Ya ce: “Za mu yi amfani da dandamalin Taron Kasuwanci na Faransa da Nijeriya domin isar da saƙon da Shugaban Ƙasa ke son mu isar a wannan shekara.

 

“Wannan shekara, 2025, ita ce shekarar da za a ƙarfafa tattalin arziki da zamantakewa a Nijeriya kamar yadda Shugaban Ƙasa ya alƙawarta. Kamar yadda kuka ji a lokuta da dama, tattalin arzikin mu ya fara samun ingantacciyar nasara.

Farashin abinci da ya hauhawa a baya yana sauka.

 

“Darajar Naira na fara nuna alamun daidaituwa, kuma duk shirin gyaran tattalin arzikin da Shugaban Ƙasa ya aiwatar suna fara samun nasara, kuma da yardar Allah, za mu kai ga burin da muke nema.”

 

Ministan ya amince da cewa kowace ƙasa da ke aiwatar da sauye-sauye na tattalin arziki da zamantakewa tana fuskantar ƙalubale, amma ya jaddada cewa tsare-tsaren Shugaban Ƙasa Tinubu sun taimaka wajen rage wahalar da ke tattare da irin waɗannan sauye-sauye.

 

Ya ce: “Kowace ƙasa da ta aiwatar da wani sauyi na zamantakewa da tattalin arziki tana fuskantar matsaloli a farkon tafiya, amma ina ganin cewa a Nijeriya, an rage tsawon wannan lokaci saboda hangen nesa, jajircewa, da ƙarfin gwiwar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke da shi cewa wannan gyara zai kai Nijeriya ga ci gaba mai ɗorewa.”

 

Idris ya bayyana Faransa a matsayin muhimmiyar abokiyar hulɗar Nijeriya kuma ya buƙaci gwamnatin Faransa da ta mara wa shirin gyaran tattalin arzikin Tinubu baya domin ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu.

 

Har ila yau, ya jinjina wa Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, bisa girmamawar da ya yi wa Shugaban Ƙasa Tinubu ta gayyata zuwa ziyarar gwamnati a watan Nuwamba 2024, yana mai cewa irin wannan girmamawa ba kasafai ake yi wa shugabanni ita ba.

 

Ministan ya tabbatar wa jakaden na Faransa cewa Nijeriya za ta ci gaba da aiwatar da duk yarjejeniyoyin da ta ƙulla da gwamnatin Faransa a lokacin ziyarar Shugaban Ƙasa Tinubu.

 

Haka kuma, Idris ya yaba wa Jakada Fonbaustier bisa ƙoƙarin sa na inganta hulɗar Nijeriya da Faransa tun daga lokacin da aka naɗa shi.

 

A nasa jawabin, Jakada Fonbaustier ya ce ziyarar sa ta ƙunshi ƙirƙirar hanyoyin aiwatar da yarjejeniyoyin da Shugabannin ƙasashen biyu suka cimma a lokacin ziyarar Shugaban Ƙasa Tinubu a Faransa a bara.

 

Ya bayyana ƙudirin gwamnatin Faransa na tallafa wa Nijeriya wajen inganta hanyoyin sadarwa da fasahar yaɗa labarai.

 

Ya ce: “Dole ne mu tabbatar da cewa an yi aiki tuƙuru don bin diddigin ziyarar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a birnin Paris a watan Nuwamba.

 

“Shugabannin biyu sun tsara wata sabuwar hanya mai faɗi don haɓaka dangantaka, kuma a wannan fanni, sadarwa da watsa labarai suna da matuƙar muhimmanci.

 

‘A nan ne Faransa za ta iya bayar da gudunmawa ta fuskar ƙwarewa da fasaha.”

 

Jakaden ya bayyana Minista Idris a matsayin gwarzon sauyi a fannin sadarwa a Nijeriya, yana mai cewa matsayin sa a gwamnatin Tinubu ya dace da inganta matsayin Nijeriya a idon duniya da kuma janyo hannun jari daga ‘yan kasuwar Faransa da za su hallara a Paris a ranar 10 ga Afrilu, 2025, don Taron Kasuwanci na Faransa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa Tinubu da Shugaban Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka

Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), ta yi alƙawarin kare dimokuraɗiyya da kuma inganta tsaro a yankin Yammacin Afirka.

Wannan alƙawarin na zuwa ne a dai-dai lokacin da yankin ke fuskantar matsalolin tsaro da na juyin mulki.

Yadda aka yi bikin naɗa Rarara sarkin wakar ƙasar Hausa a Daura Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano

An yanke wannan shawara ne a taron shugabannin ƙasashen ECOWAS karo na 68, wanda aka gudanar a Abuja a ranar Lahadi.

Shugaba Bola Tinubu, wanda Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya wakilta, ya yi kira ga ƙasashen ECOWAS da su zauna lafiya tare da haɗa kai.

Ya yi gargaɗi ncewa ƙungiyar tana samun rauni idan ƙasashe suka rabu.

Ya ce ƙasashen Yammacin Afirka ba wai waje ɗaya suka haɗa ba, face suna da tarihi, al’adu da gwagwarmaya iri ɗaya da ta haɗa su.

Shugaba Tinubu, ya bayyana cewa duk da cewa rashin jituwa na iya faruwa tsakanin ƙasashe, bai kamata hakan ya karya zumunci da makomar ƙasashen yankin ba.

Ya zayyano matsalolin da yankin ke fuskanta, kamar ta’addanci, rikice-rikice, tsattsauran ra’ayi, juyin mulki, laifukan ƙetare iyaka, yawaitar makamai, barazana a Intanet, sauyin yanayi, ƙarancin abinci da sauransu.

Ya ce waɗannan matsaloli ba su da iyaka, kuma ƙasa ɗaya ba za ta iya magance su ba.

Tinubu ya tarbi shugabannin ECOWAS zuwa Abuja, inda ya yi fatan taron zai ƙara amincewa da juna, ƙarfafa haɗin kai, tare da sake ɗora ECOWAS bisa ginshiƙan adalci da makoma ɗaya.

A yayin taron, ECOWAS ta kuma mayar da hankali kan bunƙasar tattalin arziƙi ta hanyar kamfanoni masu zaman kansu.

Shugaban Hukumar ECOWAS, Dokta Omar Alieu Touray, ya sanar da kafa Majalisar Kasuwanci ta ECOWAS.

An naɗa fitaccen ɗan kasuwan Najeriya, Alhaji Aliko Dangote, a matsayin shugaban farko na wannan majalisa.

Shugaban ƙasar Saliyo kuma Shugaban ECOWAS, Julius Maada Bio, ya bayyana taron a matsayin mai muhimmanci.

Ya ce yankin Yammacin Afirka na fuskantar manyan ƙalubale na tsaro, dimokuraɗiyya da tattalin arziƙi, kuma shawarwarin da za a yanke za su shafi sama da mutum miliyan 400.

Ya kuma bayyana cewa an yi murnar cikar ECOWAS shekaru 50 da kafuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026