‘Yan Sanda Sun Fara Bincike Kan Kisan Shugaban Kungiyar Miyetti Allah A Kwara
Published: 10th, March 2025 GMT
Rundunar ‘Yan sanda a jihar Kwara ta ce ta fara bincike kan kisan da aka yi wa Alhaji Idris Abubakar, shugaban kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) na jihar.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Adetoun Ejire-Adeyemi ya fitar, ya ce an harbe shugaban ne a ranar 8 ga Maris, 2025 a kofar gidansa da ke Oke-Ose, a unguwar Ilorin.
A cewar sanarwar Jami’an ‘yan sanda sun garzaya inda lamarin ya faru nan take, inda suka gano kwamson harsashi guda biyar da aka yi amfani da su wajen yin harbin.
Ya bayyana cewa Hukumar Binciken Laifukan Jiha (SCID) ta fara gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
Ta kuma bada tabbacin za a gano, tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya, sannan ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da bayanai masu muhimmanci ga ‘yan sanda.
A halin da ake ciki kungiyar Miyetti Allah reshen jihar Kwara, ta bayyana kaduwarta dangane da kisan da aka yi wa shugaban ta Alhaji Idris Abubakar Sakaina, wanda wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kashe a gidansa da ke Oke-ose da misalin karfe 10 na dare.
A wata sanarwa da shugaban Fulanin (Ardon Ardodi) a jihar Kwara, Alhaji Ojonla Mahmud ya fitar dauke da sa hannun sakataren kungiyar MACBAN ta jihar, AbdulAzeez Muhammed ya bukaci hukumomin tsaro da su gaggauta zakulo wadanda suka gudu domin tabbatar da sun fuskanci hukunci.
Sanarwar ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta taimaka wa iyalan mamacin wajen samar da ingantaccen ilimi ga yaran da kuma kyautata jin dadinsu.
Ali Muhammad Rabi’u
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
Daga Bello Wakili
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ganawar sirri da gwamnonin jihohi shidda daga sassan ƙasar a ci gaba da tattaunawar da ake yi domin ƙarfafa batun tsaro a ƙasa.
Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo, Umar Namadi na Jigawa, Nasir Idris na Kebbi, Ahmed Ododo na Kogi, Lucky Aiyedatiwa na Ondo, da Ahmed Aliyu na jihar Sokoto.
Taron, wanda ya ɗauki kusan mintuna 40, ya mayar da hankali ne kan muhimman matsalolin tsaro da ke shafar jihohinsu, duk da cewa ba a bayyana cikakkun bayanai ba.
Wakilin Rediyon Najeriya da ke fadar shugaban kasa ya ruwaito cewa wannan zaman na daga cikin kokarin shugaban kasa na ƙara haɗin kai da jihohi wajen magance matsalolin tsaro.
Wannan cigaban ya biyo bayan nasarar da Gwamnatin Tarayya ta samu na kubutar da dalibai 100 da aka yi garkuwa da su a Jihar Neja, baya ga wanda aka yi a Jihar Kebbi.
Ci gaba da irin waɗannan tattaunawa na shugaban kasa na nuna jajircewar gwamnati wajen tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin ƙasar.