Masu rajin kare hakkin bil’adama a birnin Sao Paulo na kasar Brazil, sun ratsa tsakiyar birnin tare da makeken tutar kasar Falasdinu inda suke kira zuwa ga cikekken yenci ga Falasdinawa da kuma dakatar da kissan kiyashin da HKI take aikatawa a can.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, a dai dai lokacinda ake kira zuwa ga goyin bayan mutanen gaza wadanda HKI takewa kissan kiyashi a fagen kasa da kasa, mutanen Brazil sun fito kwansu da kwarkwartansu a birnin Sao Paulo don tabbatar da wannan kiran.

A halin yanzu dai ana kokarin samarda kawance ta kasa da kasa, wacce zata game ko ina a duniya, don goyon bayan mutanen Falasdinu da kuma korar yahudawa yan mulkin mallaka kuma yan mamaya, daga kasar Falasdinu da aka mamaye.

Labarin ya kara da cewa, wadanda suka yi jawabi a gaggamin taron na Sao Paulo sun bukaci a kawo karshen kissan kiyashi a Gaza, a kuma kafa kasar Falasdinu mai cikekken yenci daga teku zuwa kogi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Daga cikin ƙorafe-ƙorafen da masu ƙara suka zayyana sun haɗa cewa, ya danganta halittar Annabi SAW da ƙasƙantun halittu (‘Ya’yan Tumkiya, da Karya, da Ƙwarƙwata), sannan kuma ya taɓa alfarmar iyayen Annabi SAW wanda a cewarsu, hakan bai dace ba a alfarmarsa fiyayyen halitta.

 

Gwamnatin Kano, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ba tare da ɓata lokaci ba, ta miƙa koken ga Majalisar Shura ta jihar domin fayyace gaskiyar lamari.

 

Majalisar Shura, ta bakin Sakatarenta, Shehu Wada Sagagi, a wani taron manema labarai da ta gudanar, ta tabbatar da cewa, za ta gudanar da cikakken bincike akan zargin da aka yi wa Malamin (Abubakar Triumph). Sannan kuma, za ta gayyaci masu ƙorafe-ƙorafe da kuma Malamin domin sauraron bayanansu. Ya ce matakin zai bai wa kowanne ɓangare dama kuma za a bi ƙa’idojin shari’ar Musulunci wajen gudanar da binciken.

 

Sagagi ya roƙi jama’a da su zauna cikin kwanciyar hankali, tare da jaddada muhimmancin kiyaye zaman lafiya da Kano ta yi fintinƙau akai. Ya tabbatar da cewa, majalisar za ta yi bincike da tattaunawa kafin ta bai wa gwamnati shawara kan matakin da ya dace bisa ga ƙa’idar shari’a.

 

Daga bisani kuma, rahotanni sun bayyana cewa, Majalisar ta dakatar da Malam Abubakar Triumph daga yin wa’azi a jihar har sai ta kammala bincike.

 

Ta kuma yi gargaɗi ga ‘yan siyasa da su guji tsoma baki a lamarin, inda ya jaddada buƙatar barin Majalisar ta kammala aikinta cikin gaskiya da adalci.

 

Ranar da aka daɗe ana tsumayi, ranar zaman tattaunawa da Malam Triumph da masu sukar kalamansa, ta tabbata inda aka yi zama a ofishin Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da ke Kano a ranar Litinin, 13 ga watan Oktoban 2025.

 

An gudanar da taron ne ƙofa rufe, inda mambobin Majalisar suka shawarci malamin da ya riƙa yin taka-tsantsan da natsuwa a cikin bayanansa na addini. Rahotanni sun nuna cewa, malamin ya nemi afuwa a yayin tattaunawar.

 

Bayan kammala zaman, Malam Triumph ya wallafa kalmar “Alhamdulillah” a shafinsa na Facebook abin da jama’a da dama suka fassara a matsayin alamar cewa an kammala zaman lafiya tsakaninsa da Majalisar Shura, amma dai, al’umma musamman masu ƙorafi suna nan suna jiran sakamakon zaman tattaunawar daga bakin gwamnatin Kano.

 

Ko ina aka kwana? Majalisar Shura ba ta miƙa sakamakon zaman ba ne ga gwamnatin Kano ko kuma gwamnatin ce ta yi biris?

 

Don jin wannan amsar ne, masu ƙorafi a ƙarƙashin ɗariƙun sufaye suka maka gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da kwamishinan ‘yansanda na jihar a kotu kan zargin cewa, sun ƙi gudanar da haƙƙin da ya rataya a kansu kan cafke wanda ake zargi da yin ɓatanci ga Annabi Muhammad SAW.

 

An ga matakin kotun ne a wata takarda da aka yada a kafafen sada zumunta, mai taken “Dambarwar Shari’a a cikin batun Malam Abubakar Lawal (Lawan Triumph) a Babbar Kotun Shari’a ta Jihar Kano.”

 

A cewar takardar, waɗanda ake ƙara da suka haɗa da Gwamna Yusuf, Kwamishinan ‘Yansanda, da Babban Lauyan gwamnati, an zarge su da gazawa wajen aiwatar da ayyukansu na doka na gurfanar da masu aikata manyan laifuka a ƙarƙashin Dokar Shari’a ta Jihar Kano ta 2000 da Dokar Laifukan Intanet ta 2024 (wadda aka yi wa kwaskwarima).

 

Ƙungiyoyin da suka yi haɗin gwiwar shigar da ƙarar sun haɗa da Interfaith Partners for Peace and Development, Fityanul Islam of Nigeria, Sairul Qalbi Foundation, Tijjaniyya Youth Enlightenment Initiative, Hablullahi Mateen Foundation, Dariqa Qadiriyya of Nigeria, Kadiriyya Youth Awareness, Kadiriyya Riyadul Janna Kofar Na’isa, Ashabul Kahfi Foundation, da Majmau Ashabul Yameen.

 

Har zuwa lokacin rubuta wannan nazari, gwamnatin Jihar Kano ko rundunar ‘yansanda ba su bayar da wani martani a hukumance kan ƙarar ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya November 8, 2025 Manyan Labarai Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi November 8, 2025 Manyan Labarai Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10 November 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
  • Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?
  • Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako
  • An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
  • Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin
  • Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo
  • Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC
  • Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15
  • Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura