‘Yan Sanda Sun Fara Bincike Kan Kisan Shugaban Kungiyar Miyetti Allah A Kwara
Published: 10th, March 2025 GMT
Rundunar ‘Yan sanda a jihar Kwara ta ce ta fara bincike kan kisan da aka yi wa Alhaji Idris Abubakar, shugaban kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) na jihar.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Adetoun Ejire-Adeyemi ya fitar, ya ce an harbe shugaban ne a ranar 8 ga Maris, 2025 a kofar gidansa da ke Oke-Ose, a unguwar Ilorin.
A cewar sanarwar Jami’an ‘yan sanda sun garzaya inda lamarin ya faru nan take, inda suka gano kwamson harsashi guda biyar da aka yi amfani da su wajen yin harbin.
Ya bayyana cewa Hukumar Binciken Laifukan Jiha (SCID) ta fara gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
Ta kuma bada tabbacin za a gano, tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya, sannan ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da bayanai masu muhimmanci ga ‘yan sanda.
A halin da ake ciki kungiyar Miyetti Allah reshen jihar Kwara, ta bayyana kaduwarta dangane da kisan da aka yi wa shugaban ta Alhaji Idris Abubakar Sakaina, wanda wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kashe a gidansa da ke Oke-ose da misalin karfe 10 na dare.
A wata sanarwa da shugaban Fulanin (Ardon Ardodi) a jihar Kwara, Alhaji Ojonla Mahmud ya fitar dauke da sa hannun sakataren kungiyar MACBAN ta jihar, AbdulAzeez Muhammed ya bukaci hukumomin tsaro da su gaggauta zakulo wadanda suka gudu domin tabbatar da sun fuskanci hukunci.
Sanarwar ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta taimaka wa iyalan mamacin wajen samar da ingantaccen ilimi ga yaran da kuma kyautata jin dadinsu.
Ali Muhammad Rabi’u
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Antonio Guterres Ya Kira Yi Kungiyar G 20 Da Su Warware Matsalar Rashin Adalci A Harkokin Kasuwanci
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres ya yi kira ga shugabannin kasashen duniya da suke taro a birnin Johannesburg na kasar Afirka Ta Kudu da su warware matsalar rashin daidaito a cikin harkokin kasuwanci a tsakanin kasashe.
Babban magatakardar MDD wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron na G 20 ya yi Ishara da gibin kasuwanci da ake da shi a tsakanin kasashen da su ka ci gaba da masu tasowa wanda ya kamata a san yadda za a magance shi.
Antonio Gutrres ya kuma ce: “Wani abu guda daya wanda zan iya bayar da tabbaci a kansa shi ne cewa ofishin babban magatakardar MDD zai yi duk abinda zai iya yi domin yin gyara a cikin rashin daidaito da rashin adalci, sannan kuma ya tabbatar da cewa kasashe masu tasowa sun sami kyakkyawan wakilci.
Sai dai kuma babban magatakardar kungiyar ta MDD ya yi Ishara akan yadda MDD take da iyaka da raunin samar da sauyi a cikin mihimman cibiyoyin duniya da ake da su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Fitar Da Kudurin Bayan Taron Kungiyar G20 Ba Tare Da Halartar Kasar Amurka Ba November 23, 2025 An Kulla Yarjejeniyar Aikin Soja A Tsakanin Kasashen UAE Da Ethiopia November 23, 2025 Pezeshkian: Iran na Allawadai da hare-haren Isra’ila a kan Lebanon November 23, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161 November 23, 2025 Esma’il Khatib: Isra’ila Na Fuskantar Manyan Ayyukan Leken Asiri Daga Iran November 23, 2025 An Gabatar Da Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar G20 Duk Tare Da Kauracewar Amurka November 23, 2025 Zabebben Magajin Garin Birnin NewYork Ya Nanata Cewa HKI Tana Aikata Kissan Kiyashi A Gaban Trump November 23, 2025 Venezuela Ta Gargadi Amurka Kan Shirin Tada Hankali A Kan Iyakokin Kasar November 23, 2025 CAN: Yawan Yaran Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Ranar Jumma’a Sun Fi 300 November 23, 2025 Ribadu Ya Gana da Sakataren Yakin Amurka Kan Batun Kashe Kiristoci A Nijeriya November 22, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci