Aminiya:
2025-11-07@14:45:20 GMT

WHO za ta bai wa Nijeriya magungunan cutar kuturta

Published: 8th, March 2025 GMT

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za ta aika da magungunan cutar kuturta zuwa Nijeriya a ƙarshen makon nan.

Wannan dai na zuwa ne bayan jinkirin da aka samu na gwaje-gwajen da hukumar ke gudanarwa, lamarin da ya jawo dubban masu fama da cutar ciki har da yara ba su samu magungunan da suka kamata na kare cutar ba.

Mun kama ’yan bindiga da suka yi kutse a Kano — ’Yan sanda NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya

Kakakin hukumar ta WHO ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters cewar, an samu ƙarancin maganin cutar ta kuturta a Nijeriya.

Ya ce hukumar ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta miƙa buƙatar ganin an samu izinin shigar da maganin cikin ƙasar akan lokaci, kuma a watan Janairu aka amince da hakan.

Nijeriya wadda ita ce ƙasar Afirka da ta fi yawan jama’a na bayar da rahoton samun aƙalla mutum 1,000 da cutar kuturta a duk shekara, wadda cuta ce da ke kama fatar jiki da jijiyoyi da idanu.

Ana iya magance cutar bayan shan magani na wani lokaci, amma idan ba a shan magani, cutar na ƙaruwa, idan take jawo gyambo da kuma nakasa kamar makanta da shanyewar rabin jiki.

Haka kuma, masu fama da cutar na fuskantar hantara da tsangwama a cikin al’umma.

Sai dai magungunan da Nijeriya take da su na cutar sun ƙare a farkon shekarar 2024 sakamakon jinkirin da aka samu na sabbin dokokin cikin gida da aka samar na gwaje-gwaje kan magungunan da ake shigar da su cikin ƙasar.

Jinkirin wanda ya jawo wahalhalu a Nijeriya, misali ɗaya ne daga ake samu a tsarin duniya wanda ke faruwa a ƙasashe da dama waɗanda suka haɗa da Indiya da Brazil da Indonesia a ‘yan shekarun nan, kamar yadda wakili na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya kan cutar kuturta ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Ƙididdigar WHO ta nuna cewa Nijeriya na ɗaya daga cikin ƙasashe 12 da ke bayar da rahoton kamuwa da cutar inda ake samun tsakanin mutum 1,000 zuwa 10,000 a duk shekara masu kamuwa cutar, bayan Brazil, Indiya da Indonesia.

Kowace ƙasa tana buƙatar allurai na kuturta, wanda magani ne na kafso da ake amfani da shi na tsawon watanni 12, daga WHO kowace shekara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya cutar kuturta

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Annabi Ibrahim ne ya fara kafa massallaci ya fara tsaida sallah, wadannan salloli na Ikamu da muke yi Annabi Ibrahim ya fara, Annabi Ibrahim ya fara canza a yi layya dabba maimakon dan Adam, saboda darajar da dan Adam yake da ita wajen Allah. Ya kawo tsarin a bar layya da mutane a yi da dabbobi da abubuwa da yawa, sai dai wadannan malamai na wannan lokaci ba su yarda wani ya yi tunanin wani ilmi a waje ba, saboda suna tsoron kar ya yi wani tunani da ya fi nasu, don haka jama’a kar mu ji tsoron wani ilimi, babu wani ilimi da Annabi bai zo da shi ba, amma har yau wanda ba su san ilimin ba suna tsoron wanda zai yi tunani a gaba, saboda duk wanda ya kawo wani ilimi sai ka ji an ce Zindiki ne, sai a so a halaka shi ma idan ba a yi wasa ba. Toh abin da ya dinga faruwa kenan har Allah Ya kawo falasfawa na Greeks Socrate, wasu sun ce Annabi ne, suka zo suka canza ilimi shi kan shi wannan Socrate din kashe shi aka yi da aka ce ko ya ce bai yarda da wannan ilimi ba, ko ya sha dafi shi kuma ya ce Allah ba zai ba shi ilmi ba, don haka gwara ya sha dafi ya mutu ya yarda ya sha, ga shi su wanda suka kashe shi ba sunansu shi kuwa har yau sunansa a duniyar ilimi ba zai bace ba. Toh Allah kuma Ya kawo juyin juya hali daga karni na 1800 har ya zuwa 1900 ilimin ya soma yalwata da aka fara rubuta shi, wasu na cewa ba mahaukaci sai wanda ya ba da aron littafi, ba wanda ya fi shi hauka sai wanda ya dawo da shi, wannan a lokacin da ake rubuta littafi da hannu kenan amma yanzu ya kare, an ce Shehu ya zo gidan daya daga cikin shehunnanmu yana duba library sai ya ga wani littafi sai ya ce ka ga wannan littafi na neme shi ban samu ba, ba ni aro sai ya ce Shehu na ba ka aro dauki, sai Shehu ya ce masu hikima sun ce babu mahaukaci sai wanda ya ba da aron littafi, ba wanda ya fi hauka sai wanda ya dawo da littafi, ya ce ni dai ba zan zama mahaukaci ba, sai Shehu ya yi masa wasa.

To da aka soma rubutun, China kamar su suka soma, to da buga littafi ilimi ya soma ya]uwa zuwa ga jama’a, ilimi ya fito daga dakin bauta, ya fito daga masarautar sarakuna ya shiga gidan kowa, a da kuwa yana gidan sarakuna ne kawai, ilimi ya soma yaduwa har Allah ya kawo Rediy,o tana daga cikin abin da ya yada ilimi, ta yi hobbasa wajen wayar da kan komai, dan haka a kula da rediyo yana da matukar kyau saboda galibin mutane rediyon nan ita ce hanyar daukar maganarsu, Allah ya saka wa Shehu Ibrahim Inyass (RA) da alkhairi, ya sha wahala wajen sa karatun Kurani a ciki, har Allah ya kawo talabijin, har “cable” din nan ta zo, yanzu fa za ka iya ganin duniya a cikin abu, karshen wayewa, karshen ci gaba a yanzu kuma wayar salula, wadannan wayoyi da suke hannunmu sun sa a yanzu babu jahili sai dai dakiki wanda ya ki sani da gangan, amma wayar nan babbar farfesa ce ta kowane karni, idan fannin jinya ne za ta fada ma har abin da hankalinka ba zai taba kawowa ba, haka a fannin alheri, idan fannin tarihi ne za ta kai ka har inda kudinka ba zai iya kai ka ba. Alhamdu Lillah, mun gode Allah.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Dausayin Musulunci Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya October 17, 2025 Dausayin Musulunci Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2) October 10, 2025 Dausayin Musulunci Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi October 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • Likitoci sun wayar da kan mata kan cutar Sankara a Gombe
  • Matan 500 Za Su Amfana da Gwajin Cutuka Kyauta a Jihar Gombe
  • Iravani: Kalaman Trump barazana ce ga zaman lafiyar duniya
  • Khatibzadeh: Shirin Nukiliya na Iran ya fi bayyana a duniya
  • Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar