Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
Published: 13th, October 2025 GMT
An kammala kada ƙuri’a da yammacin Lahadi a zaɓen shugaban ƙasa na Kamaru, inda shugaban ƙasa mai shekaru 92, Paul Biya — wanda shi ne tsohon shugaban ƙasa mafi tsufa a duniya — yake neman wa’adi na takwas a mulki.
Biya, wanda ya shafe shekaru 43 yana mulkin ƙasar, ya fafata da ’yan takara 11, ciki har da tsoffin muƙarrabansa.
Ɗaya daga cikinsu shi ne Issa Tchiroma Bakary, tsohon ministan ma’aikata wanda ya yi murabus daga gwamnati a watan Yuni bayan fiye da shekaru 20 yana aiki tare da Biya.
Bakary, mai shekaru 79, ya zama babban abokin hamayyar Biya bayan Kotun Tsarin Mulki ta ƙi amincewa da takarar fitaccen ɗan adawa Maurice Kamto — matakin da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam ciki har da Human Rights Watch suke cewa ya rage sahihancin tsarin zaɓen.
Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku Yajin Aikin ASUU: Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya Matasa da dogon mulkiKamaru na da masu kaɗa ƙuri’a kusan miliyan takwas, yawansu matasa da ba su taɓa sanin wani shugaban ƙasa ba sai Biya, tun da ya hau mulki a 1982.
A cikin shekaru 20 da suka gabata, Biya yakan lashe zaɓe da sama da kashi 70 na ƙuri’u.
Bayan ya jefa ƙuri’arsa a kusa da fadar gwamnati a Yaounde, Biya ya ce wa manema labarai: “Ba a san komai ba tukuna. Mu jira mu ga wanda aka zaɓa.”
Wani jami’in hukumar zaɓe ta ƙasa, Jean-Alain Andzongo, ya shaida wa AFP cewa an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da tsari a babban birnin.
Mai sharhi kan harkokin siyasa, Stephane Akoa, ya ce duk da cewa jam’iyyar mai mulki na da damar ganin ta sami nasara, wannan yaƙin neman ya kasance “mai ɗan ɗumi fiye da yadda aka saba,” yana nuna yiwuwar “samun wasu abubuwan mamaki.”
’Yan takara da yaƙin neman zaɓeBiya bai yi fitowa sosai ba a lokacin yaƙin neman zaɓe, inda ya bayyana sau ɗaya kacal a wani babban gangami a Maroua, a yankin Arewa Mai Nisa — inda akwai masu kaɗa ƙuri’a miliyan 1.2.
Sai dai wannan yankin da aka daɗe ana ɗauka matsayin ginshikin goyon bayansa, yanzu wasu tsoffin abokansa ne ke takara da shi daga yankin.
’Yan adawa sun gudanar da gangami a sassa daban-daban na ƙasar, suna alkawarin kawo sauyi ga al’ummar Kamaru.
A yayin da Biya ya tara ’yan ɗaruruwan mutane kaɗan a gangaminsa, Bakary kuwa ya samu tarbar dubban magoya baya a yankin da ya fito, suna ɗaga tutoci masu taken “Tchiroma Mai Ceto.”
Tattalin arziki da ƙorafin jama’aDuk da albarkatun ƙasar – musamman noma da ma’adinai – Kamaru na ci gaba da fama da talauci da rashin aikin yi.
Bisa ga rahoton Bankin Duniya (2024), kusan kashi 40% na ‘yan ƙasar na rayuwa ƙasa da layin talauci, yayin da rashin aikin yi ya kai kashi 35% a manyan birane.
Jama’a na ci gaba da koka kan tsadar rayuwa, ƙarancin ruwan sha mai tsafta, rashin ingantaccen kiwon lafiya da kuma matsalolin ilimi.
Matasa da neman sauyiAkoa ya bayyana cewa matasan Kamaru na ƙaunar ganin sauyi, amma har yanzu ba su kai matakin yin zanga-zanga kamar yadda ake gani a wasu ƙasashe na Afirka da Asiya ba.
Ya ce: “Yawancin matasa sun nuna niyyar kaɗa ƙuri’a. Wannan alama ce mai kyau, amma ba ta kai matakin tayar da gagarumin yunƙuri irin na Madagascar ko Tunisia ba.”
Sauran bayanai da sakamakon zaɓeGwamnatin Kamaru ta bai wa masu lura da zaɓe kusan 55,000 — ciki har da wakilan Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) — damar sa ido kan zaɓen.
Kotun Tsarin Mulki na da wa’adin Oktoba 26 don fitar da sakamakon ƙarshe.
Sai dai wasu kafafen sada zumunta sun sanar da shirinsu na tattara sakamako da kansu — abin da gwamnati ta soki, tana zargin suna ƙoƙarin karkatar da ra’ayoyin jama’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bakary Biya Kamaru Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara
An kashe wani da ake zargin ɗan bindiga ne, yayin wani artabu da ’yan sanda da ’yan sa-kai suka yi da wasu mahara a Jihar Kwara.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Adekanbi, kusa da garin Bode Saadu.
Kotu ta sake hana PDP gudanar da babban taronta na ƙasa Mutfwang ya musanta raɗe-raɗin sauya sheƙa zuwa YPPRahotanni sun nuna cewa ’yan bindigar sun yada zango a saman wani dutse da ke kallon ƙauyen.
Suna hangar jami’an tsaro sai suka fara harbi ba ƙaƙƙautawa.
’Yan sanda da jami’an sa-kai sun yi artabu tare da tarwatsa maharan, inda wasu daga cikinsu suka tsere da raunin harbin bindiga.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Adetoun Ejire Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a.
Bayan an artabun, jami’an tsaro sun duba yankin, inda suka samu gawar mutum ɗaya da ake zargin ɗan bindiga ne.
Haka kuma an gano bindiga ƙirar AK-49 da harsasai 32 a wajen.
SP Adetoun, ta ce wannan aikin wani muhimmin ci gaba ne a ƙoƙarin da rundunar ke yi wajen kawar da masu aikata laifi a jihar.
Ta kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa yaƙi da laifuka.