Gwamnatin Kano ta shirya ɗaurin auren ma’aurata 2,000
Published: 9th, October 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta umurci Hukumar Hisba ta jihar da ta fara shirye-shiryen ɗaurin auren ma’aurata aƙalla 2,000 a ƙarƙashin shirinta na ɗaurin auren gata.
Mataimakin babban Kwamandan hukumar, Sheikh Mujahid Aminudeen ya shaida wa kafar PUNCH a wata tattaunawa ta wayar tarho a ranar Alhamis, inda ya ce nan ba da daɗewa ba hukumar za ta fara shirin don ganin an samu nasarar gudanar da taron bikin.
“Muna shirin gudanar da ɗaurin auren wani rukunin ma’aurata guda 2,000 kamar yadda gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta umarta,” in ji shi.
Duk da cewa, babban kwamandan bai bayyana ainihin ranar da za a gudanar da babban taron ba, ya ce akwai hanyoyin da za a bi wajen gudanar da ɗaurin auren.
A cewarsa, duk ma’auratan da suka yi rijistar dole ne su je a duba lafiyarsu domin a tabbatar da lafiyarsu domin a yi musu gwajin cutar ƙanjamau da ciwon hanta da gwajin miyagun ƙwayoyi da dai sauransu.
“Duk ma’auratan da za suke da sha’awar shiga tsarin auren dole ne su yi rajista kafin su shiga taron ɗaurin auren da gwamnati ta shirya.
Sakamakon binciken likitan kuma wani ɓangare ne na tsarin da ake buƙata na gudanar da bukukuwan auren, kuma ya zama dole saboda duk wanda bai gabatar da kansa ba don tantancewar za a kore shi, kai tsaye,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ma aurata ɗaurin auren
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
Daga Usman Muhammad Zaria
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bukaci maniyyatan aikin hajjin 2026 da su gaggauta biyan kudin kujerun su kafin ranar 24 ga watan gobe.
Darekta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka jim kadan bayan kammala taro da shugabannin sassa na hukumar da shugabannin shiyya da sauran ma’aikatan hukumar a Dutse babban birnin jihar.
Yana mai cewar, hukumar aikin hajji ta kasa wato NAHCON ta bayyana ranar 5 ga watan Disamba da ta kayyade a matsayin ranar rufe biyan kudin kujerun aikin Hajjin 2026 a fadin kasar nan.
Ya bayyana cewar ranar itace ranar karshe da hukumar aikin Hajji da Umrah ta kasar Saudiyya ta kayyade na biyan kudin kujerun domin maniyyatan da za su sauke farali.
Alhaji Ahmed Umar Labbo, yayi nuni da cewar, a duk fadin kasar nan jihar Jigawa ce kadai ta sami ranar 24 ga watan gobe sakamakon karamci da Gwamna Umar Namadi ya yiwa hukumar na bada lamunin sama da naira miliyan dubu 3 domin kebe kujerun jihar a aikin Hajjin 2026.
Kazalika, ya kara da cewar babu wata jihar da ta sami karamci da tagomashi wajen alkinta kujerun maniyyata fiye da jihar Jigawa.
A don haka, Labbo ya bukaci maniyyata da su gaggauta biyan kudin kujerun su ta hannun shugabannin shiyya ko kuma a shelkwatar hukumar dake Dutse nan da makwanni 4.
Ya kuma kara jaddada kudurinsa na rike kambun hukumar wajen tabbatar da kula da jin dadin alhazai da walwalar su tun daga gida Najeriya har zuwa kasa mai tsarki.
Ahmed Umar Labbo ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa karamcin da yake yiwa hukumar na bada lamunin kudi domin tare kujerun alhazan jihar da sauran ayyukan hukumar domin gudanar da aikin Hajji ingantacce.