Aminiya:
2025-11-27@21:15:57 GMT

Yau Juma’a ake bikin nada sabon Olubadan na Ibadan

Published: 26th, September 2025 GMT

A yau Juma’a Gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo zai mika sandar sarauta ga sabon Olubadan na Ibadan na 44, Oba Rashid Adewolu Ladoja.

Ana sa ran Shugaba Bola Ahmed Tinubu da tsohon mataimakin Shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar za su halarci wannan gagarumin biki da aka shirya yi a Ibadan babban birnin Jihar Oyo.

Bikin da ba a taba yin irinsa a Ibadan ba

Shugaban Hadaddiyar Kungiyar Dattawa ’Yan asalin Ibadan (CCII), Cif Ajeniyi Ajewole ya ce, dukkan attajirai ’yan asalin Ibadan an dora masu haraji daga Naira miliyan 10 zuwa sama a matsayin gudunmawarsu ga wannan biki da aka fara da addu’ar rokon Allah a ranar Litinin da ta gabata.

Ya ce, “mun kammala shirin yin bukukuwan nada sabon Olubadan da ba a taba yin irin sa a baya ba, inda za mu shafe mako daya cif ana yi a wurare da lokuta daban-daban a Ibadan.

Haka kuma a matsayinsa na Attajirin mai kudi dan kasuwa da ya taba zama Sanata kuma tsohon Gwamnan Jihar Oyo ya cancanci samun wannan girmamawa a yanzu da ya zama sabon Sarki a Masarautar Ibadan mai kunshe da kananan hukumomi 11 a wannan Jiha ta Oyo”, inji shi.

Kwamitoci biyu da Kungiyar CCII ta kafa, domin tsara bikin na yau Juma’a a karkashin jagorancin Injiniya Dotun Sanusi da Cif Adegboye Adegoke sun yi bayanin cewa, an tanadi jami’an tsaro dubu 2 da aka girke a sassa daban-daban, musamman harabar babban zauren taro na Mapo da ke tsakiyar birnin, inda ake yin bikin domin tabbatar da tsaron lafiyar mahalarta da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali kafin isowa da ranar bikin da bayan kammalawa.

Aminiya ta rawaito cewa, kabilun Yarbawa, musamman ’yan asalin Ibadan daga Jihohi 19 na Arewacin kasa a karkashin jagorancin Sarkin Yarbawan Jihar Kano, Ambasada Murtala Alimi Otisese tun cikin makon jiya suka fara isowa gidajensu a sassa daban-daban na Masarautar Ibadan, domin halartar wannan gagarumin biki.

Da yake yi wa Aminiya karin haske, Ambasada Murtala Alimi Otisese a matsayinsa na mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Yarbawan Jihohin Arewa ya ce, “duka Sarakunan Yarbawan Arewa tare da iyalinsu da ‘yan uwa da abokan arziki da muke zaune a ciki da wajen Nijeriya, mun iso nan birnin Ibadan tun kafin isowar wannan rana, domin halartar wannan gagarumin bikin mika wa ubanmu, Oba Rashid Adewolu Ladoja sandan sarauta a matsayin Olubadan na 44 a Masarautar Ibadan.

Wallahi mun yi matukar farin ciki da irin bayanan da Oba Rashid Ladoja ya rika yi tun kafin isowar wannan rana, inda yake cewa, a zamanin mulkinsa za a samu ci gaba a Masarautar Ibadan da Jihar Oyo da kasa baki daya, musamman wajen lalubo hanyar kyautata tsaro a wannan sashe’’.

Ya ce, zai gayyaci bakin ’yan kasuwa na ciki da da wajen Nijeriya, domin zuba jarin kasuwanci da zai bunkasa tattalin arzikin Jihar Oyo da kasa baki daya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: a Masarautar Ibadan

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta

Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Dr Ali Larijan wanda ya ke ziyarar aiki na kwanaki uku a kasar Pakistan ya yabawa kasar saboda goyon bayan da ta bawa kasarsa a lokacin yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorawa kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Dr Ali Larijana yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Talata.  Sannan yace ya isar da sakon gaisuwa na Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khami’ae ga mutanen kasar Pakistan. Banda haka ya gana da Firai ministan kasar  Shehbaz Sharif da shugaban kasa Asif Ali Zardari da kuma kakakin majalisar dokokin kasar kasar Sardar Avaz Saadik.

A ganawar Larijani da Sharif sun tattauna kan dangantaka mai tsawo da ke tsakanin Iran da Pakisatan, da kuma bukatar a kara zurfafata.

Sharif a nasa bangaren ya bayyana cewa nan ba da dadewa waministan harkokin wajen kasar Mohammad Ishak Dar zai ziyarci Tehran inda ake saran zai rattaba hannu kan yarjeniyoyi na bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, daga ciki har da batun kammala aikin shimfida bututun gas  daga kasar Iran zuwa Pakistan. Da kuma harkokin sadarwa.

A cikin wannan shekarar ne dai kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjeniyar bunkasa kasuwanci ta dalar Amurka billion 10 a tsakaninsu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru  Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba