Aminiya:
2025-10-13@17:53:41 GMT

Isra’ila ta kai hare-hare a Gaza duk da kiran Trump na tsagaita wuta

Published: 4th, October 2025 GMT

Hukumar kashe gobara ta yankin Gaza ta ce a ranar Asabar, sojojin Isra’ila sun kai hare-hare da dama a birnin Gaza duk da kiran da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi na a dakatar da luguden wuta bayan ƙungiyar Hamas ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta.

A ranar Asabar din nan da karfe 6 na yamma wa’adin da Trump ya bayar na cimma yarjejeniyar zaman lafiyar take cika.

“Dare ne mai tsanani ƙwarai, inda sojojin Isra’ila suka kai hare-haren sama da harbin manyan bindigogi da dama a birnin Gaza da wasu yankuna na zirin, duk da kiran Shugaba Trump na a dakatar da luguden bama-bamai,” in ji kakakin hukumar kashe gobara ta Gaza, Mahmud Bassal, yayin tattaunawa da kamfanin Dillancin Labarai na AFP.

Bassal, wanda ke jagorantar ƙungiyar agaji da ke ƙarƙashin ikon Hamas, ya ce gidaje 20 ne suka rushe sakamakon hare-haren da aka kai cikin dare.

’Yan bindiga sun ƙaƙaba wa ƙauyuka harajin N10m a Neja Wata mata ta banka wa kanta wuta a Bauchi

“Yanayin ya yi tsanani ƙwarai a birnin Gaza,” in ji shi, yana mai ƙarawa da cewa ƙungiyarsu ba ta iya isa ga dukkan mutanen da abin ya shafa ba saboda “tankoki da kuma ci gaba da luguden wuta.”

Da AFP ta tuntuɓi rundunar sojin Isra’ila, ta ce tana “bincike” rahotannin hare-haren da aka kai cikin dare a Gaza.

Shirin zaman lafiya da Shugaba Trump ya gabatar a wannan makon, tare da goyon bayan Fira Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ƙunshi tsagaita wuta, sakin fursunonin da ake rike da su cikin sa’o’i 72, ajiye makaman Hamas da kuma janye sojojin Isra’ila a hankali daga Gaza.

Hamas ta bayyana a ranar Juma’a cewa tana shirye ta saki fursunonin da ke hannunta bisa shirin Trump, amma ta nemi a tattauna cikakkun bayanai tare da samun damar ba da gudummawa a tattaunawar kan makomar yankin Falasɗinu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza

Rahotanni sun bayyana cewa an gano daruruwan gawawwaki a karkashin burabutsai a yankin gaza bayan sanar da dakatar da bude wuta tsakanin isra’ila da kuma kungiyar Hamas, adadai lokacin da tawagar agaji ke ci gaba da gano gawarwaki da suka makale a karkashin duwatsu bayan kwashen shekaru 2 Isra’ila na kisan kare dangi,

Majiyar Asibiti a yankin Gaza ta sanar a yau litinin cewa akalla an gano gawarwakin mutane 323 da suke karkashin burabutsai,  kuma har yanzu akwai gawarwarki sama da 10,000 da ke karkashin gine –gine da aka rusa a yankin Gaza.

Bisa kidddigar da majalisar dinkin duniya ta gabatar ya nuna cewa an rusa gidaje 430,000 a yankin Gaza sakamakon hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kai wa, tun bayan da ta shelanta yaki kan gaza a watan oktoban shekara ra 2023 da ta gabata,

Daga lokacin Isra’ila ta kaddamar da hari a yankin Gaza kimanin mutane 67806 ne suka rasa rayukansu yayin 17066 kuma suka jikkata mafiyawancinsu mata ne da yara kanana, kamar dai yadda ma’aikatar lafiya ta yankin gaza ta sanar.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tehran Ta yi Gargadi Game Da  Barazanar Yaduwar Fadan Iyakar Afghanisatan Da Pakistan. October 13, 2025 Kungiyar (ASUU) Ta Sanar Da Shiga Yajin Aikin  Gargadi A Kasa Baki Daya . October 13, 2025 Aragchi: HKI Ba Zata Mutunta Tsaida Wuta A Gaza Ba October 13, 2025 Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza October 13, 2025 Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh October 13, 2025 An Fara Musayar Fursinoni Tsakanun Hamas Da HKI A Safiyar Yau Litini October 13, 2025 Falasdinawa Sun Gano Gawakin Wadanda HKI Ta Kashe A gaza  Fiye Da 320 Cikin Kwanaki Biyu Kacal October 13, 2025 Iran Ba Zata Halarci Zaman Taron Sharm El-Sheikh Ba Saboda Wasu Dalilai Da Ta Bayyana October 13, 2025 Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta October 13, 2025 Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta October 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza
  • Aragchi: HKI Ba Zata Mutunta Tsaida Wuta A Gaza Ba
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a Masar ranar Litinin  
  • Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza.
  • HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta
  • Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza
  • Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa