Leadership News Hausa:
2025-10-13@17:53:40 GMT

Jami’an Tsaro Sun Ceto Fasinjoji 8 Da Aka Sace A Kogi

Published: 28th, September 2025 GMT

Jami’an Tsaro Sun Ceto Fasinjoji 8 Da Aka Sace A Kogi

Jami’an tsaro a Jihar Kogi sun ceto mutane takwas daga cikin fasinjojin da aka yi garkuwa da su har 12 a hanyar Okene–Auchi.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ƴansanda ta jihar, William Aya, ya tabbatar da faruwar lamarin a Lokoja ranar Asabar. Ya bayyana cewa fasinjojin suna tafiya ne a cikin motar haya ta Big Joe mai lambar Edo FUG 13 XY daga Abuja zuwa Benin, da Jihar Edo, kafin ƴan bindiga su tare su a hanya.

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

Aya ya ce rahoton sace Fasinjoji yana shigowa, DPO na Okene, Nasir Muhammad, tare da haɗin gwuiwar Sojoji da ƙungiyar sa-kai, suka ƙaddamar da sintiri wanda ya kai ga kuɓutar da mutane takwas ciki har da direban motar.

Ya ƙara da cewa ana cigaba da ƙoƙarin ceto sauran mutane huɗun da ke hannun masu garkuwa da su, tare da tabbatar da cewa za a kamo waɗanda suka aikata wannan ta’asa domin fuskantar hukunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin Kogi

এছাড়াও পড়ুন:

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

Gidajen mai da dam aka rufe, yayin da wadanda suka kasance da dan sauran mai kuma, layuka ne marasa iyaka suka makare su, lamarin da ta kai har kwana mutane ke yi a gidajen man.

 

A kan titunan babban birnin kasar, bayanai sun ce ba kasafai ake ganin motoci suna kai komo ba, ko kuma mutane na tura babura, bisa alama dai mutane sun ajiye ababen hawansu a gida.

 

Sai dai duk da wannan karancin man da ake fama da shi, farashinsa ya ci gaba da kasancewa a yanda yake, domin kuwa farashin lita na mai CFA 775 yayin da dizal yake akan CFA 725.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba October 12, 2025 Manyan Labarai An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro October 12, 2025 Manyan Labarai Trump Da Al-Sisi Za Su Jagoranci Taron Zaman Lafiya Dawwamammiya Ta Gaza A Masar October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara