Aminiya:
2025-10-16@06:15:47 GMT

Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC

Published: 10th, March 2025 GMT

Jam’iyyar APC ta yi kira ga Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara da ya sauka daga mulki ko kuma a tsige shi.

Shugaban APC na Jihar Ribas, Tony Okocha ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai yau Litinin a birnin Fatakwal.

An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai

Okocha ya ce gayyatar da Fubara ya aika wa ’yan majalisar dokokin jihar domin ya gana da su akwai lauje cikin naɗi.

“Hukuncin Kotun Ƙoli ne ƙarshe babu wani abu da wani zai iya yi. Abun da ya rage wa gwamnan shi ne ko dai ya sauka, ko kuma a tsige shi,” in ji Okocha.

Tun da farko, bayan hukuncin kotun ƙolin, majalisar jihar ta ba gwamnan jihar wa’adin kwana biyu ya sake gabatar da kasafin kuɗi, gayyatar da ya ƙi amsawa.

Daga baya shi kuma gwamnan ya gayyace su gidan gwamnati domin su tattauna, inda su ma suka ce ba za su je ba, domin a kafofin sadarwa suka ga gayyatar.

Ana iya tuna cewa, majalisar ta kuma bai wa Gwamna Fubara wa’adin sallamar da sau naɗe-naɗen da ya yi wanda ba ita ta tantance su ba.

Za a sake zaɓen ƙananan hukumomin Ribas

A makon jiya ne Hukumar zaɓen Rivers ta saka 9 ga watan Agusta a matsayin ranar sake zaɓen ƙananan hukumomi.

Rahotonni sun ambato shugaban hukumar Adolphus Enebeli na sanar da hakan yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a birnin Fatakwal.

Wannan na zuwa ne bayan Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke zaɓen da hukumar ta gudanar a ranar 5 ga watan Oktoban 2024.

A gefe guda kuma, majalisar dokokin jihar ta gayyaci shugaban hukumar ya bayyana a gabanta domin yin bayani game da zaɓen.

Wannan dambarwar na zuwa ne a yayin da rikicin siyasa tsakanin gwamnan da tsohon gwamna kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ke ƙara kamari.

Tun bayan ɗarewar Fubara kan mulki, dangantakar da ke tsakaninsa da magabacinsa ta yi tsami, lamarin da ya haddasa rabuwar kawuna a Majalisar Dokokin jihar.

Wasu ‘yan majalisa sun tsaya tsayin daka domin kare gwamnan, yayin da wasu ke goyon bayan APC da Wike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Siminalayi Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Cirar kudin kwastoma: Majalisa ta gayyaci CBN da bankuna

Majalisar Wakilai ta gayyaci Babban Bankin Najeriya (CBN) da bankunan kasuwanci domin amsa tambayoyi kan yadda suke cirar cajin kudade barkatai daga asusun masu ajiya.

Majalisar ta gayyace su ne bayan kudurin da Honorabul Tolani Shagaya ya gabatar kan abin da ta kira ‘cirar cajin kudade barkatai babu bayani ba,’ da bankuna suke yi daga asusun masu ajiya, sabanin dokokin CBN.

Honorabul Shagaya ya ce kodayake bankuna da gudanar da hidima ne da ake biya, amma yawancin ’yan Najeriya suna kuka kan yadda suke yawan ciyar kudade — kamar na tura sakon tses, kula da katin ajiya, kula da asusun ajiya, tura kudi, hrajin kan sarki da wasu da ba su san da ake fiye da sau daya.

Ya ce bankuna na ci gaba da cirar irin wadannan kudade daga asusun jama’a duk kuwa da dokar CBN da ke kula da haraji, amma bankunan ba su bi.

Dan Majalisar ya ce, “Wannan mummunar dabi’a tana shafar kasuwanci da masu karamin karfi da dalibai da sauran masu rauni da suke cikin halin kakanika yi.

“Idan ba a gaggaunta yin bincike da kuma magance wannan matsalar za ta ci gaba da kawo rashin yardar jama’a da tsarin banki tare da tafiya ba tare da wasu rukuni na al’ummar kasa ba, gami da zagon kasa ga muradun bankin CBN,” a cawersa.

Bayan sauraron kudurin ne Majisar ta umarci CBN ya wallafa cikakken jerin cajin kudaden da ya amince da su cikin kalamai masu saukin ganewa, kuma ta hukunta bankuna masu kunnen kashi.

Daga nan Majalisar ta bukaci CBN ya samar da kafar tuntuba mai saukin samu domin gabatar da korafin kwastomomi kan irin wadannan caji.

Mambobin Majalisar sun kuma bukaci hukumar kare hakkin kwastomomi (FCCPC) da dangoginsa da wayar da kan al’umma kan hakkokin da suka danganci cajin da bankuna ke cira daga asusun masu ajiya.

Daga nan zauren Majalisar ya umarci Kwamitin Majalisar kan Harkokin Cibiyoyin Hadahadar Kudade su bayyana a gabansa domin amsa tambayoyi kan wadannan korafe-korafe sannan ya mika rahotonsa cikin makonni hudu domin daukar matakin da ya dace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Inuwa ya naɗa sabbin shugabanni a ma’aikatar lafiya ta Gombe
  • Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 
  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP
  • Cirar kudin kwastoma: Majalisa ta gayyaci CBN da bankuna
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako