Tutocin Falasdinu Sun Yi Ta Kadawa A Birnin Sao Paulo Na kasar Brazil, A Gagarumin Gaggami Da Masu Goyon Bayan Falasdinawa Suka Shirya
Published: 10th, March 2025 GMT
Masu rajin kare hakkin bil’adama a birnin Sao Paulo na kasar Brazil, sun ratsa tsakiyar birnin tare da makeken tutar kasar Falasdinu inda suke kira zuwa ga cikekken yenci ga Falasdinawa da kuma dakatar da kissan kiyashin da HKI take aikatawa a can.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, a dai dai lokacinda ake kira zuwa ga goyin bayan mutanen gaza wadanda HKI takewa kissan kiyashi a fagen kasa da kasa, mutanen Brazil sun fito kwansu da kwarkwartansu a birnin Sao Paulo don tabbatar da wannan kiran.
A halin yanzu dai ana kokarin samarda kawance ta kasa da kasa, wacce zata game ko ina a duniya, don goyon bayan mutanen Falasdinu da kuma korar yahudawa yan mulkin mallaka kuma yan mamaya, daga kasar Falasdinu da aka mamaye.
Labarin ya kara da cewa, wadanda suka yi jawabi a gaggamin taron na Sao Paulo sun bukaci a kawo karshen kissan kiyashi a Gaza, a kuma kafa kasar Falasdinu mai cikekken yenci daga teku zuwa kogi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Shugabannin jam’iyyar APC a matakin gunduma na Gayam, cikin ƙaramar hukumar Lafia, sun dakatar da shugaban jam’iyyar a matakin jiha, Hon. Aliyu Bello. Sun zarge shi da aikata abubuwan da suka saɓa da kundin tsarin mulki na jam’iyyar, musamman sashe na 21 (D)(i–iii), wanda ya haɗa da cin amanar jam’iyya da goyon bayan ɗan takarar wata jam’iyya daban.
Shugaban gundumar, Ibrahim Ilyasu, ya bayyana cewa matakin dakatarwar ya fara aiki nan take, kuma Hon. Bello ba zai iya wakiltar kansa ko amfani da matsayin sa a matsayinsa na mamba na APC daga Gayam ba, har sai an warware batutuwan da aka gabatar. Sun kuma zarge shi da jawo wa jam’iyyar tozarci da keta mutuncinta a idon jama’a.
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A KanoSai dai wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar a jihar sun ce wannan matakin wani yunkuri ne daga wani ɓangare na ƙungiyar siyasa da ke ƙoƙarin kifar da Bello daga kujerarsa, musamman bisa alaƙa da wani ɗan takarar gwamna a jihar. Sun ce wannan rikici ya ƙara bayyana rabuwar kai da rikicin cikin gida a jam’iyyar.
A wata ganawa da wasu shugabannin jam’iyyar a Lafia, an kaɗa ƙuri’ar nuna goyon baya da amincewa da shugabancin Hon. Bello, wanda hakan ke nuna cewa har yanzu akwai sassa a jam’iyyar da ke goyon bayansa, duk da dakatarwar da aka sanar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp