Aminiya:
2025-10-13@14:54:49 GMT

’Yan sanda sun kama wanda ake zargi da sace hakimi a 2023 a Kano

Published: 4th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama wani mutum da ake zargi da hannu wajen sace Hakimin Garin Garun Babba, Alhaji Abdulmumini Mudi Zakari, a shekarar 2023.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Asabar.

Gwamna Namadi ya raba wa mata 1,400 tallafin kayan ɗinkin hula a Jigawa Dalilin da ya sa na tsere Kamaru bayan Boko Haram ta ƙone fadata a Borno — Basarake

Ya ce an kama wanda ake zargin mai suna Usman Lawan Baba, wanda aka fi sani da “Yellow,” mai shekara 27, a ranar 2 ga watan Oktoba, 2025, a garin Dakatsalle da ke Ƙaramar Hukumar Bebeji.

Wanda ake zargin tare da wasu sun sace hakimin sannan suka ƙwace masa kuɗi har Naira miliyan 2.75, waya ƙirar Tecno Kevo 4 da kuma agogo.

Daga baya ’yan sanda sun ceto hakimin bayan sun fatattaki ’yan bindigar.

Yayin gudanar da bincike, Baba, ya amsa cewa yana daga cikin waɗanda suka aikata laifin, inda ya bayyana cewa Naira 6,000 aka ba shi a matsayin rabonsa.

Ya kuma bayyana sunayen wasu daga cikin abokan aikinsa.

Wasu daga cikinsu sun muty a hannun jami’an tsaro a yayin wasu samame da aka kai, kamar su Bello Kici-Kici daga Doguwa da Mallam Sale daga Gezawa.

Wani kuma mai suna Ruwa Shehu daga Bebeji, yana gidan yari bayan samun sa da laifin satar mutane.

Sauran da suka haɗa da Ibrahim Gwanja da Sule Naye har yanzu ana ƙoƙarin gano inda suka shiga.

’Yan sanda sun ce za a gurfanar da Baba a kotu bayan an kammala bincike.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yaba wa rundunar da ke yaƙi da garkuwa da mutane, bisa jajircewarsu, tare da gode wa jama’a kan goyon bayan suke bai wa jami’an tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya October 10, 2025 Labarai Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara October 10, 2025 Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • 2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe