Aminiya:
2025-10-13@17:53:41 GMT

‘Yan fashi sun sace mutum 17 a mahadar tekun Akwa Ibom da Kuro Riba

Published: 28th, September 2025 GMT

Wasu mutane da ake kyautata zaton ‘yan fashin teku ne sun yi awon gaba mutum 17 a wani kwale-kwale da ke kan iyakar teku a jihohin Akwa Ibom da Kuros Riba.

Lamarin ya faru ne a lokacin da fasinjojin suka taso daga wani ƙauye a kan iyakar jihohin biyu, inda ‘yan fashin suka afka wa kwale-kwalen a cikin nasu jirgin ruwa, sannan suka yi awon gaba da fasinjoji 17.

Matatar Dangote ta ci gaba da sayar da man fetur a naira Nukiliya: MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkuman karayar tattalin arziki

Kwale-kwalen na wani kamfani ne da ke aikin jigilar fasinjoji tsakanin jihohin biyu a kan teku.

A ‘yan shekarun baya matsalar satar mutane da garkuwa da su ta yi ƙamari a yankin, amma daga baya ta lafa.

Sai dai alamu na nuna cewa lamarin yana neman sake dawowa a kudancin ƙasar, haɗi da matsalar safarar yara zuwa ƙasashen waje domin kai su aikatau.

Rundunar ’yan sandan Kuros Riba ta tabbatar wa Aminiya faruwar lamarin ta hannun mataimakin mai magana da yawunta, DSP Igri Ewa.

A cewar DSP Ewa, “Gaskiya ne lamarin ya faru ranar Alhamis, amma jami’anmu na iya bakin ƙoƙari wajen bincike domin gano wadanda aikata wannan laifi da kuma inda aka ɓoye mutanen.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashi Akwa Ibom

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

Uba ya ce dakarun sun ci gaba da bincike da fatattakar ƴan ta’addan don hana su sake samun damar motsi a yankin Arewa maso Gabas.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe October 11, 2025 Tsaro Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba October 11, 2025 Tsaro Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza
  • Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya