Aminiya:
2025-12-04@09:41:43 GMT

WHO za ta bai wa Nijeriya magungunan cutar kuturta

Published: 8th, March 2025 GMT

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za ta aika da magungunan cutar kuturta zuwa Nijeriya a ƙarshen makon nan.

Wannan dai na zuwa ne bayan jinkirin da aka samu na gwaje-gwajen da hukumar ke gudanarwa, lamarin da ya jawo dubban masu fama da cutar ciki har da yara ba su samu magungunan da suka kamata na kare cutar ba.

Mun kama ’yan bindiga da suka yi kutse a Kano — ’Yan sanda NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya

Kakakin hukumar ta WHO ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters cewar, an samu ƙarancin maganin cutar ta kuturta a Nijeriya.

Ya ce hukumar ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta miƙa buƙatar ganin an samu izinin shigar da maganin cikin ƙasar akan lokaci, kuma a watan Janairu aka amince da hakan.

Nijeriya wadda ita ce ƙasar Afirka da ta fi yawan jama’a na bayar da rahoton samun aƙalla mutum 1,000 da cutar kuturta a duk shekara, wadda cuta ce da ke kama fatar jiki da jijiyoyi da idanu.

Ana iya magance cutar bayan shan magani na wani lokaci, amma idan ba a shan magani, cutar na ƙaruwa, idan take jawo gyambo da kuma nakasa kamar makanta da shanyewar rabin jiki.

Haka kuma, masu fama da cutar na fuskantar hantara da tsangwama a cikin al’umma.

Sai dai magungunan da Nijeriya take da su na cutar sun ƙare a farkon shekarar 2024 sakamakon jinkirin da aka samu na sabbin dokokin cikin gida da aka samar na gwaje-gwaje kan magungunan da ake shigar da su cikin ƙasar.

Jinkirin wanda ya jawo wahalhalu a Nijeriya, misali ɗaya ne daga ake samu a tsarin duniya wanda ke faruwa a ƙasashe da dama waɗanda suka haɗa da Indiya da Brazil da Indonesia a ‘yan shekarun nan, kamar yadda wakili na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya kan cutar kuturta ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Ƙididdigar WHO ta nuna cewa Nijeriya na ɗaya daga cikin ƙasashe 12 da ke bayar da rahoton kamuwa da cutar inda ake samun tsakanin mutum 1,000 zuwa 10,000 a duk shekara masu kamuwa cutar, bayan Brazil, Indiya da Indonesia.

Kowace ƙasa tana buƙatar allurai na kuturta, wanda magani ne na kafso da ake amfani da shi na tsawon watanni 12, daga WHO kowace shekara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya cutar kuturta

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa

An kashe wani ɗan sanda a wani mummunan hari da ’yan bindiga suka kai gidan Babban Jami’in Ɗan Sanda (DPO) mai kula Babba Ofishin ’Yan Sanda da ke Aujara a Ƙaramar Hukumar Jahun ta a Jihar Jigawa.  

Da misalin ƙarfe 4:00 na asuba, ranar 25 ga Nuwamba, 2025, ne wasu ’yan bindiga suka kai farmaki gidan DPO na Babban Ofishin ’Yan Sandan.

Sanarwar rundunar ’yan sanda ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa jami’an tsaro da ke gadin gidan sun yi ƙoƙarin dakile harin, inda aka samu musayar wuta.

A yayin arangamar, biyu daga cikin jami’an sun samu munanan raunuka, aka garzaya da su asibiti domin samun kulawa.

Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus An kama ’yan bindiga 4 a Kano

Washegari, ɗaya daga cikin waɗanda suka ji rauni ya rasu a sakamakon tsananin raunukan da ya samu.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Jigawa, Ɗahiru Muhammad, ya yi ta’aziyya ga iyalan mamacin da abokan aikinsa, yana mai tabbatar da cewa rundunar ta fara bincike na musamman domin kamo waɗanda suka aikata wannan ta’addanci.

Bayan harin, rundunar ta ƙara tsaurara matakan tsaro ta hanyar yawaita sintiri da sanya ido a Aujara da maƙwabtan garuruwan domin hana sake faruwar irin wannan barazana.

Kakakin rundunar, SP Shiisu Lawan Adam, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da ci gaba da ba da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin taimaka wa binciken da ake yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio
  • Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • Tinubu ya naɗa Janar CG Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030