Majalisar Zartarwa ta ware naira biliyan 4.8 domin yaƙi da yaɗuwar cutar HIV a Nijeriya.

Wannan na daga cikin matsayar da aka cimma a taron Majalisar Zartarwa da ya gudana a ranar Litinin kamar yadda Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate ya tabbatar.

Ma’auratan da aurensu ya mutu sau 12 a shekara 43 Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa

Ministan ya ce wannan yana daga cikin manufofin gwamnatin na inganta kiwon lafiya a matakin farko.

A cewarsa, an tsara kashe kuɗaɗen ne a fannin ɗaukar ma’aikatan lafiya da ba su horo domin samun ƙwarewa da kuma tabbatar da an bayar da kulawar da ta dace domin hana yaɗuwar cutar HIV a sassan ƙasar.

A yayin da abokan hulɗa daban-daban daga ƙetare sun taka rawar gani wajen yaƙi fa cutar, Farfesa Pate ya ce za ta ƙara zage damtse wajen ɗaukar matakan ceto rayuwar mutanen da ke ɗauke da cutar ta HIV.

A bayan nan dai an riƙa bayyana damuwa game da sabbin tsare-tsaren da gwamnatin shugaban Amurka, Donald Trump ta ɓullo da su, musamman a fannin bayar da tallafi, inda ake tunanin za su iya shafar tallafi ga yaƙi da cutar HIV a ƙasashe masu tasowa.

Amma a ranar Asabar gwamnatin Amurkan ta sanar da ware sabon ƙunshin tallafin yaƙi da cutar ta HIV.

Alƙalumman da hukumar hana yaɗuwar cutar HIV a Nijeriya ta fitar, sun ce ƙasar ce ta fi kowacce yawan masu cutar a yammacin Afirka, kuma an daɗe ana samun kiraye-kiraye daga faɗin duniya na ganin Najeriya ta zage damtse wajen yaƙi da yaɗuwar cutar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cutar HIV a

এছাড়াও পড়ুন:

Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura

Amincewar Gwamnatin Tarayya da kashe Naira biliyan 712 biliyan don gyaran Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed da ke Legas ya haifar da ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya.

Wannan gagarumin kashe kuɗi, da Majalisar Zartarwa ta Kasa ta amince da shi a ranar Alhamis da ta gabata, ya sanya masana harkar jiragen sama, ’yan adawa, da kuma jama’ar ƙasa yin tambayoyi game da buƙatarsa, tsadarsa, da kuma inda za a samo kuɗin.

Masu suka suna nuna yadda kuɗin ya yi yawa, har ya ninka kuɗin da aka ware wa Ma’aikatar Sufurin Jiragen Sama a kasafin kuɗin 2025 har sau goma. Hasali ma aikin ba ya cikin kasafin 2025.

Wannan ya sa wasu ke kiran aikin a matsayin “almubazaranci,” musamman ganin halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki.

Wani babban abin da ke haifar da surutan shi ne tsarin samo kuɗin. Gwamnati ta sanar da cewa za a samu kuɗin ne daga Asusun Ayyukan Raya Kasa na Renewed Hope Infrastructure Development Fund.

Amma jam’iyyun adawa, ciki har da ADC, sun ce Majalisar Dokoki ta Ƙasa ba ta amince da wannan kashe kuɗi ba, don haka suka kira shi “kashe kuɗi ba tare da kasafi ba.”

Yunkurinmu na jin ta bakin kakakin Majalisar Dattawa da ta Wakilai ya ci tura, wanda hakan ya ƙara ɓoye sirrin aikin.

Gyaran tashar jirgin ta Legas, wanda aka ba kamfanin gine-gine na CCECC kwangilar, zai haɗa da kwance ginin gaba ɗaya sannan a sake gina sabbin na’urorin zamani da tsarin lantarki da ruwa.

Wasu ayyukan sun haɗa da kwangilar Naira biliyan 44.13 na sabbin fitilun titin jirgin, Naira biliyan 24.27 na faɗaɗa wuraren ajiye jiragen sama, da kuma shingen tsaro . mai ɗauke da na’urorin zamani na Naira biliyan 49.9.

Jimillar kuɗin ta kuma haɗa da irin waɗannan gyare-gyaren a filayen jiragen sama na Kano da Fatakwal.

Wannan ba shi ne yunkurin farko na gyara filin jirgin na Legas ba. Tsohuwar gwamnatin Marigayi Muhammadu Buhari ta buɗe wani sabon tashar jirgin a shekarar 2022, wanda aka gina da kuɗin rancen dala miliyan 500 daga ƙasar China.

Amma wannan tashar ta fuskanci matsaloli masu yawa, inda kamfanonin jiragen sama da yawa suka ƙi amfani da ita saboda ƙarancin wurin ajiye manyan jirage.

Sabuwar tashar ta kasance ba a amfani da ita na tsawon fiye da shekara guda, inda yawancin kamfanonin jiragen sama na duniya ke ci gaba da amfani da tsohuwar tashar da yanzu aka shirya wa gagarumin gyara.

Yayin da gwamnati ke ci gaba da shirin ta, cece-kucen ya ƙara ta’azzara.

Tare da rashin samun cikakken bayani daga hukumomin Majalisar Dokoki da kuma tarihin ayyukan filayen jiragen sama da suka tsaya, jama’a na ci gaba da shakkar gaskiyar kuɗin da za a kashe da kuma nasarar da za a samu a wannan sabon aiki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi  Na Tabbatar Da Karfi Da Ci gaba
  • Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
  • Gwamna AbdulRazaq Ya Amince Da Naira Biliyan 20 Don Gyaran Gine-ginen Makarantu A Kwara
  • Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Wani Dan Siyasa Ya Shirya Addu’o’i Na Musamman Domin Samun Zaman Lafiya A Zamfara
  • Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura
  • Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino