Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole
Published: 10th, October 2025 GMT
“Ta yaya Jonathan zai zama barazana? Mun doke shi a baya lokacin da PDP take kan mulki.
“Idan mutum yana ganin cewa PDP ita ce kololuwar jam’iyya a Nijeriya, kuma ya sha kaye a lokacin da yake ganiyarsa, ina ganin sai makiyinsa ne kawai zai tilasta masa ya kara tsayawa takara a zaben 2027,” in ji shi.
Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa ya ce a yanzu haka Jonathan ya kasance dan siyasa mai daraja, yana mai cewa komawa fagen siyasa na iya rage masa kima da kuma zubar masa da darajar da yake da shi a idon duniya.
Ya jaddada cewa Jonathan ya samu damar nuna cewa mulki bai tsole masa ido ba, domin haka ne ya samu daraja a cikin harkokin siyasar Nijeriya, sake dawowa takara zai zubar masa da daraja.
Oshiomhole ya jaddada cewa, “Da zan iya ba shi shawara, zan cewa, ka ci gaba da rike matsayin. Ka yi mulki har na tsawon shekaru takwas, ba lallai ba ne ka sake yin mulki na shekara tara.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
Rahotanni na cewa ’yan bindiga sun sace wasu mutum takwas a garin Biresawa da ke Karamar Hukumar Tsanyawa ta Jihar Kano a daren jiya na Litinin.
Wata majiyar da ta tabbatar da lamarin ta shaida wa Aminiya cewa maharan sun shiga garin tsakanin 11 na dare zuwa 12 na tsakar dare, inda suka yi awon gaba da maza biyu da mata shida.
’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun TuraiWani ɗan uwa ga waɗanda aka sace, Kabiru Usman, ya ce maharan sun zo ne a ƙafa ɗauke da makamai, suka kuma yi garkuwa da matarsa Umma, ɗiyarsa mai shekara 17, da matar ɗan’uwansa da wasu mata biyu daga Tsundu mai makwabtaka.
Ya ce al’ummar garin sun yi ƙoƙarin daƙile harin amma suka kasa saboda ƙarancin makamai, duk da cewa sun sanar da ’yan sanda da sojoji tun kafin faruwar harin bayan samun bayanan cewa ’yan bindigar na dosar yankin.
Ya roƙi gwamnati ta ɗauki mataki wajen ceto mutanen da aka sace da kuma kare rayukan mazauna yankin.
Aminiya ta yi ƙoƙarin ji ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, sai da har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.