Aminiya:
2025-10-13@15:53:06 GMT

Babu wata jam’iyya dana ke shirin shiga — Kwankwaso

Published: 26th, September 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya aike wasiƙar neman shiga wata jam’iyya ta daban.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso ya ce babu gaskiya a labaran, kuma ya shawarci jama’a da su yi watsi da su.

’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a Masallaci a Zamfara Ganduje ya gindaya wa Kwankwaso sharadin shiga APC

“Mun samu bayanin wasu rubuce-rubucen da ke yawo a Intanet cewa mun miƙa wasiƙar neman shiga wata jam’iyya a ƙasar nan.

“Muna so mu fayyace wa jama’a cewa ba mu taɓa miƙa irin wannan wasiƙa ga kowace jam’iyya ba.

“Saboda haka mun shawarci jama’a da su riƙa neman duk wani bayani game da mu daga shafukanmu na gaskiya,” in ji shi.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da ake ta hasashen komawar Kwankwaso jam’iyyaar APC kafin zaɓen 2027.

Aminiya ta ruwaito cewa akwai alamun cewa Kwankwaso ya tattauna da Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kan yiwuwar komawa jam’iyyar mai mulki.

Majiyoyi daga APC a Jihar Kano, sun yi iƙirarin cewa Kwankwaso ya aike wa sakatariyar jam’iyyar a Abuja wasiƙa, inda ya bayyana ƙudirinsa na sake shiga jam’iyyar.

Amma Aminiya ba ta tabbatar da wannan batu ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Sai dai wata majiya daga sakatariyar APC a Abuja, ta ce Kwankwaso da shugaban jam’iyyar na ƙasa sun daɗe suna tattaunawa kan shirin sauya sheƙarsa, kuma shirye-shiryen sun yi nisa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwankwaso labaran ƙarya martani raɗi Sauya Sheƙa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

A cewarta, shirin ya taimaka wajen noman shinkafa da ta kai kimanin tan 99,452, wacce kuma kudinta ya kai kimanin Naira biliyan 13.527 tare kuma da noman rogo da ya kai kimanin tan 87,237, wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 3.925, musamman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin jihar.

 

Sai dai, ta bayyana cewa; har yanzu a jihar ba a samar da wani cikakken tsari a hukumance ba, a kan tsarin na shirin na CAF wanda hakan ke haifar wa da shirin koma baya a jihar.

 

Ta yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki a fannin bunkasa aikin noma, domin samun riba a jihar da su bayar da hadin kai wajen shiga cikin tsarin na CAF, musamman a bangaren noman shinkafa da rogo da sauran amfanin gona.

 

Kazalika, ta bukaci mahukunta a jihar da su samar da tsari a hukumance, musamman na dogon zango domin ci gaba da samar da wadataccen abinci a fadin jihar baki-daya.

 

Shi ma a nasa bangaren, jami’in shirin na jihar; Dakta Emmanuel Igbaukum ya bayyana cewa, masu ruwa da tsaki a jihar, sun nuna sha’awarsu ta shiga cikin shirin tare kuma da sanya shi a cikin tsarin jihar na samar da abinci mai gina jiki.

 

Ya kara da cewa, shirin zai kuma taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin aikin noma na jihar baki-daya.

 

A nata jawabin, Babbar Sakatariya a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, Pharm. Elijah ta bayar da tabbacin cewa; gwamnatin jihar za ta bayar da kason kudi a kan lokaci tare kuma da yin rangwame wajen sayen kayan aikin noma cikin rahusa.

 

Ta bayyana cewa, gudunmawar shirin na IFAD ya taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin tattalin arziki da kuma fannin aikin noma na jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara October 11, 2025 Noma Da Kiwo Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina October 3, 2025 Noma Da Kiwo Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo October 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa
  • Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho