HausaTv:
2025-10-19@23:59:31 GMT

Isra’ila ta aike da tawaga zuwa Doha domin ci gaba da tattaunawar sulhun Gaza

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnatin Isra’ila ta tura wa tawaga zuwa kasar Qatar a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin Isra’ilar da masu shiga tsakani ciki har da Amurka.

Wannan ya biyo bayan tattaunawar kai tsaye da ba a taba yin irinta ba tsakanin Hamas da wakilin Amurka Adam Boehler dake kula da mutanen da akayi garkuwa da su.

Wakilin na Amurka ya sha bayyanawa a baya baya nan cewa Ya yi imanin cewa za a iya cimma yarjejeniya a makonni masu zuwa.

Ya kuma ce Hamas ta shirya tsagaita bude wuta na tsawon shekaru biyar zuwa goma sannan kuma kungiyar ta kwance damara.

Tunda farko dai kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem ya shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa, “suna kira ga masu shiga tsakani a Masar da Qatar, da kuma gwamnatin Amurka, da su tabbatar da cewa ‘yan mamaya sun mutunta yarjejeniyar, da ba da damar shigar da kayayyakin jin kai, da kuma ci gaba da tafiya mataki na biyu na tsagaita.

A nata bangaren dai Isra’ila na son tsawaita wa’adin zangon farko na tsagaita bude wuta har zuwa tsakiyar watan Afrilu, kuma ta bukaci ficewar Hamas daga yankin Falasdinu da ta ke mulki tun shekara ta 2007, da kuma dawo da ragowar mutanen da taka garkuwa da su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Shugaban ya kara da cewa, aana sa ran aikin za a fara gudanar da shi ne, a zangon farko na shekarar 2026.

 

Ya ci gaba da cewa, aikin na yiwa wadannan Tashoshin garanbawul, na daga cikin kudurorin Gwamnatin Tarayya na zamantar da Tashoshin Jiragen Ruwa na kasa, musamman ta hanyar samar da kayan aiki na zamia da kuma ci gaba da janyo hankalin masu son zuba hannun jari zuwa ga fannin, wanda hakan zai kuma kara sanya gasa a cikin wadanda suke a cikin fannin.

 

Ya bayyana cewa, masu son zuba hannun jari a fannin suna ci gaba da nuna shawarsau, musamman saboda sauye-sauyen da Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinbu ta kirkiro da su, a fannin kara habaka tattalin arzkin kasar.

 

Kazalika, Shugaban ya kuma jinjinawa Ministan Bunkasa Tattalin Arzikin Kasa na kan Teku Adegboyega Oyetola, musamman kan goyon bayan da yake ci gaba da bayarwa ga fannin.

 

Ya yi nuni da aiki irin wannan mai mahimmancin gaske, abu da ke bukatar isassehen lokaci domin a samu damar gudanar da ciakken shiri, duba da cewa, aiki ne, da ya kunshi bangaren injiniyoyi gudanar da bincike da sauransu.

 

Hakazalika, Dantsoho, wanda kuma shi ne, Masu Kula da Harkar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Afrika ta Yamma wato  IAPH, ya jaddda cewa, tattalin arzikin kasar nan zai kara samun dimbin masu son zuba hannun jari a fannin, musamman biyo bayan sauye-sauyen da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya kirkiro da su.

 

A cewarsa, Hukumar ta NPA ta yi hadaka da sauran masu ruwa da tsaki a fanin, wanda ya sanar da cewa, hadar za ta taimaka wajen janyo ra’ayin masu son zuba hannun jari a fannin.

 

Ya yi nuni da cewa, a bayanan da wasu daga cikin masu ruwa da tsaki suka bayyana a wajen taron shi ne, yadda a shekarun baya, fannin ya fuskanci rashin nuna yarda da kuma iya gudanar da shugabanci na gari, inda ya  kara da cewa, a yanzu mu muna bukatar ganin cewa, an yi hadaka domin a kara ciyar da fanning aba.

 

“Zamu yi wannan hadakar ne, ta hanyar nuna amincewa domin a cimma burin da aka sanya a gaba, na yin hadakar, “ Inji Dantsoho.

 

Shugaban ya kuma sanar da cewa, wani Kamfani da ke a kasar Singapore ya bai wa Hukumar NPA kwangila wadda za a gudanar da ita, a karkashin shirin NSW na kasar nan.

 

“Kamfanin da kayan aiki da kudade da za aiwatar da kwangilar, A cewar Shugaban.”

 

Shugaban ya kara da cewa, aikin bunkasa ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa, aiki ne da ke bukatar a kashe kudade masu yawa, wanda kuma masu zuba hannaun jari daga kasar waje ne kawai za su iya yin hakan.

 

Dantsoho ya ci gaba da cewa, duba da yadda a yau ake yin amfani da kayan aiki  na zamani dajen tafiyar da ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa a fadin duniya, dole ita ma Nijeriyata shiga cikin wannna sahun a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwa da a kasar.

 

“A yau duniya ta sauya wajen daina yin amfani da tsohon tsari wanda mutane suke gudanar da abu daya kadai,” A cewar Shugaban.

 

A cewar Shugaban Nijeriya ba ta wadatatun kudaden da za iya aiwatar da wadannan manyan ayyukan, amma muna kan ci gaba da kokarim janyo ra’ayin masu son zuba hannun jari a fannin.

 

“Akwai matukar bukatar mu yi hadaka da sauran jama’a, domin kamar yadda na bayyana a shekarar 2006, cewa ya zama wajibi Hukumar ta NPA ta daina doharo kan bangaren ggwamnati, amma ta mayar da hanjali a bangaren kamfanonin masu zaman kansu.

 

“A yanzu muna son mayar da hankali wajen zuba hannun jari ta hanyar yin amfani da fasahar zamani, kuma wannan abu ne, da ke bukatar kudade masu yawa, muna kuma kara kokari domin kulla wannan hadakar, Inji Dantsoho.

 

“A yayin da muka hallara a nan, za mu kuma kara hallara wasu taruka na da ban kuma suna yi mana kallon cewa, tabbas mu abokan yin hadaka ne,” Acewar Shugaban.

 

“Muna a cikin kungiyar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na PMAWCA, muna kuma a cikin kungiyar IAPH da kuma ta masu kula da masu tafiya cinari ta kasa da kasa wato IMO za mu kuma ci gaba da tattaunawa wadda muke da yakin za a samu sakamako mai kyau,”  Inji Dantsoho.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho October 17, 2025 Tattalin Arziki Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida October 11, 2025 Tattalin Arziki Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
  • Hamas ta yi Allah wadai da Isra’ila kan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta
  • Doha: Pakistan da Afghanistan sun amince da tsagaita bude wuta a tsakaninsu
  • Masani Kan Harkokin Tsaro Ya Ce: Makami Mai Linzamin Iran Kirar Ghadir Ya Aike Da Sako Ga Isra’ila
  • Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce: An Rusa Gaza Gaba Daya
  • Hamas Ta Bukaci A Kafa Kotun Kasa Da Kasa Kan Gawarwarkin Da Isra’ila Ta Dawo Mata Da Su.
  • Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF
  • Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
  • Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Kira Da Matsa Wa Isra’ila Lamba Da Ta Cika Sharuddan Yarjejeniyar Gaza