An kama 26 da ake zargin masu garkuwa da mutane
Published: 9th, October 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ta kama wasu mutane 26 da ake zargi da yin garkuwa da mutane, tare da ƙwato bindigogi guda 4, da muggan makamai da dama.
Ta kuma kama wani ɓangare na kuɗin fansa da ake zargin an biya masu garkuwa da mutane a wasu hari daban-daban a jihar.
Nasarar kamen dai ya biyo bayan wasu jerin samame da jami’an ’yan sanda da na ’yan banga suka yi a tsakanin ranakun 3 zuwa 5 ga watan Oktoban 2025, inda suka yi ta kai farmaki kan gungun masu garkuwa da mutane da ke kai hari a ƙananan hukumomin Anchau, Ikara da kuma Makarfi.
Wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan ya fitar a ranar Alhamis, ta ce samamen da aka gudanar tare da haɗin gwiwar hukumar ’yan banga ta Kaduna, wani ɓangare ne na ƙoƙarin kawar da ’yan bindiga da yin garkuwa da mutane a jihar.
Sanarwar ta ce, an samu nasarar farko ne a ranar 5 ga watan Oktoba, a lokacin da tawagar ’yan sintiri daga reshen Anchau, da ke aikin sahihan bayanan sirri, suka kai farmaki maɓoyar wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da misalin ƙarfe 1:15 na safe, tare da kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a ciki, ciki har da wani Jibrin Abubakar mai suna Oga, mai shekara 21.
“Bincike ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun haɗa baki ne a ranar 22 ga watan Satumba, 2025, don yin garkuwa da wani Idris Adamu mai shekara 60, wanda suka yi garkuwa da shi na tsawon kwanaki kafin su sake shi bayan sun karɓi kuɗin fansa Naira miliyan 5,” in ji Hassan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Masu Garkuwa da mutane masu garkuwa da mutane da ake zargin
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
Rahotanni na cewa ’yan bindiga sun sace wasu mutum takwas a garin Biresawa da ke Karamar Hukumar Tsanyawa ta Jihar Kano a daren jiya na Litinin.
Wata majiyar da ta tabbatar da lamarin ta shaida wa Aminiya cewa maharan sun shiga garin tsakanin 11 na dare zuwa 12 na tsakar dare, inda suka yi awon gaba da maza biyu da mata shida.
’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun TuraiWani ɗan uwa ga waɗanda aka sace, Kabiru Usman, ya ce maharan sun zo ne a ƙafa ɗauke da makamai, suka kuma yi garkuwa da matarsa Umma, ɗiyarsa mai shekara 17, da matar ɗan’uwansa da wasu mata biyu daga Tsundu mai makwabtaka.
Ya ce al’ummar garin sun yi ƙoƙarin daƙile harin amma suka kasa saboda ƙarancin makamai, duk da cewa sun sanar da ’yan sanda da sojoji tun kafin faruwar harin bayan samun bayanan cewa ’yan bindigar na dosar yankin.
Ya roƙi gwamnati ta ɗauki mataki wajen ceto mutanen da aka sace da kuma kare rayukan mazauna yankin.
Aminiya ta yi ƙoƙarin ji ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, sai da har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.