Zargin ɓatanci: Kwamitin Shura na Kano ya fara sauraron koke-koke kan Malam Triumph
Published: 26th, September 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta miƙa ƙorafe-ƙorafen da aka yi a kan Malam Shu’aibu Abubakar, wanda aka fi sani da Triumph, ga Kwamitin Shura na Jihar don ɗaukar matakin da ya dace.
Sakataren Gwamnatin Jihar ne, ya tura ƙorafe-ƙorafen a ranar Juma’a, inda kwamitin ya fara zama domin sauraronsu.
’Yan Najeriya da tauraronsu ya haska a Ballon d’Or Yadda ’yan haya za su samu ragin N500,000 a shekaraA cewar kwamitin, za a gayyaci masu ƙorafi da Malam Triump domin su gabatar da hujjoji.
Masu ƙorafi za su fayyace abubuwan da suke tuhumar malamin, yayin da shi kuma za a ba shi damar kare kansa.
Bayan haka kwamitin zai tattauna bisa ƙa’idojin shari’ar Musulunci.
Sakataren kwamitin, Shehu Wada Sagagi, ya shaida wa manema labarai cewa an yi hakan ne domin tabbatar da adalci.
“Bayan mun saurari ɓangarorin biyu, kwamitin zai tattauna sannan ya bai wa gwamnatin jiha shawarwari,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin masu ƙorafin sun yi barazanar kai ƙara kotu, amma ya roƙe su da su bari kwamitin Shura ya yi aikinsa.
“Muna kira ga jama’a da su ci gaba da zama cikin lumana. Kano na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewa maso Yamma, kuma wajibi ne mu kiyaye wannan zaman lafiya don ci gaban tattalin arziƙi da zamantakewa,” in ji shi.
Sagagi ya ce kwamitin ya ƙunshi manyan malamai da suka ƙware a fannin shari’ar Musulunci, kuma za su bai wa gwamnati shawarar da ta dace.
Aminiya ta ruwaito cewa, cikin tuhumar da ake yi wa Malam Triump har da kalaman ɓatanci a kan Fiyayyen Hallita, Annabi Muhammad (SAW), yin tambaya kan haihuwarsa, da kuma cewa iyayensa suna cikin wuta.
Har ila yau, masu ƙorafin sun ce yana yin wasu maganganu da suka ɗauke su a matsayin raini.
Kwamitin ya yaba wa gwamnatin jihar na bai ba shi damar warware matsalar ta hanyar tsarin Musulunci, maimakon a bari ya haddasa tashin hankali a cikin jama’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɓatanci Kwamitin Shura Malam Lawan Triumph zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
Daga Isma’il Adamu
Gwamna Dikko Radda na Jihar Katsina ya sanya hannu kan kudirin kasafin kudin jihar na 2026 na Naira Biliyan 897, makonni uku bayan gabatar da shi a gaban majalisar dokokin jihar.
Yayin rattaba hannu a Fadar Gwamnati da ke Katsina, a gaban ‘yan majalisar dokokin jihar, gwamnan ya jinjinawa majalisar bisa gaggawar amincewa da kasafin, tare da tabbatar da cewa za a aiwatar da shi yadda ya dace.
Ya bayyana cewa kashi 82 cikin ɗari na kasafin an ware shi ne ga manyon ayyuka(capital expenditure), yayin da kashi 18 cikin ɗari aka ware ga ayyukan yau da kullum(recurrent expenditure), rabo wanda ya ce ya fi abin da doka ta baya ta tanada, wadda ke bukatar kada kudaden gudanarwa su haura kashi 30 cikin ɗari.
Gwamna Radda, wanda ya bayyana kasafin a matsayin “kasafin jama’a,” ya ce an tsara shi ne daga shawarwarin da aka tattara a tarukan jin ra’ayin jama’a da aka gudanar a fadin kananan hukumomi 34 na jihar.
Yayin da yake jinjinawa ‘yan majalisar dokokin jihar bisa kyakkyawar alakar aiki da suke da ita da bangaren zartarwa, gwamnan ya bukaci kwamitocin majalisar su gudanar da aikinsu na sa ido don tabbatar da cewa an aiwatar da kasafin yadda ya kamata.
Tun da farko, yayin mika kudirin kasafin domin rattaba hannu, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar, Alhaji Nasir Yahaya, ya ce ‘yan majalisar sun duba tare da amince da kasafin cikin makonni uku, lamarin da ya sanya Katsina ta zama jihar farko da ta samu dokar kasafin kudin shekara ta 2026.