Zargin ɓatanci: Kwamitin Shura na Kano ya fara sauraron koke-koke kan Malam Triumph
Published: 26th, September 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta miƙa ƙorafe-ƙorafen da aka yi a kan Malam Shu’aibu Abubakar, wanda aka fi sani da Triumph, ga Kwamitin Shura na Jihar don ɗaukar matakin da ya dace.
Sakataren Gwamnatin Jihar ne, ya tura ƙorafe-ƙorafen a ranar Juma’a, inda kwamitin ya fara zama domin sauraronsu.
’Yan Najeriya da tauraronsu ya haska a Ballon d’Or Yadda ’yan haya za su samu ragin N500,000 a shekaraA cewar kwamitin, za a gayyaci masu ƙorafi da Malam Triump domin su gabatar da hujjoji.
Masu ƙorafi za su fayyace abubuwan da suke tuhumar malamin, yayin da shi kuma za a ba shi damar kare kansa.
Bayan haka kwamitin zai tattauna bisa ƙa’idojin shari’ar Musulunci.
Sakataren kwamitin, Shehu Wada Sagagi, ya shaida wa manema labarai cewa an yi hakan ne domin tabbatar da adalci.
“Bayan mun saurari ɓangarorin biyu, kwamitin zai tattauna sannan ya bai wa gwamnatin jiha shawarwari,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin masu ƙorafin sun yi barazanar kai ƙara kotu, amma ya roƙe su da su bari kwamitin Shura ya yi aikinsa.
“Muna kira ga jama’a da su ci gaba da zama cikin lumana. Kano na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewa maso Yamma, kuma wajibi ne mu kiyaye wannan zaman lafiya don ci gaban tattalin arziƙi da zamantakewa,” in ji shi.
Sagagi ya ce kwamitin ya ƙunshi manyan malamai da suka ƙware a fannin shari’ar Musulunci, kuma za su bai wa gwamnati shawarar da ta dace.
Aminiya ta ruwaito cewa, cikin tuhumar da ake yi wa Malam Triump har da kalaman ɓatanci a kan Fiyayyen Hallita, Annabi Muhammad (SAW), yin tambaya kan haihuwarsa, da kuma cewa iyayensa suna cikin wuta.
Har ila yau, masu ƙorafin sun ce yana yin wasu maganganu da suka ɗauke su a matsayin raini.
Kwamitin ya yaba wa gwamnatin jihar na bai ba shi damar warware matsalar ta hanyar tsarin Musulunci, maimakon a bari ya haddasa tashin hankali a cikin jama’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɓatanci Kwamitin Shura Malam Lawan Triumph zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
Al’ummomin dake garin Warwade da kewaye a karamar hukumar Dutse ta jihar Jigawa sun yi kira ga gwamnatin jihar da ta yashe madatsar ruwa ta Warwade wanda ta kasance daya daga cikin hanyar samun aikin dogaro da kai ga Mazauna yankin.
Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya ziyarci al’ummomin da ke zaune a kusa da mmadatsr ruwan wanda aka gina ta sama da shekaru hamsin da suka gabata.
Madatsar ruwan ta Warwade ta kasance hanyar samun sana’o’in dogaro da kai ga mazauna yankin, wadanda suke kamun kifi da noman rani domin samun na yau da kullum.
Malam Umar Sani, wanda masunci ne a Warwade, yace da abin da yake samu daga kamun kifi yake kula da iyalan shi da kuma sauran bukatun yau da kullum.
Yace ana samun ribar kimanin naira dubu goma zuwa ashirin a kowace rana daga siyar da kifin ga matafiya da kuma baki masu kai ziyara garin.
A don haka, Umar yayi kira ga gwamnatin jihar Jigawa da ta yi yashen madatsar ruwan saboda a samu karin kifaye da kuma ruwa da za a iya amfani da shi domin noman rani.
Shi ma a yayin tattaunawa da Dagacin Warwade, Malam Musa Ado, ya ce madatsar ruwan tana samar da ayyukan yi ga matasan yankin, tare da hana tafiya zuwa cirani a sauran yankunan kasar nan da sunan yin sana’o’i.
Ya ce matasan yankin suna gudanar da sana’ar kamun kifi da kuma nomar rani da ta damina.
Sai dai kuma, Malam Musa ya koka kan rashin samar da injinan noman rani da kuma Malaman gona kamar yadda ake yi a gwamnatocin baya.
Kazalika, yace a ‘yan kwanakin baya gwamnatin jihar Jigawa ta kai ziyara kauyen inda ta sanar da cewar Bankin duniya zai samar da wasu kudade ta hannun gwamnatin tarayya wanda za’a baiwa gwamnatocin jihohi domin yashewa tare da gina burtuloli da hanyoyin noman rani.
Bisa haka ne dagacin yayi kira ga gwamnatin jihar da ta fara yin garambawul a madatsar ruwan domin a baiwa mazauna yankunan damar amfani da shi.
A shekarun baya dai, gwamnatin jihar Jigawan ta samar da irin kifaye guda dubu Dari uku domin inganta samar da kifi a yankin.
Usman Mohammed Zaria