HausaTv:
2025-11-25@06:52:45 GMT

Masana A Iran Sun Samar Da Maganin Rashin Haihuwa Na Maza

Published: 9th, March 2025 GMT

Masana a jami’ar Tehran sun samar da wani sabon salo na magance matsalar rashin haihuwa da wasu maza suke fama da shi.

Ta hanyar aikin hadin gwiwa tsakanin injiniya a fagen kere-kere dake jami’ar Tehran Muhammad Mahdi Takiyyah, da kuma Mahdi Zand, da Mansurah muwahhidin daga jami’ar Tarbiyat-Mudarrris, an samar da hanyar magance rashin haihuwar bisa dogaro da nau’oin matsaloli mabanbata da maza suke da su.

Sabon maganin dai an gina shi ne akan kyautata ingancin ruwan maniyin masu fama da wannan matsalar, kamar yadda bayanan farko suna nuna.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 

Ƙungiyar Ƙwadago ta Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa (NUEE) ta yi barazanar dakatar da dukkan ayyukan samar da wutar lantarki a faɗin Najeriya, sakamakon harin da ta ce jami’anta sun fuskanta a Jihar Imo.

Ƙungiyar ta bayyana cewa wasu jami’an ’yan sanda ɗauke da makamai ne suka kai wa ma’aikatanta hari a Egbu 132/33kB Transmission Substation da ke Owerri, Jihar Imo, lamarin da ya janyo fargaba da tayar da hankali ga ma’aikatan da ke wurin.

Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi

A wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na ƙasa ya fitar, NUEE ta ce wannan hari na nuna take haƙƙin ma’aikaci, kuma ba za a lamunta da shi ba.

NUEE ta bayyana cewa ba za ta yi shiru ba yayin da tsaro da mutuncin mambobinta ke fuskantar barazana ba.

Sanarwar ta ce, “Wannan hari da jami’an tsaro suka kai ya saɓa wa duk ka’idojin aikin yi. Jami’anmu na gudanar da aikinsu ne na yau da kullum, amma aka afka musu da duka da barazana. Mun gaji da irin wannan cin zarafi.”

Ƙungiyar ta gargaɗi gwamnati da shugabannin rundunar ’yan sanda da cewa za ta rufe dukkan tashoshin wutar lantarki a sassan ƙasar, muddin ba a ɗauki matakin hukunta masu laifin da kuma bada tabbacin tsaron ma’aikata ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool
  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Shirin Samar Da Tsaro A Makarantun Najeriya Ke Ciki
  • Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji
  • Antonio Guterres Ya Kira Yi Kungiyar G 20 Da Su Warware Matsalar Rashin Adalci A Harkokin Kasuwanci
  • Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 
  • Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF
  • H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba
  • Obi ya yi watsi da hukuncin ɗaurin rai da rai da aka yi wa Kanu
  •  Afirka Ta Kudu: Rashin Halartar Amurka Taron G-20 Ba Zai Yi Wani Tasiri Ba