Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)
Published: 10th, October 2025 GMT
Ga alkawarin, komai da Allah Ya yi wa wani, Allah Ya fada. Allah bai boye komai ba, sai abin da ya yi ga Annabi Muhammadu (S.A.W.), nan ko ba a fada ba, amma kowane annabi komai matsayinsa in ka duba sai ka ji sirrin da aka yi da shi. Yanzu game da wannan ma’aiki da annabawan da duk Allah ya tara su, ga abin da Allah Ya ce (ya ku) Annabawa, idan na ba ku littafanku da kyawawan dabi’u da hikima da ma’arifanku (ai, misali, an ba ka wukar yanka da takobin yanka da tagwayen masu ke nan).
Wani malami yake cewa in dai lamarin Manzon Allah (S.A.W.) ne wani baki ma bai iya fada, kamar za ka iya cewa komai Allah kan dauke shi yadda ya dauke shi, amma idan abin Manzon Allah ne Allah bai daukar shi da wasa.
Ayar ta yi gargadi a kan kar wani (a cikin Annabawa) ya juya baya ga wannan alkawarin da Manzon Allah ya zo da shi, ya ki tashi daga annabtarsa, ya ki bin Manzon Allah. To ka ga ashe Manzon Allah (S.A.W.) shi ne Annabin Annabawa, shi ne ma’aikin ma’aika, manzon Allah shi ne mafi girman duk wani mai girma na halittar Allah.
Manzon Allah (S.A.W.) shi ne mafi girman wani mutum da tarihi ya sani, shi wannan masanin falsafa da ya fadi wannan kusan ya karanta tarihin duniya tun daga farko har karshe, yana da tarihin duniya domin malami ne masanin falfasafa da ya yi bincike kwarai kuma ba shi da wani addini da zai hana shi karanta wannan. Ya nuna idan muna son mu karanta wani abu watakila muna tsoro saboda addini, shi ko ba shi da wannan (addini) ma, yake cewa “Manzon Allah (S.A.W.) shi ne mafi girman wani dan Adam da tarihi ya sani, shi ne wanda ya juya halitta ya kawo wa halitta canji, ya kawo mata canji cikin addini da yadda duk ake addini, a zo da addini ta kowane fanni sai Manzon Allah (S.A.W.).
Masanin falsafan ya ce Manzon Allah ya kawo canji a cikin addini, ya kawo canji cikin siyasa, da tsarin rayuwa, da tsarin kasa, da tsarin jama’a. Manzon Allah (S.A.W.) Annabi ne, ma’aiki ne daga Allah, Annabi ne, ma’ana malami ne wanda ya yi karatu a Hadarar Allah, ma’aiki ne, ma’ana ma’aiki ne ba kamar yadda muke dauka kamar wani dan sako ba, saboda galibi wasunmu abin da muka sani da an batun manzo sai a dauka dan aike ne kawai mai isar da sako ko ya karanta, amma ma’iki abu ne mai girma na daga annabawa, mutum ne da ya yi fikiri, ya yi tunani har ya samu saduwa a cikin hadarar Allah, har ya zama ma’aiki a hadarar Allah.
Yanzu duk abin da zai fada Hadarar Allah ce ta sa shi, siyasa ce da Hadarar Allah yake fada, Hadara ce ta sa shi ya fada, su sauran annabawa dukkansu Allah ya bar masu ladabin su isar da sakon wanda da ma su ma’aikan Allah ne, Annabi Isa ne ya dauke masa wannan ya ba shi izini, shi Annabi Isa ne zai fadi abin kai-tsaye daga Hadarar Allah, cewa Allah ne Ya ce ba wani ma’aiki ko wani abu ba, Annabi Isa ne kadai ke da wannan, amma sauran Annabawa dukanninsu za su ce ma’aikin Allah ne, kar ka za ci wani abu ne na wulakanci, a’a abu ne da ke da girma, saboda Manzon Allah ya yi fikiri, ya yi tunani ya yi halwar da duk wani mai takamar halwa zai yi, ya shiga inda duk wani dan tunani ke takamar ya shiga.
Annabi (SAW) ya shiga kogon hira ya yi adadin kwanaki, ya yi adadin watanni, duk malamai sun tafi ba sallah ya je ba, tahamusi ya rika yi, kamar yanzu mutum ya shiga kogo na dutse ka kulle kanka na tsawon kwanaki arba’in (40) ai ka cika namiji bare ka tafi daji-dajin ma ka hau dutse, dutsen ma ka shiga cikin kogo, Allah ya san me ye a cikin kogon nan. A zamani irin na wannan lokaci, har Allah ya ba Manzon Allah (SAW) abin da ya ba shi, dan haka mun gode wa Allah.
Duk annabawa fa ba wasa ba ne, kowane a cikinsu sai ya yi tunanin nan. Annabi Ibrahim ya yi tunanin nan, Allah Ya yaye masa malakutus samawati Wal’ ard. Annabi Musa (AS) wannan ciwon da ya yi shekaru arba’in (40) a cikin yawon neman Allah ya yi, amma duk da haka sai ka ga ya iya abin da Allah ya ba shi ga shi da wani a cikin jama’arsa ko zamaninsa zai yi wani tunani babba har ya iya gano wani abin da al’imma za ta ki yarda da wannan abu in ya yi wasa ma ta kashe shi. Amma Manzon Allah da tafakkurinsa zikirinsa da shiga cikin kogo da shafewarsa da haduwarsa da mudalakin hakika da Manzon Allah (S.A.W.) babu wani dan halitta da ya isa ya ce zai yi irin wannan har ya zo da abin da annabi ya zo da shi (S.A.W.), babu shi.
Shehi babbanmu, Ibn Arabi Hatimi duk abin da zai rubuta a cikin Futuhatil Makiyya da Khususil Hikam zai ce “ni fa magaji ne na manzon Allah, ban yi kusa ma da Manzon Allah (S.A.W.) ba, gado ne”, kuma da gaske yake yi. Shehu Ibrahim Inyass (R.A.) ya ce duk abin da ya fada, ya fada ne saboda shi Hadimin Manzon Allah ne, ya ce Manzon Allah ne ya ba ni, ya yi mani wata kyauta ta daban, bayan baiwar can, ya kuma ba ni abin da ma bai ba halitta ba, amma komai girman abin na Shehu Ibrahim ya ce Manzon Allah ne ya ba shi.
Duk irin wannan ilimi na Sayyidina Ali wanda ya bugi kirji ya ce ni ne digon nan na karkashi ba’un, amma duk wanna sunansa kofar ilimin Manzon Allah, amma gidan ilimi shi ne Manzon Allah (S.A.W.), saboda haka mu daina tsoro, malamai na musulunci su daina tsoro, ba wani wanda zai zo da wani karatu, ba wani wanda zai fito da wani abu wanda ya fi karfin na Annabi din nan (S.A.W.), a’a duk abin da zai zo da shi a cikin na Manzon Allah (S.A.W.) ne.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: a Hadarar Allah duk wani mai ya yi tunani da Allah Ya da Allah ya Da Allah Ya
এছাড়াও পড়ুন:
Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi
Kishi halak ne kuma so ne yake kawo kishin. Masu irin wannan kishin karshensu nadama ce. Kishi wani abu ne da ake jinsa a cikin rai, kuma kishi ba sai akan aure ake yin sa ba.Hanyoyin da ya kamata abi wajen magance irin wannan shi ne; muna tuna komai yayi farko to yana da karshe, sannan ba kanta farau ba kuma ba kanta karau ba. Muna saka hakuri da tawakkali mu yi kiyayya ba mai zurfi ba, sannan mu yi soyayya ba mai zurfi ba, a karshe sai abin ya zo mana da sauki. Allah ya sa mu dace, amin.
Sunana Comr, Nr. Ibrahim Lawan Stk:
Abubuwa da dama na haifar da kishi amma mafi lura shi ne rashin godiya a wajen Allah subahanahu wata’ala da kuma son zuciya tare da son rai irin na mata. Kishi shi ne son kasancewa da namiji a matsayin abokin tarayya ko zamantakewar Aure ba tare da wata ta ji ra’ayin hakan ba ko kuma ta nuna bukata tare da ra’ayin akan namijin da wata ke rayuwa da shi ba. Hanyoyin da za a bi domin magance matsalolin kishi musamman a lokacin da miji zai karo abokiyar zama sun hada da hakuri, danne zuciya, tare da juriya hadi da biyayya ga duk wani umarni daga wajen miji don kuma kaucewa sabawa umarnin Allah da Manzon sa (S.A.W).
Sunana Nabila Dikko, Argungun Jihar Kebbi:
To mafi akasarin dalilai da ke sa mata irin wannan kishi shi ne; karancin fahimta da rashin hakuri, da son mallaki namiji su kadai, da son zuciya, kuma hakan na kawo rashin zaman lafiya da rikici da lalacewar dangantaka. Kishi wani abu ne da ke sa zuciya ta dinga son mallakar wani abu ita kadai ko abin da kake da shi ko tsoron rasa shi. A musulinci, kishi halas ne idan bai kauce wa ka’ida ba. Domin magance kishi dole sai mace ta dogara ga addu’a, ta daidaita tunaninta, ta rungumi gaskiyar cewa mijinta yana iya kara aure, sannan ta mayar da hankali wajen kyautatawa maigidanta ba tare da yin abubuwan da ba su dace ba. Shawarata ga mata su kasance masu natsuwa, su guji haddasa rigima. Sai maza ku kasance masu adalci, ku bayyana gaskiya, ku kiyaye hakkin kowace mata, a daidaita adalci ku daina haddasa tsananin kishi a tsakanin matanku.
Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:
To, da farko dai akwai jahilci domin shi ke jawo mutum ya kashe kan sa, don indai mutum yana da ilimi ya san illar kashe kai. Sai na biyu kuma rashin rungumar kaddarar da Allah ya kaddarawa mutum domin ita kaddara bata canjawa. To, kishi wani abu ne da Allah yake halittar mutane da shi maza da mata to a lokuta da dama maza su kan yi kokari wajen sarrafa nasu sabanin wasu daga cikin mata da kishin yake sa su aikata aikin da-na-sani ko ma su hallaka kan su.
Sunana Hafsat Sa’eed, daga Neja:
Kishi yana cikin addinin musulunci amma kuma akwai kishin hauka irin wanda mace za ta je ta hallaka ‘yar’uwarta ko abin da ‘yar’uwarta ta yi sai ta yi. Mutum yana da wahala ya daukowa kansa babban aiki. Idan namiji zai karo aure ya kamata ka bashi goyan baya, ka yi masa fatan alkhairi, haka idan ta shigo ka samu ku zauna lafiya dole akwai abin da zai sa ka yi kishi sai ka yi daidai misali ba wanda ya haura ka’ida ba.
Sunana Hassana Yahaya Iyayi, daga Jihar Kano:
Babbar magana ai wadanan dai sun hada kansu da wahala da kuma da-na-sani dan kishi dai babu komai a cikinsa sai wahala. To, shashanci ne da rashin sanin ciwon kai. Kishi dai wani halitta ne wani kuwa dorawa kaine, kishiya babu dadi amma ayi hakuri a kau da kai. Sun yi hakuri su kara hakuri.
Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos, a Jihar Filato:
Babu shakka kishi na zama guba a wajen easy matan, musamman a lokacin da mazajen su za su kara aure. Wasu kan nemi jefa kansu ga fushin ubangiji ta hanyar kokarin tilastawa mazajen su jingine bukatar su, ta kara aure, amma kuma su kawar da kai daga halayyar sa ta neman mata a waje. Sannan su a karan kansu, idan ma ba su sha guba sun hallaka kansu ba, suna shiga malamai, matsafa, da ‘yan tsibbu, wadanda ke aikata shirka, don neman biyan bukatun su. Akwai wadanda sanadiyyar kishi suke gamuwa da ciwon hawan jini da ciwon zuciya, ko matsalar kwakwalwa.
Sunana Princess Fatima Mazadu, Goben Nijeriya:
Kishi kam masifa ce babba, soyayya da kauna ke janyo wa wasu kishi, wasu kuma kwadayin dukiya da kyle-kyelen duniya. Danganta kansu ga mutuwa a kowani lokaci namiji bai zamo lallai ya rigata mutuwa ba, sannan mace ta sani lallai kishi halitta ce, amma bai halarta akan auren wata har ya zamo kin iya kashe kanki ba ko saboda abun duniya. Shawarata a nan su rage mummunan kishi, su nemi na kansu, su zamo masu godiya da kulawa a rayuwa wasu matan ko auren ma babu bare kwadayin dukiya da kishi.
Sunana Muktari Sabo Jahun A Jihar Jigawa:
Tabbas ana samun mata masu kishin da ya wuce hankali saboda son zuciya kuma gaskiya makomarsu bata kyau. Kishi dabi’ace da Allah ya halicci mata akai har ma wasu mazan ya kamata su nuna kishinsu ta hanya mafi kyau lokacin da mijinsu zai kara aure kuma su sani da ba a auren da suma ba a aurosu ba. Shawara a nan ita ce kowa ya ji tsoron Allah akan hakan.
Sunana Hauwa Abubakar Sarki, daga Suleja Jihar Neja:
Kishiya halitta ce sai dai kowa da yadda yake sarrafa nasa kalar kishin, har kullum muna kira ga matan da suke da tsanani kishi da kar su bari kishi ya rufe masu ido har ya kai ga sun aikata abun da za su zo suna da-na-sani. Biyewa Zuciya, kuma sannan a dabi’ar dan namiji baya son macen da ta cika tsanani kishi. Kishi wata aba ce da ubangiji ke halittar bawa da shi ba tare da ya sani ba. Tsananta addu’a da mika al’amura ga ubangiji a yayin da mijinki ya zo maki da zancen kara aure, dole za ki ji babu dadi a ranki amma in ki ka dage da addu’a sai komai ya zo cikin sauki. Shawara ta kada mu bari zukatanmu ya zamana ita ke sarrafa mu ba mu ke sarrafa ta.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA