Aminiya:
2025-10-13@17:53:39 GMT

Mutum 7 sun rasu yayin da tirela ta murƙushe motoci a Madalla

Published: 27th, September 2025 GMT

Aƙalla mutum bakwai ne suka rasu, yayin da wasu guda biyar suka ji rauni bayan wata tirela ta murƙushe motoci biyu a yankin Madalla, da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, a Jihar Neja.

Hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 11:30 na safiyar ranar Juma’a, lokacin da wata tirela ta samu matsalar birki, ta yi awon gaba da wasu motoci biyu.

’Yan uwa sun samu Digiri Mai Daraja ta Ɗaya a fanni iri ɗaya  Matatar Ɗangote ta dakatar da sayar da fetur a farashin Naira

Wani ganau, Saleh Haruna, ya ce kafin aukuwar hatsarin, direban wata motar bas ya bugi wata mota a gabansa, wanda hakan ya haddasa hatsaniya.

A cewarsa, a lokacin ne tirelar ta taho da sauri ta murƙushe su, hakan ya sa wani ɓangare na bas ɗin ya kama da wuta.

A sakamakon haka, mutum huɗu da ke cikin bas ɗin sun ƙone ƙurmus, yayin da sauran suka samu rauni.

An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitin Lukas da ke Madalla, inda Dakta Ugwoegbu Valentine, ya tabbatar da rasuwar ƙarin mutum uku daga cikin waɗanda suka ji rauni.

Direban tirelar, Sulaiman Rabiu, ya shaida cewa ya taso daga Warri, a Jihar Delta, yana ɗauke da buhun alkama waɗanda zai kai Kano.

Ya ce lokacin da yake saukowa daga Madalla ne birkin motarsa ya ƙi aiki, lamarin da ya janyo hatsarin.

Rundunar ’yan sandan yankin Madalla ta tabbatar da rasuwar mutum bakwai a hatsarin.

Sai dai jama’a a yankin sun koka kan yadda aikin gyaran hanyar Abuja zuwa Kaduna ke tafiya.

Sun zargi kamfanin da ke aikin da gazawa wajen saka alamomi da samar da wuraren tsayawar fasinjoji da motoci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hatsari

এছাড়াও পড়ুন:

Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan yadda shugaba Bola Tinubu ya yi wa wasu mutane afuwa, ciki har da waɗanda suka aikata manyan laifuka.

A cikin saƙon da Atiku ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ana yin afuwa ne ga waɗanda aka yi wa rashin adalci ko waɗanda suka nema gafara bayan sun shafe wani lokaci a gidan yari.

Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna

Ya ce a wannan karon an yi wa masu safarar ƙwayoyi, masu garkuwa da mutane, masu kisan kai, da kuma masu cin hanci da rashawa afuwa.

Atiku, ya ce abin mamaki ne yadda gwamnati ke yafewa irin waɗannan mutane, a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsaro da lalacewar tarbiyya, musamman tsakanin matasa masu shan miyagun ƙwayoyi.

Ya ce bincike ya nuna cewa kashi 29 na waɗanda aka yi wa afuwa suna da alaƙa da hakrar miyagun ƙwayoyi, yayin da Najeriya ke ƙoƙarin wanke sunanta a idon duniya kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi.

Atiku, ya ce maimakon wannan afuwa ta zama darasi ga masu laifi, ta zama hanyar durƙusa da ɓangaren shari’a da jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu wajen kamawa da hukunta masu aikata laifuka.

Ya ƙara da cewa idan gwamnati ta fara yafe wa masu laifi, hakan zai rage ƙimar shugabanci kuma ya ƙarfafa wa masu aikata laifuka su ci gaba da aikata su.

Atiku ya jaddada cewa Najeriya tana buƙatar  shugabanci na gari wanda zai tabbatar da adalci a shari’a, ba tare da nuna bambanci ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano