Gwamnatin Kano ta shirya ɗaurin auren ma’aurata 2,000
Published: 9th, October 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta umurci Hukumar Hisba ta jihar da ta fara shirye-shiryen ɗaurin auren ma’aurata aƙalla 2,000 a ƙarƙashin shirinta na ɗaurin auren gata.
Mataimakin babban Kwamandan hukumar, Sheikh Mujahid Aminudeen ya shaida wa kafar PUNCH a wata tattaunawa ta wayar tarho a ranar Alhamis, inda ya ce nan ba da daɗewa ba hukumar za ta fara shirin don ganin an samu nasarar gudanar da taron bikin.
“Muna shirin gudanar da ɗaurin auren wani rukunin ma’aurata guda 2,000 kamar yadda gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta umarta,” in ji shi.
Duk da cewa, babban kwamandan bai bayyana ainihin ranar da za a gudanar da babban taron ba, ya ce akwai hanyoyin da za a bi wajen gudanar da ɗaurin auren.
A cewarsa, duk ma’auratan da suka yi rijistar dole ne su je a duba lafiyarsu domin a tabbatar da lafiyarsu domin a yi musu gwajin cutar ƙanjamau da ciwon hanta da gwajin miyagun ƙwayoyi da dai sauransu.
“Duk ma’auratan da za suke da sha’awar shiga tsarin auren dole ne su yi rajista kafin su shiga taron ɗaurin auren da gwamnati ta shirya.
Sakamakon binciken likitan kuma wani ɓangare ne na tsarin da ake buƙata na gudanar da bukukuwan auren, kuma ya zama dole saboda duk wanda bai gabatar da kansa ba don tantancewar za a kore shi, kai tsaye,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ma aurata ɗaurin auren
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya
Na farko, manufofi da ka’idojin kundin mulkin MDD su kasance tushen ka’idojin dangantakar kasa da kasa, kuma jigon tsarin shari’a na duniya.
Na biyu, dole ne dokokin duniya su mutunta bambancin al’adu da tsare-tsaren shari’a na kasashen duniya, tare da tabbatar da cewa dukkannin kasashe na da matsayi iri daya, kuma ya zama dole a karfafawa kasashe masu tasowa gwiwar yin magana.
Na uku, daidaiton ‘yancin kai ya kasance tushen shari’a ta zamani a duniya.
Na hudu, nuna biyayya ga yarjejeniyoyin kasa da kasa, wata babbar ka’ida ce wajen aiwatar da shari’a a duniya, kuma dole ne dukkannin kasashe su cika alkawuransu bisa aminci da gaskiya.
Na biyar, dole ne kasashe su gaggauta tsara dokoki a sabbin fannonin da sabbin bangarorin tsaro, don samar da tsarin hadin gwiwa da shugabancin duniya a wadannan bangarori, ta yadda za su biya bukatu da kuma magance matsalolin da suka dace da bukatun kasashe.
Na shida, warware rikice-rikice ta hanyar zaman lafiya wata babbar ka’ida ce ta shari’ar duniya, kuma neman sulhu daya ne daga cikin hanyoyin da kundin mulkin MDD ta kayyade na magance rikice-rikice. (Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA