HausaTv:
2025-11-13@21:37:18 GMT

Isra’ila ta katse wutar lantarki a zirin Gaza

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnatin Isra’ila ta sanar da katse wutar lantarki a Zirin Gaza.

Ministan Makamashi na Isra’ila Eli Cohen ne ya sanar da matakin da gwamnatin kasar ta dauka na katse wutar lantarki a zirin, a yayin da wasu rahotanni ke cewa mataki na gaba bayan katsewar wutar lantarkin, shi ne yanke ruwa a arewacin zirin Gaza.

Ya ce matakin da gwamnatin kasar ta dauka na kara kaimi ne domin kwato dukkan mutanen da ake garkuwa dasu tare da tabbatar da cewa Hamas ba za ta ci gaba da zama a Gaza ba bayan yakin.

A daya banagaren kuma Ministan kudi na Isra’ila ya yi ikirarin cewa gwamnatin kasar za ta hada kai da gwamnatin Amurka karkashin jagorancin Donald Trump domin sanin kasashen da za su karbi bakoncin bakin haure daga Gaza.

A baya-bayan nan ne shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar da shirin tilastawa mazauna yankin Zirin Gaza zuwa kasashen Jordan da Masar da ke makwabtaka da ita.

Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi da Sarkin Jordan Abdallah na biyu sun yi kakkausar suka ga shirin mamayar tare da jaddada cewa ba za su iya karbar sabbin ‘yan gudun hijira ba.

Jami’an kasashen Jordan da Masar da kuma wasu kasashen Larabawa sun jaddada cewa dole ne a kafa kasar Falasdinu, kuma a bar al’ummarta su zabi makomarsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministocin harkokin wajen kasashen yamma sun yi Allah wadai da ta’asar RSF a El Fasher Darfur

Kungiyar kasashe da cibiyoyin kasa da kasa ta fitar da wata sanarwa ta haɗin gwiwa da ta yi Allah wadai da manyan laifukan da aka aikata a ƙasar Sudan bayan kwace El Fasher daga dakarn (RSF) suka yi, da kuma ƙaruwar tashin hankali a yankin arewacin Darfur da Kordofan.

Wannan sanarwar, wadda ministocin harkokin waje da manyan jami’ai daga Australia, Belgium, Kanada, Denmark, Estonia, Hukumar Tarayyar Turai, Jamus, Iceland, Ireland, Luxembourg, New Zealand, Netherlands, Norway, Slovakia, Slovenia, Spain, Sweden, da Birtaniya, tare da goyon bayan Austria, Croatia, Cyprus, Czechia, Finland, Latvia, Poland, Romania, da Switzerland suka yi, ta nuna damuwa sosai game da rahotannin ta’asar da aka aikata a kan fararen hula.

Wannan sanarwar haɗin gwiwa ta yi nuni da manyan zarge-zarge, ciki har da kisan gillar da aka yi wa fararen hula, cin zarafin mata dasauransu, da kuma amfani da yunwa a matsayin makamin yaƙi. An kuma nuna toshe hanyoyin tallafin jin kai a matsayin babban abin damuwa.

Sanarwar ta ce, “kin hari da gangan kan fararen hula, kisan gillar da aka yi wa jama’a bisa dalilai na kabilanci, cin zarafin mata da kananan yara, na a matsayin laifin yaƙi a bisa dokokin jin kai na duniya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Abdel-Aty: Diflomasiyya Ce Kawai Hanyar Da Maido Da Zaman Lafiya A Libya November 11, 2025 Larijani : ‘babu wani sabon sako’ da muka aika wa Amurka November 11, 2025 Gaza : Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau 282 tun bayan aiwatar da ita November 11, 2025 Iraki : Ana zaben ‘yan majalisa don tsara makomar siyasar kasar November 11, 2025 Sudan ta soki shirun kasashen duniya game ta’asar dake faruwa a kasar November 11, 2025 Hamas ta soki kudurin Isra’ila na yin dokar hukuncin kisa kan laifin ta’addanci November 11, 2025 Iran Za Ta Harba Taurarin Dan Adam Guda Uku Zuwa Sararin Samaniya November 11, 2025 Lebanon: An Saki Hannibal Kaddafi Bayan Zaman Kaso Na Shekaru 10 November 11, 2025 An Sake Bude Gidajen Mai Da Makarantu Da Aka Rufe A Kasar Mali November 11, 2025 Trump Ya Yi Wa Ma’aikatan Filayen Jiragen Sama Barazana November 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Na Shirye-Shiryen Aikewa Da Sojoji Guda 1000 A Iyakar Isra’ila Da Yankin Gaza
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • Sheikh Qassem: Kawar Da Hizbullah Ne Babban Burin Isra’ila A Lebanon
  • Masar Da Sudan Sun Jaddada Wajabcin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yankin
  • UNICEF ta ce Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza
  • Ministocin harkokin wajen kasashen yamma sun yi Allah wadai da ta’asar RSF a El Fasher Darfur
  • Gaza : Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau 282 tun bayan aiwatar da ita
  • Sudan ta soki shirun kasashen duniya game ta’asar dake faruwa a kasar
  • Hamas ta soki kudurin Isra’ila na yin dokar hukuncin kisa kan laifin ta’addanci
  • Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn