NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya
Published: 27th, September 2025 GMT
A wani labarin kuma, Jami’an NDLEA sun kama wata ‘yar kasuwa mai shekaru 38, Okolonkwo Ebere Theresa, a ranar Lahadi, 14 ga watan Satumba, bayan da jami’an tsaron jiragen sama na hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta Nijeriya tare da hadin gwiwar jami’an hukumar NDLEA suka gano 1.40kg na methamphetamine da ta boye a cikin rigarta domin shiga jirgin saman Katar.
A tashar NAHCO da ke filin jirgin saman Legas a ranar Litinin, 15 ga Satumba, NDLEA ta kama wani kayyakin abinci mai kunshe da dauri 40 na methamphetamine mai nauyin kilogiram 2.30 wanda ya nufi Hong Kong ta hanyar jirgin saman Turkish Airlines. An kama wani da ake zargi mai shekaru 59, Umelo Ifeanyi Benatus, wanda ya gabatar da kayan.
“A ranar Alhamis, 18 ga watan Satumba, jami’an da ke aiki a wani kamfanin jigilar kayayyaki da ke Legas sun kama wani kaya da aka shirya zuwa Turai, cajar waya guda bakwai da aka nufi New Zealand, an gano dauke da hodar iblis gram 257.
A wajen Legas hukumar NDLEA ta kai wasu manyan samame. A Adamawa, an gano kwayoyin Tramadol 233,800 a wasu ayyuka guda uku.
Kusan kwayoyi 196,000 aka jefar cikin wata mota kirar Toyota Sienna da ke Mayo Belwa, yayin da aka kama wata da ake zargi mai suna Rita Zira a Jambutu, Yola, tare da boye kwayoyi 27,900 a cikin dakin kwananta. Wani wanda ake zargi mai suna Halilu Abubakar, mai shekaru 22, an kama shi ne a shingen bincike na Namtari dauke da kwayoyi 10,300,” in ji sanarwar.
A Jihar Zamfara, jami’an tsaro da ke samun goyon bayan jami’an tsaro sun kama buhuna 109 na skunk mai nauyin kilogiram 1,099.4 a cikin wata mota kirar Mitsubis
Sauran abubuwan da aka kama sun hada da capsules na tramadol 14,000 da aka kwato daga hannun wasu mutane biyu a hanyar Damaturu zuwa Potiskum a Yobe, da kuma buhu uku na skunk mai nauyin kilogiram 25.5 da aka kwato daga hannun Anas Hamisu mai shekaru 28 a Taraba.
A Jihar Edo, hukumar NDLEA ta lalata gonakin tabar wiwi guda biyu da ke da sama da hekta hudu a dajin Atororo, Karamar Hukumar Owan ta Yamma, wanda aka kiyasta yawansu ya kai kilogiram 11,330.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: mai shekaru
এছাড়াও পড়ুন:
Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
’Yan wasan tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya ta Mata, Super Falcons, sun yi barazanar ƙaurace wa wasannin sada zumunta da Najeriya za ta buga a watan Disamba mai kamawa.
’Yan wasan sun ce za su ƙaurace wa wasannin ne idan har Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta ci gaba da jinkirta biyan kuɗaɗen alawus-alawus da suke biyo tun na Gasar Olympics da aka yi a birnin Paris a 2024.
Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaroWasu majiyoyi daga ƙungiyar sun tabbatar cewa ’yan wasan na ci gaba da jiran a biya su haƙƙoƙinsu na wasannin da suka buga, ciki har da alawus na nasarar da suka samu a gasar Olympics, duk da cewa Najeriya ta fice tun a matakin rukuni bayan shan kashi a hannun Brazil da Spain da Japan.
Wani jami’in tawagar, wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya ce ’yan wasan gaba ɗaya sun amince cewa ba za su halarci kowanne wasa ba muddin ba a biya su haƙƙoƙinsu ba.
Ana sa ran Najeriya za ta buga jerin wasannin sada zumunta daga ranar 2 zuwa 10 ga watan Disamba, a wani ɓangare na shirye-shiryen Super Falcons domin tunkarar gasar cin Kofin Afrika ta Mata na 2026.
A halin yanzu, NFF ba ta fitar da jerin sunayen ’yan wasan da za su wakilci Najeriya a wasannin ba.