Aminiya:
2025-10-13@13:38:03 GMT

’Yan sanda sun kama mutum 26 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a Kaduna

Published: 10th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna ta kama mutum 26 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne tare da kwato makamai da kudade daga hannunsu.

Daga cikin abubuwan da aka samu nasarar kwatowar har da bindigogi na gida guda huɗu, makamai masu hatsari da kuma tsabar kuɗi Naira 546,000 da ake zargin wani ɓangare ne na kuɗin fansa.

Tinubu ya yi wa Mamman Vatsa, Farouk Lawan da wasu mutum 173 afuwa Tinubu ya naɗa Amupitan a matsayin Shugaban INEC

An kama waɗanda ake zargin ne a cikin jerin samame da aka gudanar daga ranar 3 zuwa 5 ga watan Oktoban 2025, a sassa daban-daban na jihar.

Samamen ya haɗa jami’ai daga sashen ’yan sanda na Anchau, Hukumar Kula da Tsaro ta Jihar Kaduna (KADVIS), da kuma sashen yaƙi da garkuwa da mutane na rundunar.

Bayanin samamen na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar a ranar Alhamis.

Ya ce cikin wani samame da aka kai da safiyar ranar 5 ga watan Oktoba, an kama mutane shida, ciki har da wani Jibrin Abubakar wanda aka fi sani da “Oga,” bayan samun sahihan bayanan sirri.

Waɗanda ake zargin sun yi garkuwa da wani mutum mai shekaru 60 da haihuwa mai suna Idris Adamu, a ranar 22 ga Satumba, inda suka tsare shi na tsawon kwanaki kafin su sako shi bayan sun karɓi kuɗin fansa na naira miliyan biyar.

An kuma kama wasu mutane biyu bayan musayar wuta da ’yan sanda, yayin da wasu biyu suka cika wandonsu da iska.

A lokacin samamen, ’yan sanda sun kwato bindigogi biyu na gida kirar pump-action, harsasai biyar da ba su da ciko, laya, da kuma kuɗi naira 546,000 da ake zargin wani ɓangare ne na kuɗin fansa.

A wani samame daban da aka gudanar a ranar 3 ga Oktoba kuma, an kama wani da aka gano da suna Habibu Alhaji Ahmadu, wanda aka fi sani da “Munyaye,” daga ƙaramar hukumar Ikara, tare da bindigogi biyu kirar revolver ƙirar gida.

Ya amsa cewa ya taba kai hari ga wani mazaunin yankin, kuma an danganta shi da wata ƙungiyar ’yan ta’adda da ke aiki a yankin.

Kazalika, rundunar ta ce an kuma kai wani samamen a ranar hudu ga watan na Oktoba a kauyen Gazara da ke ƙaramar hukumar Makarfi, inda aka kama mutum 14, ciki har da wani Bello Umar, wanda aka taɓa gurfanar da shi a baya kan laifin garkuwa da mutane.

Dukkan waɗanda aka kama suna tsare a hannun ’yan sanda yayin da ake ci gaba da bincike.

Rundunar ta ce tana ci gaba da farautar sauran mambobin ƙungiyar da kuma ƙoƙarin kwato ƙarin makamai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda garkuwa da mutane garkuwa da mutane da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan yadda shugaba Bola Tinubu ya yi wa wasu mutane afuwa, ciki har da waɗanda suka aikata manyan laifuka.

A cikin saƙon da Atiku ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ana yin afuwa ne ga waɗanda aka yi wa rashin adalci ko waɗanda suka nema gafara bayan sun shafe wani lokaci a gidan yari.

Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna

Ya ce a wannan karon an yi wa masu safarar ƙwayoyi, masu garkuwa da mutane, masu kisan kai, da kuma masu cin hanci da rashawa afuwa.

Atiku, ya ce abin mamaki ne yadda gwamnati ke yafewa irin waɗannan mutane, a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsaro da lalacewar tarbiyya, musamman tsakanin matasa masu shan miyagun ƙwayoyi.

Ya ce bincike ya nuna cewa kashi 29 na waɗanda aka yi wa afuwa suna da alaƙa da hakrar miyagun ƙwayoyi, yayin da Najeriya ke ƙoƙarin wanke sunanta a idon duniya kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi.

Atiku, ya ce maimakon wannan afuwa ta zama darasi ga masu laifi, ta zama hanyar durƙusa da ɓangaren shari’a da jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu wajen kamawa da hukunta masu aikata laifuka.

Ya ƙara da cewa idan gwamnati ta fara yafe wa masu laifi, hakan zai rage ƙimar shugabanci kuma ya ƙarfafa wa masu aikata laifuka su ci gaba da aikata su.

Atiku ya jaddada cewa Najeriya tana buƙatar  shugabanci na gari wanda zai tabbatar da adalci a shari’a, ba tare da nuna bambanci ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano