Aminiya:
2025-11-27@21:12:45 GMT

Ruftawar ƙasa ta kashe masu haƙar ma’adinai 4 a Filato

Published: 27th, September 2025 GMT

Mutum huɗu sun rasa rayukansu sakamakon ruftawar da ramin da suke hakar ma’adanan ya yi, a Unguwar Dura da ke Ƙaramar hukumar Jos ta Kudu a Jihar Filato.

Mai taimaka wa gwamnan Filato Caleb Mutfwang kan harkokin ma’adanai, Solomon Dung ya bayyana cewa, “Daga abin da aka gaya min, wasu matasa maza suna aiki a cikin wani ramin haƙar ma’adinai, kwatsam ƙasa ta ruguje kan huɗu daga cikinsu.

“Uku suka mutu nan take, kuma an kai wani mutum guda asibiti, kuma abin takaici shi ma daga baya ya mutu.”

A cewar shaidun gani da ido, lamarin ya faru ne a daren ranar Alhamis ɗin nan da ta gabata.

Wani mazaunin Unguwar, Chuwang Davou ya shaida wa manema labarai a Jos cewa, “Eh, muna da cikin wani mummunan yanayi a Unguwar Dura, wani wurin haƙar ma’adinai ya ruguje a daren ranar Alhamis.

“Ban san adadin waɗanda suka mutu ba, amma ina tabbatar muku da cewa akwai wasu mutane a cikin ramin, lokacin da lamarin ya faru.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haƙar ma adinai ruftawar

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bukaci maniyyatan aikin hajjin 2026 da su gaggauta biyan kudin kujerun su kafin ranar 24 ga watan gobe.

Darekta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka jim kadan bayan kammala taro da shugabannin sassa na hukumar da shugabannin shiyya da sauran ma’aikatan hukumar a Dutse babban birnin jihar.

Yana mai cewar, hukumar aikin hajji ta kasa wato NAHCON ta bayyana ranar 5 ga watan Disamba da ta kayyade a matsayin ranar rufe biyan kudin kujerun aikin Hajjin 2026 a fadin kasar nan.

Ya bayyana cewar ranar itace ranar karshe da hukumar aikin Hajji da Umrah ta kasar Saudiyya ta kayyade na biyan kudin kujerun domin maniyyatan da za su sauke farali.

Alhaji Ahmed Umar Labbo, yayi nuni da cewar, a duk fadin kasar nan jihar Jigawa ce kadai ta sami ranar 24 ga watan gobe sakamakon karamci da Gwamna Umar Namadi ya yiwa hukumar na bada lamunin sama da naira miliyan dubu 3 domin kebe kujerun jihar a aikin Hajjin 2026.

Kazalika, ya kara da cewar babu wata jihar da ta sami karamci da tagomashi wajen alkinta kujerun maniyyata fiye da jihar Jigawa.

A don haka, Labbo ya bukaci maniyyata da su gaggauta biyan kudin kujerun su ta hannun shugabannin shiyya ko kuma a shelkwatar hukumar dake Dutse nan da makwanni 4.

Ya kuma kara jaddada kudurinsa na rike kambun hukumar wajen tabbatar da kula da jin dadin alhazai da walwalar su tun daga gida Najeriya har zuwa kasa mai tsarki.

Ahmed Umar Labbo ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa karamcin da yake yiwa hukumar na bada lamunin kudi domin tare kujerun alhazan jihar da sauran ayyukan hukumar domin gudanar da aikin Hajji ingantacce.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran