HausaTv:
2025-03-19@16:58:03 GMT

Isra’ila ta aike da tawaga zuwa Doha domin ci gaba da tattaunawar sulhun Gaza

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnatin Isra’ila ta tura wa tawaga zuwa kasar Qatar a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin Isra’ilar da masu shiga tsakani ciki har da Amurka.

Wannan ya biyo bayan tattaunawar kai tsaye da ba a taba yin irinta ba tsakanin Hamas da wakilin Amurka Adam Boehler dake kula da mutanen da akayi garkuwa da su.

Wakilin na Amurka ya sha bayyanawa a baya baya nan cewa Ya yi imanin cewa za a iya cimma yarjejeniya a makonni masu zuwa.

Ya kuma ce Hamas ta shirya tsagaita bude wuta na tsawon shekaru biyar zuwa goma sannan kuma kungiyar ta kwance damara.

Tunda farko dai kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem ya shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa, “suna kira ga masu shiga tsakani a Masar da Qatar, da kuma gwamnatin Amurka, da su tabbatar da cewa ‘yan mamaya sun mutunta yarjejeniyar, da ba da damar shigar da kayayyakin jin kai, da kuma ci gaba da tafiya mataki na biyu na tsagaita.

A nata bangaren dai Isra’ila na son tsawaita wa’adin zangon farko na tsagaita bude wuta har zuwa tsakiyar watan Afrilu, kuma ta bukaci ficewar Hamas daga yankin Falasdinu da ta ke mulki tun shekara ta 2007, da kuma dawo da ragowar mutanen da taka garkuwa da su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Masu Zuba Jari Na Waje Suna Da Kyakkyawan Fata Game Da Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Jaridar Financial Times ta Burtaniya ta bayyana cewa, masu zuba jari na kasashen waje suna kara “gano kasar Sin”, kuma sun yi imanin cewa, kasar Sin za ta iya samar da “kirkire-kirkire da damammaki” masu yawa a wasu fannoni. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Fatan Dukkan Bangarori Za Su Guji Daukar Mataki Da Zai Ta’azzara Rikici A Gaza
  • Masu Zuba Jari Na Waje Suna Da Kyakkyawan Fata Game Da Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin
  • Hamas ta ɗora alhakin harin da Isra’ila ta kai a kan Amurka
  • Mutum 330 Sun Mutu Yayin da Isra’ila Ta Kai Wa Gaza Sabbin Hare-hare 
  • Sayyid Husi: Idan Amurka Ta Ci Gaba Da Kai Mana Hare-hare To Muna Da Hanyoyin Gasa Mata Aya A Hannu
  • Munanan Hare-hare  Sojojin HKI A Gaza Da Safiyar Yau Talata Sun Yi Sanadiyyar Shahadar Fiye Da Falasdinawa 200
  • Isra’ila ta ƙaddamar da sabon hari a Zirin Gaza
  • Trump zai tuntuɓi Putin kan yaƙin Ukraine
  • Angola Ta Bukaci Tsagaita Wuta Kafin Taron Zaman Lafiya Tsakanin Kongo Demokradiyy Da Kungiyar M-23
  • Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen