a makomarsu.

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana, zai nazarci irin waɗannan ƙalubale da matasa ke fuskanta, musamman a matakin farko na rayuwarsu.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m
  • Karin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arzikin Duniya
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Isuhu Yellow a Zamfara
  • Miliyoyin  ‘Yahudawa Sun Gudu Neman Mafaka Saboda Makamin Mai Linzami Daga Yemen
  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Matasa Suka Tsinci Kansu A Najeriya
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]
  • Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina
  • Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]
  • Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar ‘Yan Majalisu