Ruftawar katanga ta yi ajalin uwa da ’ya’yanta 2 a Zariya
Published: 28th, August 2025 GMT
Musiba da auka wa wani gida a Zariya da ke Jihar Kaduna, bayan da katangar wani kango da ke maƙwabtaka da su ta faɗa wa mazauna gidan suna tsaka da barci.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, ruftawar ginin wadda ta auku a safiyar wannan Larabar ta yi ajalin matar gidan, Habiba Nuhu da ’ya’yanta biyu, Hauwa’u da Aina’u Nuhu.
Sai dai mijinta, wanda shi ma ya samu rauni a sakamakon faruwar lamarin, tuni an sallamo shi bayan duba lafiyarsa a asibiti.
Wani maƙwabcinsu, Malam Ahmed, ya shaida wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4 na asubahi, lokacin da iyalin ke barci.
Sai dai ya ce “a gaskiya wannan tsohon gini ne da aka bari babu gyara, wanda hakan ne ya sa ya rushe.
“Ba zato ba tsammani kawai ginin ya faɗa musu,” in ji shi.
Tuni dai an yi jana’izar mamatan kamar yadda addinin musulunci ya tanada.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ya ya Jihar Kaduna Ruftawar gini Uwa Zariya
এছাড়াও পড়ুন:
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp