Aminiya:
2025-10-13@13:37:51 GMT

An kama 26 da ake zargin masu garkuwa da mutane

Published: 9th, October 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ta kama wasu mutane 26 da ake zargi da yin garkuwa da mutane, tare da ƙwato bindigogi guda 4, da muggan makamai da dama.

Ta kuma kama wani ɓangare na kuɗin fansa da ake zargin an biya masu garkuwa da mutane a wasu hari daban-daban a jihar.

Nasarar kamen dai ya biyo bayan wasu jerin samame da jami’an ’yan sanda da na ’yan banga suka yi a tsakanin ranakun 3 zuwa 5 ga watan Oktoban 2025, inda suka yi ta kai farmaki kan gungun masu garkuwa da mutane da ke kai hari a ƙananan hukumomin Anchau, Ikara da kuma Makarfi.

Tinubu ya naɗa Amupitan a matsayin Shugaban INEC Ma’aikatan jami’a sun yi zanga-zanga a Jami’ar Bayero

Wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan ya fitar a ranar Alhamis, ta ce samamen da aka gudanar tare da haɗin gwiwar hukumar ’yan banga ta Kaduna, wani ɓangare ne na ƙoƙarin kawar da ’yan bindiga da yin garkuwa da mutane a jihar.

Sanarwar ta ce, an samu nasarar farko ne a ranar 5 ga watan Oktoba, a lokacin da tawagar ’yan sintiri daga reshen Anchau, da ke aikin sahihan bayanan sirri, suka kai farmaki maɓoyar wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da misalin ƙarfe 1:15 na safe, tare da kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a ciki, ciki har da wani Jibrin Abubakar mai suna Oga, mai shekara 21.

“Bincike ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun haɗa baki ne a ranar 22 ga watan Satumba, 2025, don yin garkuwa da wani Idris Adamu mai shekara 60, wanda suka yi garkuwa da shi na tsawon kwanaki kafin su sake shi bayan sun karɓi kuɗin fansa Naira miliyan 5,” in ji Hassan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Masu Garkuwa da mutane masu garkuwa da mutane da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba

Ya bayyana cewa an riga an hada wadanda aka ceto da iyalansu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike da aikin ceton domin gano wadanda suka aikata laifin da kuma kubutar da sauran wadanda ake tsare da su, idan suna nan.

 

A halin da ake ciki kuma, kwamandan Runduna ta 6 ta Sojan Nijeriya, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba da saurin daukar mataki da hadin kai tsakanin sojoji da ‘yansanda wanda ya kai ga nasarar aikin ceton.

 

Ya sake jaddada kudirin rundunar wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a Jihar Taraba.

 

Sai dai, ya bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa sojoji da sauran hukumomin tsaro goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa a ayyukan tsaro da ake gudanarwa a fadin jihar.

 

A wani labari mai nasaba da haka, Kungiyar Matan Sojoji da ‘Yansanda (DEPOWA) ta yaba da jajircewa da sadaukarwar dakarun rundunonin sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro, wadanda ke ci gaba da sadaukar da rayuwarsu domin kare kasar.

 

Kungiyar ta kuma yi addu’a ga Allah domin kare mazajensu, wadanda ke kwana suna tashi a kan bakin aiki domin tabbatar da tsaron ‘yan Nijeriya.

 

Shugabar kungiyar DEPOWA, kuma matar Babban Hafsan Tsaro na Kasa (CDS), Mrs. Oghogho Musa, ta bayyana wannan godiya tare da yin addu’o’i a birnin Abuja yayin gudanar da wasan motsa jiki na rawa (Dance Aerobics Edercise) da aka gudanar a makarantar DEPOWA da ke sansanin Mogadishu.

 

Shugabar DEPOWA ta kuma jaddada kudirin kungiyar na gudanar da yakin addu’a da godiya na tsawon shekara guda ga dakarun da ke bakin daga, domin nuna yabo da godiya ga jajircewarsu wajen kare kasar Nijeriya, duk da hadarin da ke tattare da aikin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara October 11, 2025 Tsaro ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta October 11, 2025 Tsaro Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara October 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano