Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Masanin Aikin Jarida, Kabir Ɗangogo
Published: 10th, March 2025 GMT
An haife shi a ranar 21 ga Fabrairu, 1949, kuma ya yi karatu a Jami’ar Ohio da ke Athens a Amurka, a 1981, da Jami’ar Leicester ta ƙasar Birtaniya a 1987.
Ya yi aiki a kamfanin jaridun New Nigerian, da hukumar talbijin ta NTA, da Ofishin Yaɗa Labarai na Amurka (USIS). Haka kuma ya yi koyarwa a Kaduna Polytechnic, ya yi aiki a Bankin Arewa da kuma Bankin Union inda a nan ya yi ritaya a ranar 26 ga Yuni, 2005.
A cikin saƙon ta’aziyyar sa a ranar Asabar, Minista Idris ya bayyana rasuwar Malam Kabir Ɗangogo a matsayin babban rashi ga Nijeriya da fannin sadarwa a nahiyar Afirka.
Ya ce: “Mutuwa ta ƙwace mana ƙwararren ma’aikaci wanda ke da cikakkiyar sadaukarwa ga aiki, da ƙwarewa a aikin jarida, da kuma gagarumar gudunmawar da ya bayar a fannin hulɗa da jama’a.
“Ta hanyar aikin sa, ya ɗaga martabar hulɗa da jama’a a Afirka, inda ya jagoranci ci gaba da tabbatar da ɗa’a, horar da ƙwararru, da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashe.”
Ministan ya yaba wa Ɗangogo a matsayin jagora, mai hangen nesa, kuma uba ga masu aikin hulɗa da jama’a (wato public relations), wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta fannin a Nijeriya da Afrika baki ɗaya.
Ya ƙara da cewa a lokacin da Ɗangogo ke riƙe da muƙamin Sakatare-Janar na APRA, ya jajirce wajen ƙarfafa tattaunawa, da fito da sababbin abubuwa, da kuma ci gaba da tabbatar da ɗa’a a ɓangaren sadarwa da kula da suna.
Ya ce: “A madadin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ina miƙa ta’aziyya ta ga iyalan sa, abokan aikin sa, da ɗaukacin ‘yan jarida da masu hulɗa da jama’a.
“Ina roƙon Allah ya gafarta masa, ya jiƙan sa, ya kuma ba iyalan sa haƙurin jure wannan babban rashi.”
Ministan ya kammala da cewa gagarumar gudunmawar da Ɗangogo ya bayar za ta ci gaba da zaburar da sababbin ‘yan jarida da masu aikin hulɗa da jama’a nan gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: hulɗa da jama a
এছাড়াও পড়ুন:
Za a sa zare tsakanin Amurka da Turai kan harajin kasuwanci
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da lafta wa Tarayyar Turai da kuma Mexico harajin kashi 30 kan kayayyakin da ake shiga da su da su ƙasar daga ranar 1 ga Agusta.
Bayanai sun ce ana ganin wannan matakin zai iya haddasa rikici mai tsanani tsakanin Amurka da biyu daga cikin manyan abokan kasuwancinta.
An sanya dokar hana fita a Adamawa Tinubu ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki a Saint Lucia da BrazilTrump ya yi cikakken bayani kan wadannan haraje-harejen ne a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, yana mai cewa matuƙar ba a cimma wata tartibiyar matsaya ba, ba shakka zai ƙara lafta musu harajin.
Wannan na daga cikin jerin sabbin haraje-haraje da Trump ke kara wa abokan kasuwancin Amurka a wani abu da ya zama ginshiki yayin yakin neman zabensa.
Mista Trump ya ce matakin zai zama tushen farfado da tattalin arzikin Amurka, inda ya zargi sauran kasashe da zaluntar Amurka na tsawon shekaru.
A cikin wasikarsa ga shugabar Mexico, Claudia Sheinbaum, Trump ya yarda cewa kasar ta taimaka wajen dakile kwararar bakin haure da miyagun kwayoyi irin su fentanyl zuwa Amurka.
Amma ya ce Mexico ba ta yi isasshen kokari ba don hana Arewacin Amurka zama dandalin masu safarar miyagun kwayoyi.
A cikin wasikarsa zuwa ga Tarayyar Turai kuma, Trump ya bayyana cewa gibin cinikayya tsakanin Amurka da EU barazana ce ga tsaron kasa.
A martaninta ga wannan matakin, Shugabar Hukumar Tarayyar Turai, Ursula von der Leyen ta fada a ranar Asabar cewa EU na shirye ta dauki matakin rama wa kura aniyarta don kare muradun tarayyar idan Amurka ta sanya harajin kashi 30 cikin 100 kan kayayyakin Turai daga ranar 1 ga Agusta.
Sai dai von der Leyen wacce ke kula da kasuwancin kasashen EU 27 ta ce kungiyar tana da niyyar ci gaba da kokarin cimma yarjejeniya kafin sabon wa’adin na shugaba Trump.
Ta kara da cewa kasashen kalilan ne ke yin dalla-dalla kan harkokin cinikayya kamar Tarayyar Turai tare kuma da bin ka’idojin kasuwanci na gaskiya.
Shugabar ta EU ta yi kalaman ne a matsayin martani kan barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ya sake yi a ranar Asabar, wacce ke kara tayar da fargabar barkewar yakin kasuwanci da Turai ke fatan kauce wa.
Von der Leyen ta kuma ce EU za ta dauki duk matakan da suka dace don kare muradunta ciki har da ramawa kura aniyarta idan bukatar hakan ta taso.