Isra’ila ta katse wutar lantarki a zirin Gaza
Published: 10th, March 2025 GMT
Gwamnatin Isra’ila ta sanar da katse wutar lantarki a Zirin Gaza.
Ministan Makamashi na Isra’ila Eli Cohen ne ya sanar da matakin da gwamnatin kasar ta dauka na katse wutar lantarki a zirin, a yayin da wasu rahotanni ke cewa mataki na gaba bayan katsewar wutar lantarkin, shi ne yanke ruwa a arewacin zirin Gaza.
Ya ce matakin da gwamnatin kasar ta dauka na kara kaimi ne domin kwato dukkan mutanen da ake garkuwa dasu tare da tabbatar da cewa Hamas ba za ta ci gaba da zama a Gaza ba bayan yakin.
A daya banagaren kuma Ministan kudi na Isra’ila ya yi ikirarin cewa gwamnatin kasar za ta hada kai da gwamnatin Amurka karkashin jagorancin Donald Trump domin sanin kasashen da za su karbi bakoncin bakin haure daga Gaza.
A baya-bayan nan ne shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar da shirin tilastawa mazauna yankin Zirin Gaza zuwa kasashen Jordan da Masar da ke makwabtaka da ita.
Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi da Sarkin Jordan Abdallah na biyu sun yi kakkausar suka ga shirin mamayar tare da jaddada cewa ba za su iya karbar sabbin ‘yan gudun hijira ba.
Jami’an kasashen Jordan da Masar da kuma wasu kasashen Larabawa sun jaddada cewa dole ne a kafa kasar Falasdinu, kuma a bar al’ummarta su zabi makomarsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika
Sabon bashin, ya nuna yadda Bankin ya bai wa kasar bashin da ya kai jimlar dala biliyan 5.1 tun daga ranar 31 na watan Okutobar 2025.
Kazalika, wannan sabon bashin, zai taimaka wa kashi na biyu na shirin habaka tattalin arziki a bangaren samar da makamashi da sauye-sauye, a fannin makamashin da cimma burin da ake da shi, na rage dumamar yanayi.
A zagaye na farko na shiri, za a kara karfafa sauye-sauye wajen tafiyar da kudade da tabbatar da ana aiki da Ka’ida da kuma sanya ido, kan yadda ake kashe kudaden Gwamnati.
Bugu da kari a zagaye na biyu kuma, manufar shi ne, a kara habaka samar da makamashi da fadada samar da wutar lantarki wanda hakan zai bayar da dama, wajen janyo kamfanonin masu zaman kansu domin su zuba jari, a fannin.
A jawabinsa Darakta Janar na Bankin a Nijeriya Abdul Kamara, ya sanar da cewa, a zagaye na farko na shirin ya hada da samar da sauye-sauye a fannin makamashi, musamman wajen habaka hanyar samar da kudaden shiga ga fannin da bai shafi Man Fetur ba.
Ya kara da cewa, shirin zai tallafa wa tsarin kasa na NDC wanda zai fara aiki daga 2026 zuwa 2030, musamman ganin cewa, shirin yayi daidai da koƙarin da ake yi na yakar sauyin yanayi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi December 6, 2025 Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabo Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi 20 da kwangiloli 5 a fannin fasaha December 6, 2025 Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Sheikh Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Lebanon Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye December 6, 2025 Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci