Leadership News Hausa:
2025-10-13@13:38:00 GMT

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Published: 10th, October 2025 GMT

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

 

Cikin darussan da wannan rikici ya tabbatar mana, akwai rashin tasirin amfani da karfin tuwo wajen warware duk wani rikici. Tabbas karfin soji kadai ba zai iya magance takaddama ko tashin hankali ba, ballantana ya wanzar da tsaro da walwalar bil’adama.

 

Muna iya ganin hakan a zahiri, idan mun lura da yadda Isra’ila ta nuna a fili cewa hare-haren da ta kwashe shekaru biyu tana kaiwa sassan Gaza za su iya kawo karshen barazanar da ta ce kungiyar Hamas ke haifar mata, amma sai ga shi daga karshe sakamako ya nuna akasin haka.

Har yanzu dai sannu a hankali ana komawa ga shawarar da kasashe masu son zaman lafiya suka jima suna bayarwa, wato a rungumi tattaunawa, da dakarar da bude wuta, kana a shigar da agajin jin kai, da share fagen warware takaddamar ta hanyar siyasa.

 

A wannan gaba, ya wajaba a jinjinawa kasashe masu son zaman lafiya kamar Sin, da mafiya yawan kasashe masu tasowa, wadanda suka jima suna maraba baya ga cimma daidaito, da kawo karshen wannan tashin hankali da ya ki ci ya ki cinyewa, ciki har da sama da kasashe 150 membobin MDD da suka amince da Falasdinu a matsayin kasa.

 

Ko shakka babu, lokaci ya yi da za a kawo karshen tashe-tashen hankula, da samar da isasshen agajin jin kai ga masu bukata a Gaza, kana a komawa tattaunawar diflomasiyya ta kafa kasashe biyu masu cin gashin kai, a matakin karshe na ganin bayan wannan tashin hankali baki daya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar  October 9, 2025 Daga Birnin Sin Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar October 9, 2025 Daga Birnin Sin An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin October 9, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

Ya kara da cewa, ana ci gaba da kokari don ganin an iske masu yin kiwon shanu a kasar nan, domin fadakar da su kan muhimmancin rungumar wannan tsari na zamani.

 

Sai dai, ya yi nuni da cewa; wasu al’adu na haifar da tarnaki a tsakanin wasu masu kiwon a kasar na rungumar wannan tsarin.

 

“Na ga wasu gidajen gona da ake yin irin wannan dabara ta zamani, sannan kuma ana bayar da kulawar da ta kamata; wanda hakan ya sanya ake iya samar da litar madarar shanu daga tsakanin lita 15 zuwa 30,” in ji Jatau.

 

“Akwai wasu Fulani Makiyaya ‘yan kalilan da suka rungumi wannan tsari, misali a Jihar Bauchi; inda wani makiyayi ya rungumi wannan tsari tare kuma da amfanarsa yadda ya kamata,” a cewarsa.

 

“A lokacin da muka gudanar da ayyukanmu, wasu daga cikin Fulani Makiyaya, sun zo sun saurari wannan batu na dabara ta zamani tare da shanunsu, mun kuma aiwatar da tsarin a kan shanun nasu, inda daga baya suka ga yadda madarar shanunsu ta kara habaka,” in ji shi.

 

Jatau ya kara da cewa, suna kan ci gaba da bai wa Fulani Makiyaya kwarin guiwa, kan rungumar wannnan tsari, sai dai, wasu na fuskantar kalubale na kula da shanunsu da aka dora su a kan tsarin.

 

“A wasu kasashen na Afirka za ka cewa, Makiyayin da suka rungumi wannan tsari, na da shanu uku ne kacal da daukacin iyakansa suka dogara a kansu, wanda hakan ke ba su dama a kullam na samar da litar madara daga tsanakin 15 zuwa 20, “ a cewarsa.

 

Ya kara da cewa, hakan ya sanya a kullum suke samar wa da kansu dimbin riba, wanda kuma hakan ya sa ba su dogaro da aikin gwamnati ba kwata-kwata.

 

Ya yi nuni da cewa, idan har a raba daya za ka sayar da litar madara daya kan Naira 1,000, a wata za ka iya samun kudin shiga da suka kai Naira miliyan 1.8 da shanu uku kacal.

 

Ya ci gaba da cewa, da wannan ribar kadai za ka iya ci gaba da ciyar da shanun da lula da lafiyarsu da biyan ma’aikatan da ke kula da su da kuma daukar sauran dawainiyar kula da iyalanka.

 

Ya bayyana cewa, duba da cewa; ana fuskantar matsalar wajen da dabbobi za su yi kiwo a kasar nan, amma idan Fulani Makiyaya suka rungumi wannan tsari, hakan zai rage yawan samu rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani Makiyya a kasar.

 

Kazalika, ya sanar da cewa; idan masu kiwon suka dauki wannan tsari za a samu cewa, alfanun da za su samu ya dara irin na kiwon gargajiya da ake yi a cikin kasar.

 

Jatau ya bayyana cewa, wannan tsarin abu ne da ke da tsawon tarihi a kasar nan, domin an faro shi ne tun a shekarar 1949; tun bayan da aka dauki nau’in na jinsin daga wata gona da ke garin Shika a birnin Zaria, aka kuma kai shi zuwa cibiyar gudanar da bincike kan lafiyar dabbobi ta Bom.

 

Sai dai, ya bayyana cewa; rashin ci gaba da bibiyar wannan tsare-tsaren daga bangaren gwamnati, hakan ya haifar da koma baya ga wannan tsair.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina October 3, 2025 Noma Da Kiwo Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo October 3, 2025 Noma Da Kiwo Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi September 27, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
  • Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza
  • Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara