Aminiya:
2025-07-13@06:48:24 GMT

Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC

Published: 10th, March 2025 GMT

Jam’iyyar APC ta yi kira ga Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara da ya sauka daga mulki ko kuma a tsige shi.

Shugaban APC na Jihar Ribas, Tony Okocha ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai yau Litinin a birnin Fatakwal.

An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai

Okocha ya ce gayyatar da Fubara ya aika wa ’yan majalisar dokokin jihar domin ya gana da su akwai lauje cikin naɗi.

“Hukuncin Kotun Ƙoli ne ƙarshe babu wani abu da wani zai iya yi. Abun da ya rage wa gwamnan shi ne ko dai ya sauka, ko kuma a tsige shi,” in ji Okocha.

Tun da farko, bayan hukuncin kotun ƙolin, majalisar jihar ta ba gwamnan jihar wa’adin kwana biyu ya sake gabatar da kasafin kuɗi, gayyatar da ya ƙi amsawa.

Daga baya shi kuma gwamnan ya gayyace su gidan gwamnati domin su tattauna, inda su ma suka ce ba za su je ba, domin a kafofin sadarwa suka ga gayyatar.

Ana iya tuna cewa, majalisar ta kuma bai wa Gwamna Fubara wa’adin sallamar da sau naɗe-naɗen da ya yi wanda ba ita ta tantance su ba.

Za a sake zaɓen ƙananan hukumomin Ribas

A makon jiya ne Hukumar zaɓen Rivers ta saka 9 ga watan Agusta a matsayin ranar sake zaɓen ƙananan hukumomi.

Rahotonni sun ambato shugaban hukumar Adolphus Enebeli na sanar da hakan yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a birnin Fatakwal.

Wannan na zuwa ne bayan Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke zaɓen da hukumar ta gudanar a ranar 5 ga watan Oktoban 2024.

A gefe guda kuma, majalisar dokokin jihar ta gayyaci shugaban hukumar ya bayyana a gabanta domin yin bayani game da zaɓen.

Wannan dambarwar na zuwa ne a yayin da rikicin siyasa tsakanin gwamnan da tsohon gwamna kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ke ƙara kamari.

Tun bayan ɗarewar Fubara kan mulki, dangantakar da ke tsakaninsa da magabacinsa ta yi tsami, lamarin da ya haddasa rabuwar kawuna a Majalisar Dokokin jihar.

Wasu ‘yan majalisa sun tsaya tsayin daka domin kare gwamnan, yayin da wasu ke goyon bayan APC da Wike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Siminalayi Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI

Majalisar limaman musulmin nahiyar turai ta fitar da wani bayani da ta nesanta kanta daga wasu mutane da su ka kai ziyarar HKI tare da bayyana kansu a matsayin limamai daga kasashen turai, tana mai cewa, ko kadan ba su wakiltar al’ummar musulmin da suke cikin nahiyar ta turai.

A ranar Litinin din da ta gabata ne dai ofishin shugaban HKI Ishaq Herzog ya fitar da bayani da a ciki yake cewa; A ofis dinsa dake birnin Kudus ya karbi bakuncin limaman musulmi daga kasashen Faransa,Belgium, Holland, Italia da kuma Birtyaniya.”.

Ofishin majalisar limaman musulmin na turai, mai  matsugunni  a Faransa ya bayyana ziyarar mutanen zuwa Isra’ila da cewa, tana da daure kai, haka nan kuma lokacin da aka yi ta.”

Majalisar ta limaman turai din ta yi kira ga dukkanin ‘yantattu a duniya da su kasance a tare da al’ummar Falasdinu da ake zalunta, domin ganin an kawo karshen kisan kiyashin da sojojin mamaya suke yi musu.

Bugu da kari majalisar ta ce, wannan ziyarar tana nuni da yadda wadanda su ka yi ta ba su da lamiri na ‘yan’adamtaka da rashin riko da mafi karancin koyarwar musulunci ta yin kira da a taimaki gaskiya.”

Majalisar limaman na Turai ta kuma kara da cewa; ziyarar wani kokari ne na wanke ‘yan mamaya, kuma cin amanar Allah da manzon Allah ne da jinanen raunana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sanya dokar hana fita a Adamawa
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Matsayin Jihar A Zaman Nazarin Kundin Tsarin Mulki
  • Lakurawa sun kashe ’yan sanda 3 a Kebbi
  • Magance Matsalar Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta: Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyarwa A Makarantun Jihar
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
  • Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara
  • Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar
  • Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI
  • Kotun ƙoli ta tabbatar da Okpebholo a matsayin gwamnan Edo
  • Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo a Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo