’Yan sanda sun kama mutum 26 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a Kaduna
Published: 10th, October 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna ta kama mutum 26 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne tare da kwato makamai da kudade daga hannunsu.
Daga cikin abubuwan da aka samu nasarar kwatowar har da bindigogi na gida guda huɗu, makamai masu hatsari da kuma tsabar kuɗi Naira 546,000 da ake zargin wani ɓangare ne na kuɗin fansa.
An kama waɗanda ake zargin ne a cikin jerin samame da aka gudanar daga ranar 3 zuwa 5 ga watan Oktoban 2025, a sassa daban-daban na jihar.
Samamen ya haɗa jami’ai daga sashen ’yan sanda na Anchau, Hukumar Kula da Tsaro ta Jihar Kaduna (KADVIS), da kuma sashen yaƙi da garkuwa da mutane na rundunar.
Bayanin samamen na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar a ranar Alhamis.
Ya ce cikin wani samame da aka kai da safiyar ranar 5 ga watan Oktoba, an kama mutane shida, ciki har da wani Jibrin Abubakar wanda aka fi sani da “Oga,” bayan samun sahihan bayanan sirri.
Waɗanda ake zargin sun yi garkuwa da wani mutum mai shekaru 60 da haihuwa mai suna Idris Adamu, a ranar 22 ga Satumba, inda suka tsare shi na tsawon kwanaki kafin su sako shi bayan sun karɓi kuɗin fansa na naira miliyan biyar.
An kuma kama wasu mutane biyu bayan musayar wuta da ’yan sanda, yayin da wasu biyu suka cika wandonsu da iska.
A lokacin samamen, ’yan sanda sun kwato bindigogi biyu na gida kirar pump-action, harsasai biyar da ba su da ciko, laya, da kuma kuɗi naira 546,000 da ake zargin wani ɓangare ne na kuɗin fansa.
A wani samame daban da aka gudanar a ranar 3 ga Oktoba kuma, an kama wani da aka gano da suna Habibu Alhaji Ahmadu, wanda aka fi sani da “Munyaye,” daga ƙaramar hukumar Ikara, tare da bindigogi biyu kirar revolver ƙirar gida.
Ya amsa cewa ya taba kai hari ga wani mazaunin yankin, kuma an danganta shi da wata ƙungiyar ’yan ta’adda da ke aiki a yankin.
Kazalika, rundunar ta ce an kuma kai wani samamen a ranar hudu ga watan na Oktoba a kauyen Gazara da ke ƙaramar hukumar Makarfi, inda aka kama mutum 14, ciki har da wani Bello Umar, wanda aka taɓa gurfanar da shi a baya kan laifin garkuwa da mutane.
Dukkan waɗanda aka kama suna tsare a hannun ’yan sanda yayin da ake ci gaba da bincike.
Rundunar ta ce tana ci gaba da farautar sauran mambobin ƙungiyar da kuma ƙoƙarin kwato ƙarin makamai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda garkuwa da mutane garkuwa da mutane da ake zargin
এছাড়াও পড়ুন:
Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
Daga Musa kutama , kalaba
Hasana Aminu matashiyar jaruma ce a Masana’antar Kannywood, wacce ta fito a finafina da dama ciki har da fim xin A Duniya da wasu fitattun finafunan Hausa. A zantawarta da Aminiya, Hasana Aminu wadda aka fi sani da suna Nabila ta ce, a halin yanzu tana tauna taura biyu ne a baka
Ga yadda girar su ta kasan ce:
Sunan Jarumar?
Sunana Hasana Aminu, amma an fi sani na da suna Nabila a Masana’antar Kannywood da ke Kano
Ta yaya kike gwama karatu da kuma kasuwanci da harkar fim?
Eh, to farko ko da na shigo Masana’antar Kannywood sai na ga ai ashe ma ina da damar da zan iya yin karatu yayin da kuma nake sana’ata ta harkar fim. Domin kafin in fara fim na riga na samu kwalina na NCE. To sai na fahimci tunda dai ban da harkar fim kuma ina yin kasuwancin da zai iya taimaka min in xauki nauyin qaro karatu, ai gara in je in karo karatun. Wannan ne dalilin da ya sa na koma karatu, inda yanzu nake karatun Kimiyyar Aikin Xakin Gwaje-gwaje a matakin Babbar Difloma wato HND kuma sakamakon haka wasu ma daga cikin ‘yan masana’antar sun yi koyi da ni, sun koma makaranta su ma suna ci gaba da karatunsu.
Yi wa mai karatu bayanin yadda kika gwama karatun fim da kuma kasuwancu?
Gaskiya daga Asabar zuwa Lahadi ne nake zuwa karatun, daga Litininn zuwa Juma’a duk ina da lokaci da nake tafiya harkokin fim xin.
Don yanzu duk a inda aka kira ni a harkar fim ina da lokacin da zan je in dawo tsakanin Litinin zuwa Juma’a. Amma Asabar da Lahadi kowa ya san ranar makaranta ce duk wanda ke masana’antar ko ya aiko ya san lokacin makaranta ne.
Ko hakan bai sanya kin takura kanki ba?
Gaskiya ban tava jin na takura kaina ba, wani abin ma da ya fi haka duk zan iya haxawa da shi saboda ina da lokaci isasshe.
Ga wanda duk ya karanta wannan hira ta yaya zai iya gane cewa Hasana Aminu ce ta Kannywood da ake kallo a fim xin kannywood?
Eh, duk wanda ya san ni ko ya kalli finafinan da na yi kamar su Dare Xaya da Rigar Aro zai san ni ce
Ki fito a fim xin Xan Jarida kuma a matsayin ‘yar jarida kika fito, ko a iya cewa ke ma hala kina da shauqin zama ‘yar jarida ?
A gaskiya na fito dai a qanwar xan jaridar, inda na kasance abokiyar shawararsa a kan duk abin da yake yi ya riqa taqaitawa a irin aikinsa da kuma duk abin da yake yi ya lura da aikinsa.
Ko hakan ta sa ke ma kina sha’awar aikin jarida?
(Dariya) gaskiya ba na da sha’awar hakan.
Waje xaya ana samun wasu ‘yan matsaloli a Kannywood ta yadda ake samun ta da qura tsakaninsu da hukumomi, sai ga shi wasu kuma yanzu ne ma suke shirin shigowa masana’antar. Me za ki ce?
To gaskiya matsala kam akwai ta masu qoqarin shigowa kada su daka ta wasu waxanda suke ciki. Domin kowa da irin tarbiyarsa. Sannan kuma su yi binciken mutanen da suke son su shigo ta hannunsu
Batun manyan matoci na alfarma da riqe manyan wayoyi da mutane ke yawan ta da qura suna baza zarge-zarge ga ‘yan fim musamman mata. Me za ki ce?
Eh to idan duba wani lokaci za ka ga wani abu shi ke ta da wani. Domin in ka yi la’akari da hawa babbar mota, ai akwai maza akwai mata a Masana’antar Kannywood kuma matan ne kawai aka fi zargin gani suna hawa motocin. To su mazan me ya sa ba su hawan manyan motocin ko su ba su samun kuxi ne kamar mazan. Don haka wannan ba abu ne da zan so zurfafawa ba domin idan ka shigo harkar Kannywood za ka ga abubuwa da daman gaske. Kuma a rayuwa idan mutum bai da damar yin abu kuma ya sa wa kansa dole sai ya yi shi ko ta wane hali, to za a iya shiga wani hali da ba a zata ba.
Sabon salon xora finafinai a YouTube da haskawa a sinimar hakan ko a ganinki ya kawo wani ci gaba?
Eh, to wannan ka ga shi yanayin harkar ce abu ne wanda su masu shirya fim suke dubawa, ka ga mutum a da zai iya ya sayar da fim xinsa na series wato mai dogon zango, amma a yanzu yana da dama biyu ta xorawa a YouTube da sayarwa don samun riba.
Ana samun karvuwar finafinan Hausa a sauran qasashe maqwabtan Nijeriya. Me za ki ce a kan haka musamman a qasashen Nijar da Kamaru Ghana da Chadi ?
Gaskiya hakan na faruwa ne saboda yadda ake inganta ayyukan fim a Kannywood ta hanyar qwarewa da kuma samar da ingantattun kayan aiki. Wato lokaci ne kowa ya sa kuxinsa zai ga kuxinsa yadda ka zuba kuxi, ka yi fim hakan za ka ga ya yi gaba zuwa wasu wuraren da ma ba ka yi tsammani ba.