Leadership News Hausa:
2025-10-13@13:38:02 GMT

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Published: 10th, October 2025 GMT

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Yawan mace-mace ta hanyar cutar kwalarar, na faruwa ne duk da biliyoyin Nairori da aka ce gwamnati da abokan huldar kasa da kasa suna kashewa, domin kokarin ganin an dakile ta.

 

Wadannan kudade sun hada da kason kasafin kudi na shekara-shekara, wanda ya kunshi miliyoyin Nairori; akwai dala miliyan 700 da bankin duniya ya bayar domin samar da tsaftataccen ruwa sha, tsaftar muhalli a fadin kasa baki-daya, tallafin dala miliyan 2 daga Majalisar Dinkin Duniya, dubban daruruwan allurar rigakafin cutar kwalara da asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) suka bayar da sauran makamantansu.

Alkaluman da aka samu daga cibiyar NCDC, sun nuna cewa a cikin 2020, kasar ta samu rahoton kimanin mutane 3,513 da ake zargi da kamuwa da cutar da kuma mutuwar mutum 95. Adadin wadanda suka mutu ya karu kwarai da gaske a shekarar 2021 tare da mutum 111,062 da ake zargi da kamuwa da cutar, kazalika akwai mutum 3,604 da suka mutu a cikin jihohi 33, ciki har da babban birnin tarayya Abuja.

Har ila yau, kwayar cutar kwalara ta ‘Bibrio cholerae’ ce ta haifar da ita, cutar kwalara cuta ce da ake saurin kamuwa da ita; ta hanyar gurbataccen abinci da ruwa da kuma rashin tsaftar muhalli ke haifar da ita.

Barkewar cutar, ta fi yin kamari a lokacin damina, daga watan Mayu zuwa watan Oktoba, yayin da ambaliyar ruwa da gurbatattun hanyoyin ruwa ke kara ta’azzara wajen yaduwa. Alamomin cutar kwalara sun hada da yawan zawo, amai da murdawar ciki da kuma rashin ruwa a jiki. Za kuma a iya saurin tarar cutar ta hanyar amfani da ruwan gishi da sikari da kuma rigakafi, idan ba a yi saurin aiwatar da hakan ba, za a iya rasa rai cikin kankanin lokaci.

Shekarar 2021 na daya cikin wadda ake zargin mutane kimanin 111,062, sun kamu da cutar tare da mutuwar kusan mutum 3,604 a jihohi 33 ciki har da babban birnin tarayya Abuja tare da yara ‘yan shekara daga 5 zuwa 14 da suka fi kamuwa da cutar.

Jihohin Bauchi, Jigawa, Kano da Zamfara ne ke da kashi 53 cikin 100 na dukkanin masu fama da cutar.

A shekarar 2022, alkaluman yawan mace-macen sun ragu zuwa 592, wato da kashi 2.5 cikin 100, kazalika a cikin 23,763 da ake zargi sun kamu da cutar daga jihohi 32 ciki har da babban birnin tarayya Abuja, Jihohin Borno, Yobe, Katsina, Gwambe, Taraba da Kano, na da kashi 83 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar.

Daga cikin mutum 3,683 da ake zargin sun kamu da wannan cuta ta kwalara a 2023 a cikin jihohi 31, an samu rahoton mutuwar mutum 128 (kashi 3.5 cikin 100), inda yara ‘yan kasa da shekara biyar suka fi kamuwa da cutar, sai kuma wadanda ke tsakanin shekaru biyar zuwa 14. Jihar Zamfara ce ke da kashi 25 cikin 100 na dukkanin wadanda ake zargi da kamuwa; yayin da Jihohin Kuros Riba, Katsina, Bayelsa, Ogun, Ebonyi da kuma Neja ke da kashi 57 cikin 100.

Adadin ya sake karuwa a shekarar 2024 zuwa mutum 10,837 da ake zargin sun kamu da cutar da kuma mutuwar mutane 359 deaths (kashi 3.3 cikin 100) a fadin jihohi 36 na kasar nan a ranar 29 ga watan Satumba, wanda shi ne na karshe da cibiyar NCDC ta fitar kan bullar cutar ta kwalara a wannan shekarar. Har ila yau, yara ‘yan kasa da shekara biyar sun fi kamuwa da cutar, sai kuma wadanda ke tsakanin shekara biyar zuwa 14. Kazalika, Jihar Legas ta samu kashi 43 cikin 100 na kafatanin wadanda ake zargi da kamuwa da cutar.

A cikin watan Yulin bana, yayin da aka kaddamar da neman tallafin gaggawa na kimanin dala miliyan 20, domin yaki da cutar kwalara a Nijeriya da sauran kasashen yammacin Afirka da kuma Afirka ta tsakiya, daraktan yanki na UNICEF, Gilles Fagninou ya ce; “Zuwa karshen watan Yuni, Nijeriya ta samu rahoton bullar cutar kwalara kimanin 3,109 da kuma mutuwar mutum 86 cikin jihohi 34.”

Ya ce, yawan adadin wadanda ake zargin sun kamu da cutar ne yasa Nijeriya ta kasance a matsayin kasa ta biyu da cutar ta fi yin kamari a yammacin Afirka da kuma Afirka ta tsakiya.

Ya kara da cewa, “Mamakon ruwa da ambaliyar ruwan sama da kuma yawan wadanda suka rasa matsugunansu, duk suna kara ruruta wutar hadarin kamuwa da cutar kwalara da kuma jefa rayuwar yara cikin hadari. Yara kanana, sun fi fuskantar barazanar kamuwa da cutar kwalara, sakamakon dalilai kamar haka; rashin tsafta, rashin samun tsaftataccen ruwa sha, rashin tsaftace muhalli da kuma rashin isasshen ruwa a jikin mutum,” in ji shi.

 

Yadda Muka Rasa Su Cikin Kankanin Lokaci- Iyalai

Wata fita da matar Musa Aliyu ta yi da ‘ya’yanta uku cikin farin ciki, ta kare bakin ciki da kuka ga ‘yan’uwa; bayan halartarsu wani bikin daurin aure a unguwar da ke makwabtaka da cikin birnin Bauchi. Bayan ‘yan sa’o’i kadan da kammala cin abinci a wajen taron, sai suka fara amai da bayan gida a-kai-a-kai.

“Matata da ‘ya’yana uku, sun kamu da cutar bayan cin abinci a wajen wani wurin daurin aure a Bauchi, ‘yata ta farko ce ta fara kamuwa; kafin daga bisani sauran ‘ya’yan nawa biyu suka kamu da kuma mahaifiiyarsu,” wani mazaunin ‘Federal Low Cost Housing Estate’.

Duk da cewa, wasu daga cikinsu sun tsira da rayukansu; amma Muhammad Aliyu, mai shekaru 5 ya rasu. Yanzu haka, shekara hudu kenan da rasuwarsa, amma mutuwar tasa ta bar tabon dab a zai taba gogewa ba a dangin.

A shekarar 2021 a Bauchin, cutar ta yi wa ‘ya’yan Fatima su bakwai yankan kauna, wadanda mahaifinsu ya rasu shekara biyu da suka wuce. ‘Yar’uwar Fatima, Anisha Saidu, wadda ke zaune a Unguwar Kofar Ran ta bayyana cewa; ta rasu ne sa’o’i kadan bayan ta fara nuna alamun cutar ta kwalara.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi October 10, 2025 Labarai ‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar October 9, 2025 Labarai Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos October 9, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da ake zargi da kamuwa sun kamu da cutar kamuwa da cutar cutar kwalara da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa: Iran tana goyon bayan duk wani Shirin zaman lafiya da ya hada da dakatar da kisan kiyashi a Gaza

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta tabbatar da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana goyon bayan duk wani mataki ko wani yunkuri da ya hada da kawo karshen yakin kisan kiyashi a Gaza, janyewar sojojin mamayar Isra’ila, shigar da kayan agajin jin kai, sakin fursunonin Falastinawa, da kuma tabbatar da dukkanin hakkokin Falasdinawa.

Haka kuma ta kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na mai goyon bayan halastacciyar gwagwarmayar al’ummar Falastinu samun tabbatar da ‘yancin kai, ta yi amfani da dukkanin karfinta na diflomasiyya a cikin shekaru biyun da suka gabata, musamman a matakin yanki, kungiyar hadin kan kasashen musulmi, da Majalisar Dinkin Duniya, wajen matsin lamba ga yahudawan sahayoniyya da magoya bayansu da su dakatar da kisan kiyashi da kuma janyewar ‘yan mamaya daga Gaza.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta yi juyayin tunawa da manyan shahidan gwagwarmaya, inda ta jaddada nauyin da ke wuyan kasashen duniya na hana duk wani cin zarafi daga ‘yan mamaya, tare da yin kira ga dukkan bangarorin da su yi taka tsantsan da yaudara da karya alkawari da sahayoniyya suke yi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka  Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Amurka ta kakaba wa wasu kamfanoni 50 takunkumi saboda sayen man Iran October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Falasdinawa Sun Gano Gawakin Wadanda HKI Ta Kashe A gaza  Fiye Da 320 Cikin Kwanaki Biyu Kacal
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
  • Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara