Za a kashe Naira biliyan 4.8 wajen yaƙi da cutar HIV a Nijeriya — Ministan Lafiya
Published: 4th, February 2025 GMT
Majalisar Zartarwa ta ware naira biliyan 4.8 domin yaƙi da yaɗuwar cutar HIV a Nijeriya.
Wannan na daga cikin matsayar da aka cimma a taron Majalisar Zartarwa da ya gudana a ranar Litinin kamar yadda Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate ya tabbatar.
Ma’auratan da aurensu ya mutu sau 12 a shekara 43 Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a AdamawaMinistan ya ce wannan yana daga cikin manufofin gwamnatin na inganta kiwon lafiya a matakin farko.
A cewarsa, an tsara kashe kuɗaɗen ne a fannin ɗaukar ma’aikatan lafiya da ba su horo domin samun ƙwarewa da kuma tabbatar da an bayar da kulawar da ta dace domin hana yaɗuwar cutar HIV a sassan ƙasar.
A yayin da abokan hulɗa daban-daban daga ƙetare sun taka rawar gani wajen yaƙi fa cutar, Farfesa Pate ya ce za ta ƙara zage damtse wajen ɗaukar matakan ceto rayuwar mutanen da ke ɗauke da cutar ta HIV.
A bayan nan dai an riƙa bayyana damuwa game da sabbin tsare-tsaren da gwamnatin shugaban Amurka, Donald Trump ta ɓullo da su, musamman a fannin bayar da tallafi, inda ake tunanin za su iya shafar tallafi ga yaƙi da cutar HIV a ƙasashe masu tasowa.
Amma a ranar Asabar gwamnatin Amurkan ta sanar da ware sabon ƙunshin tallafin yaƙi da cutar ta HIV.
Alƙalumman da hukumar hana yaɗuwar cutar HIV a Nijeriya ta fitar, sun ce ƙasar ce ta fi kowacce yawan masu cutar a yammacin Afirka, kuma an daɗe ana samun kiraye-kiraye daga faɗin duniya na ganin Najeriya ta zage damtse wajen yaƙi da yaɗuwar cutar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cutar HIV a
এছাড়াও পড়ুন:
Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa da ita ba.
A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.”
Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”
Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.
Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.
A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.