Aminiya:
2025-11-27@21:48:31 GMT

‘Yan fashi sun sace mutum 17 a mahadar tekun Akwa Ibom da Kuros Riba

Published: 28th, September 2025 GMT

Wasu mutane da ake kyautata zaton ‘yan fashin teku ne sun yi awon gaba mutum 17 a wani kwale-kwale da ke kan iyakar teku a jihohin Akwa Ibom da Kuros Riba.

Lamarin ya faru ne a lokacin da fasinjojin suka taso daga wani ƙauye a kan iyakar jihohin biyu, inda ‘yan fashin suka afka wa kwale-kwalen a cikin nasu jirgin ruwa, sannan suka yi awon gaba da fasinjoji 17.

Matatar Dangote ta ci gaba da sayar da man fetur a naira Nukiliya: MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkuman karayar tattalin arziki

Kwale-kwalen na wani kamfani ne da ke aikin jigilar fasinjoji tsakanin jihohin biyu a kan teku.

A ‘yan shekarun baya matsalar satar mutane da garkuwa da su ta yi ƙamari a yankin, amma daga baya ta lafa.

Sai dai alamu na nuna cewa lamarin yana neman sake dawowa a kudancin ƙasar, haɗi da matsalar safarar yara zuwa ƙasashen waje domin kai su aikatau.

Rundunar ’yan sandan Kuros Riba ta tabbatar wa Aminiya faruwar lamarin ta hannun mataimakin mai magana da yawunta, DSP Igri Ewa.

A cewar DSP Ewa, “Gaskiya ne lamarin ya faru ranar Alhamis, amma jami’anmu na iya bakin ƙoƙari wajen bincike domin gano wadanda aikata wannan laifi da kuma inda aka ɓoye mutanen.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashi Akwa Ibom

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta bayyana sabbin nasarorin da ta samu wajen yaƙi da laifuka a jihar, ta hanyar holen mutum 34 da ta kama da aikata laifuka daban-daban.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Rabi’u Muhammad, ya ce wannan ci gaba ya samu ne saboda sabbin dabarun aiki da kuma bayanan sirri da aka samu daga al’umma da hukumomin tsaro.

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

A Anguwar Barnawa da wasu wurare a Kaduna, rundunar Operation Fushin Kada ta kama mutane 13 da ake zargi da aikata fashi da makami da satar wayoyi a otel-otel da gidaje.

An ruwaito sun taɓa kashe ɗan sanda a shekarar 2024, kuma suna samun bayanai daga dilolin miyagun ƙwayoyi a wuraren shaƙatawa. A

An ƙwato bindiga ƙirar gida, gatari da adduna 13, mota, kwamfuta huɗu, wayoyi 13 da talabijin huɗu.

Haka kuma, a Nunbu Bashayi da ke Sanga, an kama mutane bakwai da ake zargi da garkuwa da mutane tare da neman kuɗin fansa.

Dukkanimsu sun amsa laifinsu kuma ana neman ragowar waɗanda suke tsere.

A wani samame daban, ’yan sanda sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da aikata fashi, fyaɗe da damfara.

Sun saba kai hari gidajen mutane, ɗaukar kuɗaɗen mutane, aikata fyaɗe sannan su riƙa ɗaukar bidiyo tsoratar da mutane.

A Zariya kuwa, an kama wasu mutane tara da suka haɗa da maza da mata waɗanda ake zargi da yi wa direban Adaidaita sahu fashi ta hanyar zuba masa magani a abin sha.

Rundunar ta kuma kama wani likitan bogi mai suna Adamu Abubakar Muhammed wanda ya yi wa mutane tiyata ba tare da shaidar karatun likitanci ba.

Ya yi amfani da takardun bogi wajen yin aiki na tsawon wata guda kafin a gano shi.

Kwamishinan, ya ce duk waɗanda aka kama suna hannun rundunar, kuma za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike.

Ya gode wa jami’an tsaro da al’umma kan haɗin kai, inda ya yi da a ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin inganta tsaro a jihar da ƙasa baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina