Rundunar ‘Yan sanda a jihar Kwara ta ce ta fara bincike kan kisan da aka yi wa Alhaji Idris Abubakar, shugaban kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) na jihar.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Adetoun Ejire-Adeyemi ya fitar, ya ce an harbe shugaban ne a ranar 8 ga Maris, 2025 a kofar gidansa da ke Oke-Ose, a unguwar Ilorin.

A cewar sanarwar Jami’an ‘yan sanda sun garzaya inda lamarin ya faru nan take, inda suka gano kwamson harsashi guda biyar da aka yi amfani da su wajen yin harbin.

Ya bayyana cewa Hukumar Binciken Laifukan Jiha (SCID) ta fara gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Ta kuma bada tabbacin za a gano, tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya, sannan ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da bayanai masu muhimmanci ga ‘yan sanda.

A halin da ake ciki kungiyar Miyetti Allah reshen jihar Kwara, ta bayyana kaduwarta dangane da kisan da aka yi wa shugaban ta Alhaji Idris Abubakar Sakaina, wanda wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kashe a  gidansa da ke Oke-ose da misalin karfe 10 na dare.

A wata sanarwa da shugaban Fulanin (Ardon Ardodi) a jihar Kwara, Alhaji Ojonla Mahmud ya fitar dauke da sa hannun sakataren kungiyar MACBAN ta jihar, AbdulAzeez Muhammed ya bukaci hukumomin tsaro da su gaggauta zakulo wadanda suka gudu domin tabbatar da sun fuskanci hukunci.

Sanarwar ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta taimaka wa iyalan mamacin wajen samar da ingantaccen ilimi ga yaran da kuma kyautata jin dadinsu.

Ali Muhammad Rabi’u

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200

Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Godswill Akpabio ya shigar da Sanata Natasha Akpoti ƙara a kotu kan zargin ɓata masa suna yana mai neman ta biya shi diyyar naira biliyan 200.

Sanata Natasha mai wakiltar jihar Kogi ta tabbatar da karɓar sammacin a shafukanta na sada zumunta, inda ta nuna jin daɗinta tana mai cewa ta samu damar bayyana hujjojinta kan zargin yunƙurin lalata da ta zarge shi da yi a baya.

“Yau 5 ga watan Disamban 2025, na karɓi sabon sammacin kotu kan ƙarar diyya ta naira biliyan 200 da Sanata Godswill Akpabio ya kai ni game da ɓata masa suna da zargin lalata,” a cewar Natasha.

“Na yi farin ciki da Sanata Akpabio ya taso da wannan batu saboda kwamatin ɗa’a na majalisa ya ƙi amincewa ya saurare ni kan batun sakamakon matar Akpabio ta shigar da ni ƙara a kotu.”

A watan Fabrairun 2025 ne Natasha ta zargi Akpabio da neman yin lalata da ita bayan rikicin da ya ɓarke a tsakaninsu, wanda ya kai ga dakatar da ita daga zaman majalisar na tsawon wata shida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166
  • Dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama ni — Muhuyi
  • ’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara