Masu rajin kare hakkin bil’adama a birnin Sao Paulo na kasar Brazil, sun ratsa tsakiyar birnin tare da makeken tutar kasar Falasdinu inda suke kira zuwa ga cikekken yenci ga Falasdinawa da kuma dakatar da kissan kiyashin da HKI take aikatawa a can.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, a dai dai lokacinda ake kira zuwa ga goyin bayan mutanen gaza wadanda HKI takewa kissan kiyashi a fagen kasa da kasa, mutanen Brazil sun fito kwansu da kwarkwartansu a birnin Sao Paulo don tabbatar da wannan kiran.

A halin yanzu dai ana kokarin samarda kawance ta kasa da kasa, wacce zata game ko ina a duniya, don goyon bayan mutanen Falasdinu da kuma korar yahudawa yan mulkin mallaka kuma yan mamaya, daga kasar Falasdinu da aka mamaye.

Labarin ya kara da cewa, wadanda suka yi jawabi a gaggamin taron na Sao Paulo sun bukaci a kawo karshen kissan kiyashi a Gaza, a kuma kafa kasar Falasdinu mai cikekken yenci daga teku zuwa kogi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rukunin Karshe Na Alhazan Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

Rukunin ƙarshe na mahajjatan Jigawa 368 ya tashi daga Filin Jirgin Sama na Nuhu Muhammadu Sunusi zuwa Saudiyya don aikin hajjin shekarar 2025.

A wata hira da aka yi da shi a Radio Nigeria kafin tashinsu a daren Laraba, Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya bayyana cewa rukunin ƙarshe na mahajjatan 368 sun fito ne daga ƙananan hukumomin Birnin Kudu, Buji, da Taura na jihar.

A cewarsa, wannan rukunin ƙarshe ya haɗa da Amirul Hajj na jihar, malamai  masu wa’azi, wasu jami’an shiyyoyi da cibiyoyi, da kuma wasu jami’an hukumar.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana cewa, jihar ta kammala aikin tantance mahajjata cikin nasara ba tare da wata tangarda ba.

Ya yabawa Gwamnan jihar, Malam Umar Namadi, bisa goyon baya da haɗin kai da ya bayar ga hukumar.

Darakta Janar ɗin ya kuma yi kira ga sauran mahajjatan Najeriya da ba a ɗauka ba su ƙara haƙuri tare da ci gaba da karanta littattafan da aka basu lokacin bita da shirye-shiryen hajji a jiharsu.

A jawabin bankwana da ya gabatar a filin jirgin sama, Gwamna Umar Namadi ya shawarci mahajjatan da su yi addu’a don jiharsu da ƙasar baki ɗaya.

Namadi ya kuma ja hankalinsu da su bi dokokin da ƙasar Saudiyya ta shimfiɗa.

Wasu daga cikin mahajjatan da suka yi magana da Radio Nigeria kafin tafiyarsu sun gode wa Allah da ya basu damar zuwa kasa mai tsarki domin gudanar da aikin hajjin bana.

Sun yabawa shugabannin hukumar kula da jin daɗin mahajjata ta jihar Jigawa bisa tanadin abinci da abin sha da suka yi musu yayin da suke sansanin Alhazai da filin jirgi.

Mahajjatan sun bayyana jin daɗinsu da yadda aka tsara wa’azi tare da yabawa jami’an hukumar da yadda suka kula da su a sansanin Alhazai.

Radio Nigeria ya ruwaito cewa, jami’an hukumar shige da fice, kwastam, da NDLEA ne suka tantance mahajjatan tare da jakunkunansu masu nauyin kilo 8.

 

Usman Muhammad Zaria.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • An yi Jana’izar Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa a Zariya
  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
  • Wani Mutum Ya Harbe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Isra’ila A Birnin Washington Na Amurka
  • Rukunin Karshe Na Alhazan Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
  • Hukumar tace fina-finai ta soke lasisin gidajen gala 8 a Kano
  • Wasu Yan Siyasa A Burtaniya Suna Matsaya Gwamnatin Kasar Ta Amince Da Kasar Falasdinu
  • Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan
  • Sojojin Sudan Sun Gama Tsarkaka Birnin Khartoum Daga ‘Yan Tawayen Rapid Support Forces
  • DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”