Ya ce: “Za mu yi amfani da dandamalin Taron Kasuwanci na Faransa da Nijeriya domin isar da saƙon da Shugaban Ƙasa ke son mu isar a wannan shekara.

 

“Wannan shekara, 2025, ita ce shekarar da za a ƙarfafa tattalin arziki da zamantakewa a Nijeriya kamar yadda Shugaban Ƙasa ya alƙawarta. Kamar yadda kuka ji a lokuta da dama, tattalin arzikin mu ya fara samun ingantacciyar nasara.

Farashin abinci da ya hauhawa a baya yana sauka.

 

“Darajar Naira na fara nuna alamun daidaituwa, kuma duk shirin gyaran tattalin arzikin da Shugaban Ƙasa ya aiwatar suna fara samun nasara, kuma da yardar Allah, za mu kai ga burin da muke nema.”

 

Ministan ya amince da cewa kowace ƙasa da ke aiwatar da sauye-sauye na tattalin arziki da zamantakewa tana fuskantar ƙalubale, amma ya jaddada cewa tsare-tsaren Shugaban Ƙasa Tinubu sun taimaka wajen rage wahalar da ke tattare da irin waɗannan sauye-sauye.

 

Ya ce: “Kowace ƙasa da ta aiwatar da wani sauyi na zamantakewa da tattalin arziki tana fuskantar matsaloli a farkon tafiya, amma ina ganin cewa a Nijeriya, an rage tsawon wannan lokaci saboda hangen nesa, jajircewa, da ƙarfin gwiwar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke da shi cewa wannan gyara zai kai Nijeriya ga ci gaba mai ɗorewa.”

 

Idris ya bayyana Faransa a matsayin muhimmiyar abokiyar hulɗar Nijeriya kuma ya buƙaci gwamnatin Faransa da ta mara wa shirin gyaran tattalin arzikin Tinubu baya domin ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu.

 

Har ila yau, ya jinjina wa Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, bisa girmamawar da ya yi wa Shugaban Ƙasa Tinubu ta gayyata zuwa ziyarar gwamnati a watan Nuwamba 2024, yana mai cewa irin wannan girmamawa ba kasafai ake yi wa shugabanni ita ba.

 

Ministan ya tabbatar wa jakaden na Faransa cewa Nijeriya za ta ci gaba da aiwatar da duk yarjejeniyoyin da ta ƙulla da gwamnatin Faransa a lokacin ziyarar Shugaban Ƙasa Tinubu.

 

Haka kuma, Idris ya yaba wa Jakada Fonbaustier bisa ƙoƙarin sa na inganta hulɗar Nijeriya da Faransa tun daga lokacin da aka naɗa shi.

 

A nasa jawabin, Jakada Fonbaustier ya ce ziyarar sa ta ƙunshi ƙirƙirar hanyoyin aiwatar da yarjejeniyoyin da Shugabannin ƙasashen biyu suka cimma a lokacin ziyarar Shugaban Ƙasa Tinubu a Faransa a bara.

 

Ya bayyana ƙudirin gwamnatin Faransa na tallafa wa Nijeriya wajen inganta hanyoyin sadarwa da fasahar yaɗa labarai.

 

Ya ce: “Dole ne mu tabbatar da cewa an yi aiki tuƙuru don bin diddigin ziyarar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a birnin Paris a watan Nuwamba.

 

“Shugabannin biyu sun tsara wata sabuwar hanya mai faɗi don haɓaka dangantaka, kuma a wannan fanni, sadarwa da watsa labarai suna da matuƙar muhimmanci.

 

‘A nan ne Faransa za ta iya bayar da gudunmawa ta fuskar ƙwarewa da fasaha.”

 

Jakaden ya bayyana Minista Idris a matsayin gwarzon sauyi a fannin sadarwa a Nijeriya, yana mai cewa matsayin sa a gwamnatin Tinubu ya dace da inganta matsayin Nijeriya a idon duniya da kuma janyo hannun jari daga ‘yan kasuwar Faransa da za su hallara a Paris a ranar 10 ga Afrilu, 2025, don Taron Kasuwanci na Faransa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa Tinubu da Shugaban Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin Shirin na duniyarmu a yau shiri wanda yake kawo maku labarai masu muhimmanci a makon da ya gabata, wadanda suka shafi siyasa tattalin arziki zamantakewa tsaro da sauransu. Sannan daga karshe idan akwai lokaci mu ji ra’ayin masana dangane da su. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

///…Madallah, masu sauraro labarimmu na farko a wannan Shirin shi ne, dangane da furucin jakadan Amurka na musamman a kasar Tom Barrack wanda ya bayyana ‘shirin Amurka na 5’ dangane da siyasar Amurka a kan kasar Iran ya wargaje bayan rashin nasarar da ta fuskanta a yankin kwanaki 12 na watan yunin da ya gabata.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya nakalto Barrack yana fadar haka a wata hira da ta hada shi da kamafanin dillancin labaran National ta

(UAE) a cikin yan kwanakin da suka gabata. Inda Baraka ya bayyana cewa manufar Amurka a yakin kwanaki 12 da kasar Iran ba ‘kifar da gwamnatin; JMI ba. Amma ganin yadda Shirin ya lalace, Amurka ta kasa cimma manufofinta a kasar Iran yanzun kuma sai wasu sibbin dabaru, saboda ganin mutanen kasar Iran suka taron suka taimakawa gwamnatin kasarsu. Suka kuma hanata faduwa saboda hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar.

Sai dai masana da dama suna ganin wannan ba gaskiya bane, saboda an jima da sanin cewa gwamnatin kasar Amurka da HKI suna Shirin kifar da gwamnatin JMI tun farkon nasarar juyin juya halin musulunci a kasar amma suka kasa yin hakan. .

Banda haka a aikace gwamnatin kasar Amurka ta nuna cewa tana son ganin bayana JMI, kama daga juyin mulkin da ta shiya a farko farkon nasarar juyin juya halin musulunci a shekara 1980. Wannan itace manufa. Sannan manufar kasashen yamma daga ciki har da Amurka na ingiza Sadam Hussain ya farwa kasar Iran da yaki da kuma tallafa masa da makamai, wadanda kuma suka hada har da makaman guba, ba kome bas ai don kifar da JMI tun tana jajiri. Amma sun kasa samun hana har aka kawo karshen yaki bayan shekaru 8.

Sai kuma yake-yaken da Amurka da kawayenta suka cilla a kan yankin Asiya da kudu da kuma Afganistan suna nufin karkaresu da kasar Iran ne. Mamayar Afganistan a shekara 2002 da kuma Iraki a shekara ta 2003 da tura yan ta’adda zuwa cikin kasar Siriya da Iraki a shekara ta 2014. Da sauransu duk tare da Shirin gurgurta kasar Iran ce da kuma kifar da ita idan hakan zai yu. Amma bai yu ba.

Banda haka takunkuman tattalin arziki  kasashen yamma musamman Amurka sun fara aiki a kan kasar Iran tun bayan nasarar juyin juya halin musulunci a shekara 1979 tare da dakatar da sayan danyen mai na JMI. Wadan nan takunkuman sun yi ta karuwa da kuma fadada harzuwa lokacinda suka kai kololuwarsu a zamanin Trump na farko wato 2018.

Kuma a lokacin John Bulton mai bawa shugaban kasar Amurka shawara a kan harkokin tsaro yana fada a wani taro na masu adawa da JMI a birnin Paris na kasar Faransa kan cewa JMI ba zata ga bukukuwan juyin juya halin musulunci nag aba ba. Duk wannan ya zo ya wuce ba tare da samun nasara ba.

A wani bangare kuma gwamnatocin Amurka daya bayan daya, sai da suka yi kokarin tada rikici a cikin kasar Iran, don kawo karshen gwamnatin JMI daga cikin gida. Kama daga rikicin zabe na shekara ta 2009, inda suka yi amfani da yan Takara wadanda basu sami nasar a zaben ba, wato Mir Hussain Musawi da kuma Karubi suka hadda rikicin da ba’a taba yi ba a kasar, da nufin kawo karshen JMI amma a nan ma suka kasa, saboda goyon bayan da mutanen kasar Iran suke bawa tsarin JMI.

Sannan masa Amini ba kurdiya wacce ta yankje jiki ta fada a ofishin jami’a tsaro masu kula dahalaye masu kyau da kuma tabbatar da dokar sanya hijabi. A nan ma ma’aikatan CIA da MOSAD a cikin gida sun yi amfani da wannan damar don ingiza mutane su kawo karshen JMI, amma ma har rikicin ya lafa basu cimma manufarsu ba. Haka ma rikicin kara farashin man fetur a kasar kasashen yamma sun yi kokarin ingiza mutanen kan gwamnatin JMI don kawo karshenta amma suka gaza.

Bayan dukkan wannan gazawar ne Trump da HKI ya shigo kai tsaye da manufar kifar da JMI a ranar 13 ga watan Yulin shekara ta 2025, bayan kashe manya -manyan gwamnadojin sojojin kasar Iran. Kama daga shugaban rundunar IRGC Shahid Manjo Janar Hissain Samali, da babban hafsan hafsoshi kuma babban kwamandan sojojin  kasar Iran Manjo janar Mohammad Bakiri, da babban kwamandon sojojin kare sararin samaniya, da kuma bangaren makamai masu   Amir Ali  Hajizadeh da sauransu.

Suna tsamman idan sun kashe wadanda sun rikita harkokin tsaron JMI kenan kome kuma zai rugurgije, amma a cikin yan sa’o’I aka maye gurbinsu sanna JMI ta fara maida martini mai tsanani a kan HKI, sannan a kan Amurka daga baya a kan sansanin sojojinta take al-udait a kasar Qatar.

Bayan haka ne Trump ya gano cewa, illar da JMI tayi mata da kuma HKI sun bayyana a fili ga kowa a duniya, a sannan ne ya sauya shawara ya kuma bukaci a tsada yakin.

Wadan na dukka, shaidu ne wadanda suka tabbatar da cewa gwamnatocin kasashen yamma musamman Amurka suna son ganin bayan JMI. Don haka maganar Tom Barrack na cewa manufar Amurka a yakin kwanaki 12 ba kifar da gwamnatin JMI ba, ba gaskiya bane. Sai dai sun kasa samun hakan.

Ko a cikin yan makonni da suka gabata Tom Barrack da kansa ya bayyana cewa sun yi kokarin kifar da gwamnatin JMI har sau biyu a kasar Iran sun kasa, sannan a halin yanzu ya zo yace manufarsu ba kifar da gwamnatin ba? Wannan ba haka ne ba. Kuma abinda ya tabbata a tarin rikci tsakanin Amurka da JMI ya nuna cewa Amurka tana da wannan manufar tun farkon nasarar juyin juya halin musulunci a nan Iran.

Masana suna ganin zancen wai Amurka bata nufin sauya gwamnati a kasar, hanya ce ta kaucewa irin koma bayan da Amurka ta fuskanta a wannan fagen. Don Iran ta bayyana cewa tana da karfi.

Masana suna ganin rashin nasarar da Amurka ta yi a yakin da ita da HKI suka kaddamar a kasar Iran ya kara bayyana cewa al-amura da dama sun sauya a duniya, kuma yanking abas ta tsakiya kafin yakin kwanaki 12 ba kuma daya take da yankin a bayan yakin ba.

Banda haka matsayin Amurka a duniya ba kuma matsayin ta a bayan yakin ba. Saboda yadda Amurka take kallon Iran bayan yakin ba kuma haka take kallonta a bayansa ba. Amurka bata tsammanin kasar Iran tana da karfin jurewa farmakon da ita da HKI suka kai mata a cikin watan yunin da ya gabata ba. Su suka fara yaki amma kuma su suka bukaci a tsagaita budewa juna wuta, bayan da suka dandana wutan makamai masu linzami na kasar Iran kuma suka ji zafinsa.

Don haka bayan wannan yakin sun tabbatar da cewa makomar yanking abas ta tsakiya kuma ba a Washington ake fayyace shi ba, sai dai a filin daga a kasar Iran.

 A wani labarin kuma MDD ta bukaci gwamnatin Amurka ta kawo karshen takaita zirga-zirgan jami’an diblomasiyya JMI a birnin NewYork.

Farhan Haq mataimakin kakakin majalisar dinkin duniya ya bayyana cewa gwamnatin Amurka bata da hakkin takaita zirga-zirgan jami’an diblomasiyyar kasar Iran a birnin NewYork, saboda su ma jami’an diblomasiyya ne na MDD kamar ko wace kasa don haka a bisa yarjeniyan da aka da ita tun farkon kafa MDD a birnin News York Amurka bata da hurumin takaita ayyuka ko zirga zirgan Jami’an diblomasiyya na ko wace kasa mamba a matsalisar dinkin duniya.

Haq ya ce: matsayin MDD ita ce duk kasan da take daukar cibiyoyin MDD to dole ne su bar jami’an diblomasiyyar kasashen duniya wadanda suka zo kasar su gudanar da harkokinsu na rayuwa a cikin kasar, kasar Iran ko wata kasa.

Kafin haka dai JMI ta zargi gwamnatin kasar Amurka da takurawa jami’an diblomasiyyar kasarta wadanda suke aiki da MDD a birnin NewYork tare da korafi kan cewa gwamnatin Amurka tana sanya shinge da takunkumai a zirga zirgan jami’an diblomasiyyar kasar a cikin birnin NewYork.

Majiyar gwamnatin kasar Iran ta bayyana cewa gwamnatin kasar Amurka ta na takurawa Jami’an diblomasiyyar kasar Iran a birnin NewYork daga ciki har da hanasu zuwa sayayya na bukatun yau da kullom.

Iran da bukaci MDD ta tabbatar da cewa Gwamnatin Amurka ta bawa dukkan jami’an diblomasiyyar kasar Iran wadanda suka aiki da MDD hakkinsu na zama a birnin NewYork ta kuma tabbatar mata da cewa yin haka ya sabawa yarjeniyar samar da cibiyar MDD a birnin NewYork.

Kafin haka a watan Satumban da ya gabata jakadan kasar Iran a MDD Amir Hussain Iravani ya kai karar Amurka a gaban MDD kan yadda ta takaita zirga-zirgan shugaban kasa Masoud Pezeshkiya da kuma Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi a taron babban zauren MDD karo na 80th.

Labarin ya kara da cewa a bayan ma’aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta kafawa Jami’an jakadancin kasar Iran a MDD doka ta fita daga gidajensu don sayayya a cikin unguwar Manhatan na birnin NewYork sai da shaida mata kwanaki 5 kafin su fita.

Labarin ya kara da cewa jami’an diblomasiyyar kasar Iran sukan fita zuwa manya-manyan shaguna ko kasuwanni dake birnin NewYork wadanda suka hada da Costco wadanda suka sayarda kayaki masu yawa da kuma farashi mai sauki.

Jami’an diblomasiyyar kasar Iran dai sukan dauka hankali kafafen yada labaran Amurka a duk lokacinda suka je birnin NewYork saboda abubuwan da suke fada masu jan hankali.

Sannan jami’an tsaron Amurka da kuma wani lokaci har da yan jaridu sukan bisu zuwa kasuwannin don gani da kuma bada rahoton abubuwan da suke saya.

 A bangaren gwamnatin Amurka dai, tana cewa gwamnatin kasar ta sanyawa kasar Iran takunkuman tattalin arziki don haka jami’an diblomasiyyar kasar Iran, saboda wadan nan takunkuman basu da yencin sayan abinda suka ga dama a cikin kasar Amurka, a yayinsa mutanen kasar Iran basa samun wannan damar.

Labarin ya ce ma’aikatar harkokin wajen kasar Amurka tana kula da hatta asusun ajiyar kudin jakadun kasar Iran wadanda suke aiki a MDD.

Labarin ya kara da cewa, tun bayan kama jami’an diblomasiyyar kasar Amurka wanda daliban Jami’o’I a nan Tehran suka yi a shekara 1980 gwamnatin kasar Amurka ta takaita fitar Jami’an diblomasiyyar kasar Iran a birnin NewYork zuwa kilomita 25 kacal daga cibiyar MDD da ke birnin New York.

Labarin ya kara da cewa a wasu lokuta yansanda a birnin NewYork suke kubutar da Jami’an diblomasiyyar kasar Iran daga hannin Iraniyawa yan adawa da gwamnatin JMI idan sun shiga cikin gari don wata bukata ko don sayayya.

Sannan a baya-bayan nan gwamnatin shugaba Donal Trump ta takaita hatta abinda jami’an diblomasiyyar Iran zasu saya a birnin NewYork a lokacinda suka zama a cikinsa.

Tun shekara ta 1980 Iran da Amurka suka katse dangantakar diblomasiyya tsakaninsu, kuma amurka ta takaita fitar jami’an diblomasiyyar JMI a mdd zuwa mile 25 kacal a cikin unguwar manhatan, banda Iran gwamnatin Amurka tana dorawa jami’an diblomasiyyar kasashen Cuba, siriya a lokacin da kuma Korea ta Arewa irin wadannan dokoki.

A shekara ta 2019 gwamnatin Trump ta takaita zirga-zirgan jami’an diblomasiyya kasar Iran tsakanin cibiyar MDD a birnin NewYork, ofishinsu na jakadanci na MDD, da gidajen jakadan Iran a MDD da kuma zuwa tashar jiragen sama na JF kenedi kadai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai December 12, 2025 Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin December 12, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut December 12, 2025 Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba December 12, 2025 Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026 December 12, 2025  Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi Akan Doron Ruwa December 12, 2025 Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin