Tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya yi zargin cewa, cikin watanni shida, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya samu karin kaso daga gwamnatin tarayya fiye da yadda ya samu a cikin shekaru 8 da ya yi yana gwamna. Batun rabon kuɗaɗen wata-wata ga Jihohin dai ya zama abun muhawara a karkashin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa? Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano “A yau zan iya bugun ƙirjina kuma kowanne daga cikin gwamnonin nan zai iya tabbatar da cewa, rabon da ake bai wa jihohin ya ninka sau uku, kuma akwai l isassun kuɗaɗe daga ƙananan hukumomi.” in ji Ganduje Da yake jawabi bayan wani taron masu ruwa da tsaki a Kano, Ganduje ya bayyana cewa, ya nuna shakku kan nasarorin da magajin nasa ya samu, inda ya ce gwamnatin Yusuf na kashe kuɗi ba tare da wani lissafi ba. Tsohon gwamnan, ya ƙara da cewa, “lokacin da na karɓi mulki, ban taɓa ɓata lokaci ba wajen binciken magabatana, gwamnati tana da yawa, sai dai ka gama ka mika wa wani, amma Abba Yusuf ya fara gwamnatinsa da bincike. “Ku gaya mani, me suka bankaɗo? Sun samu kuɗi a cikin watanni shida fiye da yadda gwamnatina ta samu a cikin shekaru takwas. To amma, wacce nasara suka samu?”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi

A ranar Alhamis, 27 ga watan Nuwamban 2025 ce Allah ya yi wa fitaccen malamin addinin Musuluncin nan kuma jigo a Darikar Tijjaniyya a Najeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi rasuwa.

Ya rasu yana da sama da shekaru 100 a duniya.

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani

Baya ga tarin iliminsa da yawan shekaru, akwai wasu tarin baiwa da Allah Ya ba malamin, wadanda ba kowa ne ya san da su ba.

Aminiya ta yi nazari a kansu, inda ta zakulo muku abubuwa 18 da ya kamata ku sani a kansa.

Ga wasu daga ciki:

Ya fi kowa yawan zuri’ar da ta haddace Alkur’ani a duniya, inda yake da ’ya’ya da jikoki da tataba-kunne kusan 300 da suka haddace Alkur’ani mai girma Kundin tattara bayanai na Cholan Book Of World Records, ya ba shi shaidar girmamawa saboda yawan zuri’a mahaddata Yana da ’ya’ya 95 Yana da jikoki 406 Yana da tattaba-kunne 100 ’Ya’yansa mahaddata Alkur’ani 77 Jikokinsa mahaddata Alkur’ani 199 Tattaba-kunnensa mahaddata Alkur’ani 12 Shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Koli da ke bayar da fatawa a addinin Musulunci a Najeriya An haife shi a watan Janairun 1927, wanda ya yi daidai da watan Muharram 1346 Bayan Hijira A ranar Laraba aka haife shi a a garin Nafada da ke Jihar Gombe a yanzu Kwararre ne a fannin Alkur’ani da Tafsiri da Ma’arifa da Hadisi da Harshen Larabci da Li’irabi da Fikihu Jami’ar Tarayya da ke Lafiya a Jihar Nasarawa ta ba shi Digirin girmamawa Gwamnatin Najeriya ta ba shi lambar girmamawa ta kasa ta OFR Ya musuluntar da dubban mutane Yakan yi saukar Alkur’ani duk bayan kwana biyu Mutane fiye da 140,924 suka haddace Alkur’ani a makarantunsa da ke fadin Najeriya Ya kafa makarantun haddar Alkur’ani sama da 1,500 a Najeriya da wasu kasashen Afirka Karkashin gidauniyasa, an gina dakunan karatu guda 133,060 a Arewacin Najeriya Ya shafe shekaru sama da 50 yana gabatar da tafsirin Alkur’ani a cikin watan Ramadan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi
  • Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano