HKI tana son aiwatar da wani shiri don kara yawan yahudawa a kasar, a dai dai lokacinda take fama da karancin yahudawa a kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta ce a baya dai gwamnatin yahudawan suna son kara yawan  yahudawa musamman a yankin yamma da kogin Jordan, ammam har yanzun shirin baya tafiyar kamar yadda take so.

Labarin ya kara da cewa yawan Palasdinawa a cikin kasar Palasdinu da aka mamaye wata barazana ce babba ga gwamnatin kasar.

Banda haka a cikin yakin watanni 15 da ta fafata da Mutanen yankin Gaza, wasu yahudawa sun fice daga kasar kuma da dama daga cikinsu sun sha alwashin ba za su sake dawowa kasarba. Wasu kuma sun kai ga kona passpot dinsu na HKI tare da nufin ba zasu sake dawowa HKI ba har abada.

Har’ila yau wasu masana sun bayyana cewa duk kokarin da gwamnatin HKI za ta yi na gamsar da yahudawa da ga wasu kasashen duniya dawowa HKI da wuya su sami nasara, musamman ganin a halin yanzu ta shiga cikin yaki wanda ba wanda ya san karshensa ba.

Labarin yace kashi 53% na yahudawan da suke zaune a kasar Falasdinu da aka mamaye sun fito ne daga gabas ta tsakiya da kuma arewacin kasar Amurka. Sanna kashi 36% na yahudawan sahyoniya a HKI sun kaurane daga wasu kasashe.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rikici Tsakanin Faransa Da Aljeriya Ya Shiga Wani Sabon Salo Na Koran ‘Yan Kasashen Juna Daga Kasashensu

An samu bullar rikicin da ba a taba ganin irinsa ba a dangantaka tsakanin Aljeriya da Faransa

Rikicin ma’aikatan harkokin diflomasiyya tsakanin Aljeriya da Faransa ya dawo kan gaba a fagen dakaddamar da ke tsakaninsu.

Rikici dai na kara kamari ne tsakanin Aljeriya da Faransa, tun daga rikicin korar ‘yan kasar Aljeriya daga Faransa zuwa rikicin korar ma’aikatan diflomasiyyar Faransa daga Aljeriya. Kasashen biyu sun tsaya a gaban nauyin tarihin mulkin mallaka ba tare da shawo kan shi ba. Aljeriya ta gayyaci mukaddashin jakadan Faransa domin sanar da shi aniyarta ta korar karin jami’an Faransa da ke aikin taimakon wucin gadi daga kasarta.

Wannan kiran ya biyo bayan maimaita cin zarafi mai tsanani da bangaren Faransa ya yi ne, yana wakiltar keta doka da aka kafa da kuma keta tsarin al’ada don nada ma’aikata a ofisoshin diflomasiyya da na ofishin jakadancin Faransa da aka amince da su a Aljeriya.

Akalla ma’aikatan Faransa 15 ne aka nada don gudanar da ayyukan diflomasiyya ko na ofishin jakadancin a kasar Aljeriya, ba tare da bin ka’idojin da suka dace ba, gami da sanarwa a hukumance ko kuma ba da izini, kamar yadda ka’idoji da yarjejeniyoyin kasa da kasa suka bukata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri
  • MDD: Yunwa Ta Kara Tsanani A Duniya Daga Shekarar 2024
  • Senegal ta karbi wani sansaninta na uku daga hannun Faransa
  • Jagora: Jawaban Trump A Ziyar Da Ya Kai Wasu Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Abin Kunya Ne Gare Shi Ga Kuma Amurkawa
  • Shuwagabanin Larabawa Sun Yi Alkawalin Sake Gina Gaza, Suna Kuma Kokarin Tsagaita Wuta Da Farko
  • Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada
  • Tsohon Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Ya Bukaci A Tsige Netanyahu Daga Kan Fira Ministan Isra’ila
  • Rikici Tsakanin Faransa Da Aljeriya Ya Shiga Wani Sabon Salo Na Koran ‘Yan Kasashen Juna Daga Kasashensu
  • Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya
  • Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba