Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC
Published: 10th, March 2025 GMT
Jam’iyyar APC ta yi kira ga Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara da ya sauka daga mulki ko kuma a tsige shi.
Shugaban APC na Jihar Ribas, Tony Okocha ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai yau Litinin a birnin Fatakwal.
An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-RufaiOkocha ya ce gayyatar da Fubara ya aika wa ’yan majalisar dokokin jihar domin ya gana da su akwai lauje cikin naɗi.
“Hukuncin Kotun Ƙoli ne ƙarshe babu wani abu da wani zai iya yi. Abun da ya rage wa gwamnan shi ne ko dai ya sauka, ko kuma a tsige shi,” in ji Okocha.
Tun da farko, bayan hukuncin kotun ƙolin, majalisar jihar ta ba gwamnan jihar wa’adin kwana biyu ya sake gabatar da kasafin kuɗi, gayyatar da ya ƙi amsawa.
Daga baya shi kuma gwamnan ya gayyace su gidan gwamnati domin su tattauna, inda su ma suka ce ba za su je ba, domin a kafofin sadarwa suka ga gayyatar.
Ana iya tuna cewa, majalisar ta kuma bai wa Gwamna Fubara wa’adin sallamar da sau naɗe-naɗen da ya yi wanda ba ita ta tantance su ba.
Za a sake zaɓen ƙananan hukumomin Ribas
A makon jiya ne Hukumar zaɓen Rivers ta saka 9 ga watan Agusta a matsayin ranar sake zaɓen ƙananan hukumomi.
Rahotonni sun ambato shugaban hukumar Adolphus Enebeli na sanar da hakan yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a birnin Fatakwal.
Wannan na zuwa ne bayan Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke zaɓen da hukumar ta gudanar a ranar 5 ga watan Oktoban 2024.
A gefe guda kuma, majalisar dokokin jihar ta gayyaci shugaban hukumar ya bayyana a gabanta domin yin bayani game da zaɓen.
Wannan dambarwar na zuwa ne a yayin da rikicin siyasa tsakanin gwamnan da tsohon gwamna kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ke ƙara kamari.
Tun bayan ɗarewar Fubara kan mulki, dangantakar da ke tsakaninsa da magabacinsa ta yi tsami, lamarin da ya haddasa rabuwar kawuna a Majalisar Dokokin jihar.
Wasu ‘yan majalisa sun tsaya tsayin daka domin kare gwamnan, yayin da wasu ke goyon bayan APC da Wike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Siminalayi Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
EFCC na ƙoƙarin daƙile muradin Malami na yin takarar gwamna — ADC
Jam’iyyar ADC ta zargi Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC) da amfani da siyasa wajen belin tsohon Ministan Shari’a na Tarayya, Abubakar Malami (SAN).
Jam’iyyar ta ce babu wata shaida da ke nuna cewa Malami ya karya sharuɗan belin da aka ba shi.
Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCONA cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran jam’iyyar na ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, ADC ta ce an ɗauki matakin ne jim kaɗan bayan Malami ya halarci wani taron siyasa a Jihar Kebbi.
Jam’iyyar ta ce matakin da aka ɗauka ya nuna yadda aka ƙulla wani abu domin daƙile burinsa na takarar gwamna, ba wai domin neman adalci ba.
“Jam’iyyar ADC na kallon soke belin Malam Abubakar Malami da EFCC ta yi a matsayin amfani da siyasa,” in ji Abdullahi.
“Daga dukkanin bayanan da muka samu, Malami bai karya ko ɗaya daga cikin sharuɗan belin da aka ba shi ba, kuma hana belin ya sanya alamar tambaya a kan manufar EFCC.”
ADC ta ce tana goyon bayan yaƙi da cin hanci da rashawa tare da mara wa EFCC baya wajen gudanar da aikinta.
Sai dai jam’iyyar ta yi gargaɗin cewa ɗaukar matakai na ɓangare ɗaya kan ‘yan adawa na iya rage amincewar jama’a da kuma raunana sahihancin yaƙi da cin hanci a ƙasar.
Jam’iyyar ta kuma ce babu wata hukuma ta gwamnati da ke da ikon hana ɗan ƙasa shiga harkokin siyasa ba tare da umarnin kotu ba.
Ta ƙara da cewa tana tare da Malami, tare da yin kira da a sake nan take ba tare da sharuɗan da za su taƙaita masa haƙƙinsa na siyasa ba.