Oficin Jakadan Iran A MDD Ya Ce Babu Wani Sako Da Suka Karba Daga Shugaban Kasar Amurka
Published: 8th, March 2025 GMT
Ofishin jakadancin JMI dake MDD a birnin New York na kasar Amurka ya bada sanarwan cewa bai karbi wani sako daga shugaban kasar Amurka Donal Trump ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakoto Jaridar Axios ta Amurka na cewa Shugaban kasar Amurka ya aikawa jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Ayatullahi Khaminae wasika, inda a ciki yake kiransa zuwa tattaunawa da Amurkan a kan shirin makamashin Nukliyar kasar Iran.
Har’ila yau shugaban ya bayyana haka wa tashar talabijin ta Fox news. Iran dai ba ta son tattaunawa kai tsaye da Amurka saboda rashin gaskiya a cikin al-amuransu. Musamman shi Donal Trump, sabo da shine ya fidda kasarsa daga yarjeniyar JCPOA tun farko sannan ya dage sai ta sake tattauna da Iran sabowayar yarjeniya.
Kafin haka dai jagoran ya bayyana cewa, tattaunawa da Amurka a dai dai lokacinda take takurawa kasar da takunkuman tattalin arziki, ba zai yu ba, saboda daukan kaskanci ne wanda bai dace da JMI.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya jaddada goyon bayansa ga ra’ayin Jagoran dangane da tattaunawar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Isa Abidjan Wajen Rantsar da Shugaba Ouattara
Daga Bello Wakili
Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya isa Abidjan na kasar Côte d’Ivoire, domin wakiltar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a wajen rantsar da Shugaban Alassane Ouattara a wa’adinsa na hudu.
Za a rantsar da Shugaban ne a yau Litinin, 8 ga watan Disamban 2025, a Fadar Shugaban Kasa da ke Abidjan, wanda shugabanni daga kasashen Afrika da sauran manyan baki daga sauran kasashen duniya za su halarta.
Shugaba Ouattara ya sake lashe zabe ne a ranar 25 ga watan Oktoban 2025, inda ya sake samu wani sabon wa’adi na jagorantar kasar. Sake Rantsar da shi na nuna da ci gaban da dimokuradiyya a kasar ta Côte d’Ivoire da kuma kyakkyawar dangantakarta da Najeriya.
A cewar Fadar Shugaban Kasar, halartar Mataimakin Shugaban Kasa Shettima a taron na tabbatar da jajircewar Najeriya kan goyon bayan mulkin dimokiradiyya a yammacin Afrika. Najeriya na ci gaba da jaddada muhimmancin bin muradin jama’a da tabbatar da sauyin mulki cikin lumana a yankin.
Najeriya da Côte d’Ivoire na da kyakkyawar hulda ta aiki karkashin ECOWAS, Tarayyar Afrika, da kwamitin kasashe biyu, inda suke yin hadin gwiwa a fannoni irin su tsaro, kasuwanci, noma, yakar safarar mutane, da tattalin arzikin dijital. Dubban al’ummar ‘yan Najeriya da ke Côte d’Ivoire ma na kara zurfafa dangantakar tattalin arziki da al’adun kasashen biyu.
Ana sa ran Mataimakin Shugaban Kasa zai koma Abuja bayan kammala taron rantsarwar.