Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC
Published: 10th, March 2025 GMT
Jam’iyyar APC ta yi kira ga Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara da ya sauka daga mulki ko kuma a tsige shi.
Shugaban APC na Jihar Ribas, Tony Okocha ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai yau Litinin a birnin Fatakwal.
An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-RufaiOkocha ya ce gayyatar da Fubara ya aika wa ’yan majalisar dokokin jihar domin ya gana da su akwai lauje cikin naɗi.
“Hukuncin Kotun Ƙoli ne ƙarshe babu wani abu da wani zai iya yi. Abun da ya rage wa gwamnan shi ne ko dai ya sauka, ko kuma a tsige shi,” in ji Okocha.
Tun da farko, bayan hukuncin kotun ƙolin, majalisar jihar ta ba gwamnan jihar wa’adin kwana biyu ya sake gabatar da kasafin kuɗi, gayyatar da ya ƙi amsawa.
Daga baya shi kuma gwamnan ya gayyace su gidan gwamnati domin su tattauna, inda su ma suka ce ba za su je ba, domin a kafofin sadarwa suka ga gayyatar.
Ana iya tuna cewa, majalisar ta kuma bai wa Gwamna Fubara wa’adin sallamar da sau naɗe-naɗen da ya yi wanda ba ita ta tantance su ba.
Za a sake zaɓen ƙananan hukumomin Ribas
A makon jiya ne Hukumar zaɓen Rivers ta saka 9 ga watan Agusta a matsayin ranar sake zaɓen ƙananan hukumomi.
Rahotonni sun ambato shugaban hukumar Adolphus Enebeli na sanar da hakan yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a birnin Fatakwal.
Wannan na zuwa ne bayan Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke zaɓen da hukumar ta gudanar a ranar 5 ga watan Oktoban 2024.
A gefe guda kuma, majalisar dokokin jihar ta gayyaci shugaban hukumar ya bayyana a gabanta domin yin bayani game da zaɓen.
Wannan dambarwar na zuwa ne a yayin da rikicin siyasa tsakanin gwamnan da tsohon gwamna kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ke ƙara kamari.
Tun bayan ɗarewar Fubara kan mulki, dangantakar da ke tsakaninsa da magabacinsa ta yi tsami, lamarin da ya haddasa rabuwar kawuna a Majalisar Dokokin jihar.
Wasu ‘yan majalisa sun tsaya tsayin daka domin kare gwamnan, yayin da wasu ke goyon bayan APC da Wike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Siminalayi Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba
A wani rahoton da jaridar Jerissalam Post” ta buga ta ambaci cewa; Tun bayan farmakin 7 ga watan Oktoba 2023, ana kara samun matalauta da talauci.
Rahoton ya yi nuni da cewa karuwar talaucin yana da alaka ne da yadda farmakin 7 ga watan Oktoba ya yi tasiri a cikin tattalin arziki “Isra’ila”.
Haka nan kuma rahoton ya ce, da akwai dubban iyalai yahudawa wadanda gabanin yaki, suke rayuwa cikin yanayi mai kyau ta fuskar tattalin arziki, yanzu sun zama matalauta. A dalilin haka cibiyar da ta shirya rahoton ta “ Latit” tana yin gargadi akan cewa; za a iya samun ci gaba da yaduwar talaucin, domin iyalai da dama suna gogoriyon yadda za su iya biyan bukatar yau da kullum, duk da cewa suna da cikakken aiki.
Ita dai kungiyar “Latit” ta ‘yan sahayoniya ce wacce aka kafa a 1996 domin fada da talauci da kuma rashin abinci.
Haka nan kuma rahoton ya bayyana cewa; Adadin iyalan da suke fama da talauci a cikin ‘yan sahayoniyar sun kai 867,000, saboda ba su da lamunin abinci. Adadin daidaikun wadannan iyalan sun kai miliyan 2.8, daga cikinsu da akwai kananan yara miliyan 1.18.
Haka nan kuma wani sashen na rahoton ya ce, talaucin yana karuwa ne da kaso 27-29%.
Da dama daga cikin iyalan ‘yan sahayoniyar suna rayuwa ne ta hanyar samun taimako da tallafi na abinci,domin suna amfani da kudaden da suke samu na aikin yi, domin biyan kudaden wuta da sayen magunguna.
Kaso 40% na tsofaffi suna fama da matsalar tabarbarewar rashin lafiya, da ya faro tun daga farkon yaki.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci