Aminiya:
2025-12-09@11:50:00 GMT

WHO za ta bai wa Nijeriya magungunan cutar kuturta

Published: 8th, March 2025 GMT

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za ta aika da magungunan cutar kuturta zuwa Nijeriya a ƙarshen makon nan.

Wannan dai na zuwa ne bayan jinkirin da aka samu na gwaje-gwajen da hukumar ke gudanarwa, lamarin da ya jawo dubban masu fama da cutar ciki har da yara ba su samu magungunan da suka kamata na kare cutar ba.

Mun kama ’yan bindiga da suka yi kutse a Kano — ’Yan sanda NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya

Kakakin hukumar ta WHO ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters cewar, an samu ƙarancin maganin cutar ta kuturta a Nijeriya.

Ya ce hukumar ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta miƙa buƙatar ganin an samu izinin shigar da maganin cikin ƙasar akan lokaci, kuma a watan Janairu aka amince da hakan.

Nijeriya wadda ita ce ƙasar Afirka da ta fi yawan jama’a na bayar da rahoton samun aƙalla mutum 1,000 da cutar kuturta a duk shekara, wadda cuta ce da ke kama fatar jiki da jijiyoyi da idanu.

Ana iya magance cutar bayan shan magani na wani lokaci, amma idan ba a shan magani, cutar na ƙaruwa, idan take jawo gyambo da kuma nakasa kamar makanta da shanyewar rabin jiki.

Haka kuma, masu fama da cutar na fuskantar hantara da tsangwama a cikin al’umma.

Sai dai magungunan da Nijeriya take da su na cutar sun ƙare a farkon shekarar 2024 sakamakon jinkirin da aka samu na sabbin dokokin cikin gida da aka samar na gwaje-gwaje kan magungunan da ake shigar da su cikin ƙasar.

Jinkirin wanda ya jawo wahalhalu a Nijeriya, misali ɗaya ne daga ake samu a tsarin duniya wanda ke faruwa a ƙasashe da dama waɗanda suka haɗa da Indiya da Brazil da Indonesia a ‘yan shekarun nan, kamar yadda wakili na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya kan cutar kuturta ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Ƙididdigar WHO ta nuna cewa Nijeriya na ɗaya daga cikin ƙasashe 12 da ke bayar da rahoton kamuwa da cutar inda ake samun tsakanin mutum 1,000 zuwa 10,000 a duk shekara masu kamuwa cutar, bayan Brazil, Indiya da Indonesia.

Kowace ƙasa tana buƙatar allurai na kuturta, wanda magani ne na kafso da ake amfani da shi na tsawon watanni 12, daga WHO kowace shekara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya cutar kuturta

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167

167-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma, ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtada Muttari, ko kuma cikin littafin Mathnawa na Maulana Jalaluddeen Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin wannan Shirin.

/////….Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-Hassan al-Mujtaba(a) dan Fatimah (s) diyar manzon Allah (s)  da muke kawo maku. A cikin shirimmu da ya gabata munyi maganar

Dalilin da suka sa sojojin Imam Al-Hassan (a) suka kasa yakar sojojin Mu’awiya dan Abusufyan. Daga ciki mun bayyana cewa, kha’inci da son duniya a cikin sojojin Imam (a) ya ka suna son kama shi su mikawa mu’awiya don su su Aminta su kuma samu daukaka a wajensa.

Kamar yadda dan dan’uwan Sa’adu dan Mas’ud Athaqafi ya zo yana kudaitar da Amminsa ya kama Imam Al-Hassan (a) wanda yake jinya a gidansa ya mikawa Mu’awiya saboda ya sami aminci da da kuma daukaka. Munji da Sa’adu Athaqafi ya la’anesu ya kuma nisantar da shi, yana kuma neman tsarin Allah daga sharrinsa.

Daga ciki mun ambaci yadda Mu’awiya ya yada akidun karya dangane da banu Umayya a Sham, saboda jahilcinsu. Ya kirkoro hadidan karya ya jinginawa manzon Allah (s) tare da taimakon wasu sahabban manzon Allah wadanda suke tare da shi. Daga cikin wadan nan hadisan da suka kirkiro har da cewa Banu Umayya sune dangin manzon Allah (s) wadanda suka cancanci gadonsa.

Wannan akidar ta wanzu a kasar Sham har zuwa lokacinda Abul Abbas wanda aka fi saninsa da Saffah, sarki na farko daga cikin sarakunan Abbasiyawa ya kwace kasar Sham, sannan shuwagabannin manya manyan kungiyoyi da kabilu suka zo masa, suna rantsewa da Allah kan cewa basu taba sanin cewa manzon Allah (s) yana da dangi wadanda suka cancanci gadonsa ba in banda banu umayya.

Dangane da wannan Ibrahim dan Muhajir Al-Bajali mutumin Kufa yayi wata kisida yana fada a cikinta, yana cewa  

Ya ku mutane ! Ku Saurara, Zan baku labarin * Abin mamaki, wanda yafi ban mamaki .

Abin mamaki daga Abdushamsi (banu umayya), Lalle su* Sun budewa mutane Kofofin karya.

A riyawarsu, Sun gaji Ahmadu (manzon Allah(a))* Amma banda amminsa Abbas dan Abdul Muttalib.

Sun yi karya, na rantse da Allah, bamu sans hi ba* Kan cewa ba wanda zai sami gado sai sai wanda yake kusa.

Malaman tarihi sun bayyana cewa, mutanen sham- saboda wadan nan hadisan karya, wadanda Mu’awiya da abokan aikinsa suka yada a cikinsu, suna ganin sarakunan banu umayya sarakunan addinin musulunci ci, kuma Mu’awiya khalifan Allah ne a bayan kasa. Haka ma dansa Yaziz (la’anenen wanda ya kashi jikan manzon Allah (s) wato Imam Al-Hussain (a), to shi ma khalifan Allah ne a bayan kasa).

Wadan nan al-amura suka sa mutanen sham suke matukar biyayya ga Mu’awiya dan Abusufyan, haka ma sauran sarakunan banu Umayya da su zo bayansa, har saida al-amura suka bayyana bayan faduwar daularsu kimani shekaru 80 bayan da mu’awiya ya kwace iko daga hannun Imam Al-hassan (a).

Sannan mu’awiya ya yi amfani da damar da ya samu na biyayyar da mutanen sham suke masa, ya nesantar da su daga addinin musulunci na gaskiya, da gangan yake sabawa sharia ya kuma sabawa sunnar manzon Allah (s).

Sannan saboda irin biyayyar da mutanen sham sukewa Mu’awiya, Amirul muminina Aliyu dan Abitalib (a) yayi gurin, ina ma yana da Mabiya, wadanba basa sabawa umurnin shugabansu kamar yadda mutanen sham suke biyayya ga mu’awiya har yana fadawa mutanen Iraki wani lokaci, ina da za’a yi masa musayar daya daga cikinsu da mutum 10 daga cikin Irakawa. Wadanda ba abinda aka sansu da shi sai tashe tashen hankula da jayayya da shuwagabanninsu. Shugabansu ya fada su fada.

Sannan mutanen sham, kafin shigarsu addinin musulunci su kiristoci ne, karkashin daular Ruma da gabas wanda yake jagorantar yankin daga kasar Turkiya a lokacin. Don haka sun saba da gwamnatin da biyayya ga shugaba da kuma tsarin rayuwa mai nutsuwa, ba kamar larabawa kafin musulunci ba.

Don haka su mutanene masu saukin hali, amma basu da wayo ko kuma amfani da hankali a cikin al-amura don fahintar gaskiya. Danga ne da wannan malaman tarihi sun bayyana cewa, bayan yakin siffin wani mutumin Iraki ya je kasar Sham da rakuminsa, sai ya hadu da wani mutumin sham wanda yace ai rakumin nasa nasa. Ragima da shiga tsakaninsu, har suka je gaban Mu’awiya.

Mutumin sham ya kawo shaidu kimani 50 suka tabbatar da cewa rakumin na miji nasa ne, sai mu’awiya ya yanke hukunci kan cewa a mayarwa mutumin sham, rakumin.

Sai mutumin Iraki ya fadawa Mu’awiya ai wannan taguwa ce (macce ba rakumi) na mijiba!.

Amma sai mu’awiya yace masa hakunci ya rika wuce ka mayarma da damar. A lokacinda aka watse, sai mu’awiya ya aika a kira mutumin Iraki ya zo. A lokacinda ya zo, sai yace masa nawa kudin taguwarka sai ya fada, sai ya ninka masa ya kuma fada masa, idan ka je Iraki ka fadawa Aliyu dan Abitalib (a) kan cewa, na tanaji mutanen sham dubu 100 don yakarsa, ba wani daga cikinsa wanda yake iya bambata tsakanin rakumi na miji da taguwa ta mace.

Wannan ya nuna irin rashin wayewa da fahintar mutanen sham a lokacin, don haka Mu’awiya ya yi amfani da jahilcinsu ya yakar iyalan gidan manzon Allah (a) da su. Ya sauya al-amura da dama na addini, ya kuma takurawa iyalan gidan manzon Allah (a) da mabiyansu, ya sunnata kashesu da la’antarsu a kan mimbarorin musulmi na tsawon shekaru kimani 60 bayan sulhuntawa da Imam Al-Hassan kamar yadda zamu gani a nan gaba.

Don haka Mu’awiya ya barsu cikin jahilci, cikin duhu bayan duhu, suna masu dimwa a cikin al-amarinsu, baya barin wani ya zo ya farkar da su ko kuma su su je wani wuri a cikin daular musulunci inda zasu gano gaskiyan al-amari. Su gano kariyar Mu’awiya da kuma banu umayya gaba daya.

Sai kuma rarraba da hadin kai, kasar Sham bata da rarrabar kai na akidu da kuma kabilanci wanda ake da su a kasar Iraki.

Don haka su kalma guda ce ta hada su, basa da sabani a tsakaninsu, akidar Khawarijawa bata  shigo masa ba. Hakama basa da matsala tsakanin shuwagabannin kabilu da Mu’awiya. Yana bawa shuwagabannin kudaden da suka gabata don su rike masa kabilunsu. Iran wannan kabilun Iraki suke nema amma Ahlul Baiti suka bayyana hakan ya sabawa adalci. Rabon shugaban kabila shi ne rabon mabiyansa. Ba’a bashi fiye da rabonsa.

Don haka hadin kan da aka samu a cikin gida yana da cikin sirrin nasarorin da Mu’awiya ya yi ta samu a kan sojojin Imam Al-Hassan (a).

A wani bangare kuma Mu’awiya ya karfafa sojojinsa ne bayan da ya sami hadin kai a cikin gida. Ya sulhunta da daular Roma da ta rage a lokacin, ya kuma bata kudade masu yawa don kada ta tada masa yaki.

Sannan a cikin gida ya na karban haraji mai yawa a wajen mutane, yana karban zakka hatta a cikin kayakin da ba’a masu zakka.

Mun san cewa dukiyoyi iri 8 ne ake masu zakka, amma Mu’awiya yana karban zakka. Kuma yana matsawa kwarai wajen karban zakka da kuma haraji. Mu’awiya ya tilasta wa mutanen sham bada abinda ake kira da Farisanci :hadayar Niruz” wanda babu a cikin addinin musulunci.

Niruz sabuwar shekara ce ta Iraniyawa da kuma kabilun da suke yankin Asiya kamar Kurdawa da sauransi, musulunci bai san da shi ba. Ya kuma halatta wasu abubuwan da shari’a ta haramta, mai yuwa bai san shari’a ta haramta su ba, amma sau da dama da gangan yake sabawa addinin musulunci yana sani da matsayinsa.

Wani lokaci yakan halatta wani abu ko ya haram tashi da gangan don ya sabawa sharia. Da kuma kuma ya sauka abubuwan adiinin, kama daga hukunce-hukunce zuwa ibada da sauranci, kuma da gangana.

Har’ila yau Imam Al-Hassan (a) ya ki mutanen kufa ne bayan sun kashe mahaifinsa Amirul muminina (a) . Muntum wanda yake rayuwa a cikinsu, cikin talaunci, sannan yana matukan kokari wajen ganin sun rayuwa cikin jin dadi, da kuma adalci a tsakaninsu. Yana rayuwa cikinsu kamar rayuwar daya daga cikinsu. Amma sai wasu daga cikinsu suka fito suka kasheshi ba tare da yayi masu laifi ba, ba tare da dauki dukiyoyinsu, ba tare da ya tsokanesu. Wannan al-amarin ya bar tabo babba a zuciyar Imam Al-Hassan (a) kuma tun lokacin yake taka tsantsan da su. Yake kuma ganin basu cancanci su zana mataimakansa ba. Saboda laifukan da suka aikata, na kashe mahaifinsa, wasiyin kakansa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri December 7, 2025 Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21 December 7, 2025 Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166
  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno