Leadership News Hausa:
2025-05-01@00:23:13 GMT

NDLEA Ta Kama Tsoho Mai Shekaru 75 Da Dillancin Ƙwayoyi A Kano

Published: 4th, February 2025 GMT

NDLEA Ta Kama Tsoho Mai Shekaru 75 Da Dillancin Ƙwayoyi A Kano

Hukumar yaƙi a sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA) reshen Jihar Kano ta kama wani tsoho mai shekaru 75, Nuhu Baba, bisa zargin sayar da miyagun ƙwayoyi ga matasa.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Sadiq Muhammad-Maigatari, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata a Kano, inda ya ce wanda ake zargi ya amsa laifinsa, yana mai cewa ya rungumi sana’ar ne domin rayuwa a unguwarsu da ke ƙaramar hukumar Gezawa.

NDLEA Ta Cafke Masu Ta’ammali Da Ƙwayoyi 18,500 A 1 – Marwa NDLEA Ta Gargadi Iyaye Kan Bayyanar Alawar Ƙwaya A Kano

Hukumar ta kwato nau’ikan kwayoyi daban-daban, ciki har da Tramadol, wiwi, Diazepam, Exol-5 da man shafawa mai sa maye. Kakakin hukumar ya ce Kwamandan NDLEA na Kano, Abubakar Idris-Ahmad, ya jaddada ƙudurin hukumar na yaƙi da sha da fataucin ƙwayoyi tare da buƙatar hadin gwuiwar al’umma domin daƙile wannan matsala.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA

Shugaban hukumar makamshin Nujkliya ta MDD ya zanda da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi kan al-amuran da suka shafi shirin nukliyar kasar Iran da kuma tattaunawar da ake gudana tsakanin ta da Amurka.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a tattaunawa ta wayar tarho tsakanin jami’an guda biyu a jiya Lahadi, Grossi shugaban IAEA ya bayyana cewa ya ji dadin yadda JMI ta zabi tattaunawa da AMurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya. Ya kuma bayyana cewa hukumarsa a shirye take ta gabatar da duk wani taimakon da JMI take bukata a yayin tattaunawar.

A nashi bangaren Abbas Araqchi ya bayyana cewa kasar Iran a shirye take ta bada hadin kai ga hukumar ta IAEA kamar yadda yarjeniyar NPT take bukata da kuma dokokin kasa da kasa.

Abbas ya fada masa inda aka kai ya zuwa yanzu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, a biranen Mascat na kasar Omman da kuma Roma na kasar Italiya.

Ya zuwa yanzu dai kasashen biyu sun gudanar da taro har sau uku dangane da shirin Nukliyar kasar ta Iran, kuma bangarorin biyu sun bayyana amincewarsu da yadda tattaunawar take tafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara