HausaTv:
2025-12-02@01:03:28 GMT

Isra’ila ta katse wutar lantarki a zirin Gaza

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnatin Isra’ila ta sanar da katse wutar lantarki a Zirin Gaza.

Ministan Makamashi na Isra’ila Eli Cohen ne ya sanar da matakin da gwamnatin kasar ta dauka na katse wutar lantarki a zirin, a yayin da wasu rahotanni ke cewa mataki na gaba bayan katsewar wutar lantarkin, shi ne yanke ruwa a arewacin zirin Gaza.

Ya ce matakin da gwamnatin kasar ta dauka na kara kaimi ne domin kwato dukkan mutanen da ake garkuwa dasu tare da tabbatar da cewa Hamas ba za ta ci gaba da zama a Gaza ba bayan yakin.

A daya banagaren kuma Ministan kudi na Isra’ila ya yi ikirarin cewa gwamnatin kasar za ta hada kai da gwamnatin Amurka karkashin jagorancin Donald Trump domin sanin kasashen da za su karbi bakoncin bakin haure daga Gaza.

A baya-bayan nan ne shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar da shirin tilastawa mazauna yankin Zirin Gaza zuwa kasashen Jordan da Masar da ke makwabtaka da ita.

Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi da Sarkin Jordan Abdallah na biyu sun yi kakkausar suka ga shirin mamayar tare da jaddada cewa ba za su iya karbar sabbin ‘yan gudun hijira ba.

Jami’an kasashen Jordan da Masar da kuma wasu kasashen Larabawa sun jaddada cewa dole ne a kafa kasar Falasdinu, kuma a bar al’ummarta su zabi makomarsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Kasar Ireland Ta Sauya Sunan Shugaban  “Isra’ila” Da Na Shahidiyar Falasdinu

A birnin Dublin na kasar Ireland an cire sunan tsohon sugaban “Isra’ila” Chaim Herzog,daga wata lambu na shakatawa a unguwar Ratgar, tare da maye gurbinsa da sunan Shahida Hind Rajab.

Jaridar “Vadiot-Ahranot” ta ‘yan sahayoniya ta buga labarin cewa, hukumar birnin Dublin a Ireland ta amince da a sauya sunan shugaban “Isra’ila” ta shida Chaim Herzog daga Lambun shakatawa,saboda matsin lambar kungiyoyin da suke goyon bayan Falasdinawa.

Jaridar ta ce sauya sunan wannan lambun yana da alaka ne da yakin Gaza, kuma an amince da shawarar da aka bijiro da ita a hukumar birnin ta hanyar kada kuri’u mafi rinjaye.

Wasu kungiyoyin da suke nuna goyon bayansu ga “Isra’ila” sun nuna rashin jin dadinsu da wannan matakin na sauya sunan lambun a birnin Dublin.

Lambun  da aka sauya sunansa yaka kusa da wasu makarantu ne biyu na yahudawa na Firamare da sakandire da su kadai ake da su a Ireland. An bude lambun ne dai a karon farko a 1985 da sunan Oril Kowir Park’ sai dai daga baya an sa masa sunan shugaban Haramtacciyar Kasar Isra’ila na shida ” Chaim Herzog. 

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Turkiya November 30, 2025 Iran ta bayyana halin da Falasdinawa ke ciki da rauni mufi da aka wa dan adam a doron kasa November 30, 2025 An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu November 30, 2025 Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5 November 30, 2025 Najeriya :  Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP November 30, 2025 An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru   November 30, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  •  Kasar Ireland Ta Sauya Sunan Shugaban  “Isra’ila” Da Na Shahidiyar Falasdinu
  •  Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki
  • Hizbullah Ta Bukaci Shugaban Cocin Katolika Na Duniya Yayi Tir Da Hare-haren Isra’ila
  • MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa
  • Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya
  • Lebanon ta shigar da kara ga Kwamitin Tsaro bayan Isra’ila ta Gina katanga a Yankinta
  • Kasashen Larabawa Sun Yi Tir Da Hare-Haren Soji Da Isra’ila Ke kai wa A Kasar Siriya