Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Masanin Aikin Jarida, Kabir Ɗangogo
Published: 10th, March 2025 GMT
An haife shi a ranar 21 ga Fabrairu, 1949, kuma ya yi karatu a Jami’ar Ohio da ke Athens a Amurka, a 1981, da Jami’ar Leicester ta ƙasar Birtaniya a 1987.
Ya yi aiki a kamfanin jaridun New Nigerian, da hukumar talbijin ta NTA, da Ofishin Yaɗa Labarai na Amurka (USIS). Haka kuma ya yi koyarwa a Kaduna Polytechnic, ya yi aiki a Bankin Arewa da kuma Bankin Union inda a nan ya yi ritaya a ranar 26 ga Yuni, 2005.
A cikin saƙon ta’aziyyar sa a ranar Asabar, Minista Idris ya bayyana rasuwar Malam Kabir Ɗangogo a matsayin babban rashi ga Nijeriya da fannin sadarwa a nahiyar Afirka.
Ya ce: “Mutuwa ta ƙwace mana ƙwararren ma’aikaci wanda ke da cikakkiyar sadaukarwa ga aiki, da ƙwarewa a aikin jarida, da kuma gagarumar gudunmawar da ya bayar a fannin hulɗa da jama’a.
“Ta hanyar aikin sa, ya ɗaga martabar hulɗa da jama’a a Afirka, inda ya jagoranci ci gaba da tabbatar da ɗa’a, horar da ƙwararru, da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashe.”
Ministan ya yaba wa Ɗangogo a matsayin jagora, mai hangen nesa, kuma uba ga masu aikin hulɗa da jama’a (wato public relations), wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta fannin a Nijeriya da Afrika baki ɗaya.
Ya ƙara da cewa a lokacin da Ɗangogo ke riƙe da muƙamin Sakatare-Janar na APRA, ya jajirce wajen ƙarfafa tattaunawa, da fito da sababbin abubuwa, da kuma ci gaba da tabbatar da ɗa’a a ɓangaren sadarwa da kula da suna.
Ya ce: “A madadin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ina miƙa ta’aziyya ta ga iyalan sa, abokan aikin sa, da ɗaukacin ‘yan jarida da masu hulɗa da jama’a.
“Ina roƙon Allah ya gafarta masa, ya jiƙan sa, ya kuma ba iyalan sa haƙurin jure wannan babban rashi.”
Ministan ya kammala da cewa gagarumar gudunmawar da Ɗangogo ya bayar za ta ci gaba da zaburar da sababbin ‘yan jarida da masu aikin hulɗa da jama’a nan gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: hulɗa da jama a
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
Daga Aliyu Muraki
Hukumar Ilimi Matakin Farko ta Jihar Nasarawa (NSUBEB) ta yi barazanar kamawa tare da gurfanar da iyayen da ‘ya’yansu ba sa zuwa makaranta a jihar.
Shugaban Hukumar, Dr. Kasim Mohammed Kasim ne ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai a matsayin wani bangare na ayyukan babban taron inganta ilimi da hukumar ta shirya.
Dr. Kasim Mohammed Kasim ya ce, ilimin boko matakin farko haƙƙin kowanne yaro ne, ba gata ba, kuma ya sha alwashin tabbatar da cewa ba a bar wani yaro a baya ba.
Shugaban Hukumar ya bayyana cewa hukumar ta yanke shawarar gudanar da gagarumin wayar da kan jama’a ta hanyar tarurrukan jin ra’ayoyin jama’a, da kafofin watsa labarai domin jaddada muhimmancin ilimin boko na a matakin farko ga kowane yaro a jihar.
Dr. Kasim Mohammed Kasim ya ce sun sayi motocin bas guda bakwai da za a gudanar da wayar da kan jama’a a dukkan sassan kananan hukumomi 13 na jihar, domin fadakar da iyaye muhimmancin kai ‘ya’yansu makaranta.
Game da babban taron, Dr. Kasim Mohammed Kasim ya ce wannan taro zai hada manyan masu ruwa da tsaki ciki har da masana ilimi, jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya, masu tsara manufofi, iyaye, malamai da sauransu.
Ya ce, mahalarta taron za su tattauna hanyoyin magance matsalolin ilimi, musayar kwarewa da sabbin dabaru domin kara inganta koyarwa da koyo a jihar.
Ya lissafo wasu daga cikin matsalolin da suka hada da ginin makarantu marasa inganci, karancin kujeru, karancin malamai, yawan rashin zuwa aiki daga ma’aikata, da rashin daidaitaccen tsarin tura malamai, da sauransu.
Ya ce hukumar ta maida malamai 1,900 wadanda a da ke aiki a ofis-ofis zuwa azuzuwa domin koyarwa, kuma nan ba da jimawa ba za a dauki sabbin malamai 1,000 domin cike gibi a makarantun jihar.