Oficin Jakadan Iran A MDD Ya Ce Babu Wani Sako Da Suka Karba Daga Shugaban Kasar Amurka
Published: 8th, March 2025 GMT
Ofishin jakadancin JMI dake MDD a birnin New York na kasar Amurka ya bada sanarwan cewa bai karbi wani sako daga shugaban kasar Amurka Donal Trump ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakoto Jaridar Axios ta Amurka na cewa Shugaban kasar Amurka ya aikawa jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Ayatullahi Khaminae wasika, inda a ciki yake kiransa zuwa tattaunawa da Amurkan a kan shirin makamashin Nukliyar kasar Iran.
Har’ila yau shugaban ya bayyana haka wa tashar talabijin ta Fox news. Iran dai ba ta son tattaunawa kai tsaye da Amurka saboda rashin gaskiya a cikin al-amuransu. Musamman shi Donal Trump, sabo da shine ya fidda kasarsa daga yarjeniyar JCPOA tun farko sannan ya dage sai ta sake tattauna da Iran sabowayar yarjeniya.
Kafin haka dai jagoran ya bayyana cewa, tattaunawa da Amurka a dai dai lokacinda take takurawa kasar da takunkuman tattalin arziki, ba zai yu ba, saboda daukan kaskanci ne wanda bai dace da JMI.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya jaddada goyon bayansa ga ra’ayin Jagoran dangane da tattaunawar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
Rahotannin da suke fitowa daga kasar Yemen na cewa katafaren jirgin ruwa mai daukar jiragen saman yaki malakar klasarAmurka wato USS Harry Truman zai fice daga tekun red sea da nan kusa saboda makaman kasar Yemen da suka fada mata.
Tashar talabijin ta Almasirah ta kasar Yemen ta nakalto wani jami’in ma’aikatar tsaron kasar wanda baya son a bayyana sunansa yana cewa, saboda yawan hare haren da sojojin Yemen suka kaiwa jirgin, wadanda suka hada da amfani da makamai masu linzami samfurin Crusse da kuma Balistic, har ila yau da jiragen yaki masu kunan bakin waken da suka fada a kansa. A yanzun ya zama dole jirgin ya fice daga tekun.
Tun cikin watan Maris da ya gabata ne gwamnatin shugaba Trump ta fara kaiwa kasar yemen hare-hare da jiragen sama wadanda suke tashi daga sansanin jiragen yaki da ke kan wannan jirgin. Saboda tilastawa kasar Yemen dakatar da kai hare-hare a kan HKI, don ta kawo karshen tallafawa Falasdinawa a Gaza.
Amma ya zuwa yanzu hare-haren na Amurka sun kasa kaiwa ga bukata, majiyar gwamnatin kasar ta yemen ta ce hare-haren Amurka a kasar ba zasu sa ta dakatar da tallafawa Falasdinawa, da kuma hanata kai hare hare kan jiragen kasuwanci na HKI masu wucewa ta tekun red sea ba.
A wani labarin kuma hare haren na sojojin yemen sun sa wani jiegin yakin Amurka samfurin F-18 ya fada cikin ruwa a tekun na Red Sea a kokarin kaucewa makaman sojojin Yemen.