Gwamnatin Kano Ta Mika Ƙorafe-Ƙorafe Kan Sheikh Lawan Triumph Zuwa Majalisar Shura
Published: 26th, September 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta karɓi ƙorafe-ƙorafe da dama da kuma martani daga ƙungiyoyin addinin Musulunci kan kalaman da Sheikh Lawan Triumph ya yi kwanan nan a jihar.
A cewar sanarwar da ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar ta fitar ta hannun mai magana da yawunsa, Musa Tanko, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince a miƙa batun ga Majalisar Shura ta Jihar Kano domin yin nazari da tattaunawa.
Ƙungiyoyin da suka shigar da ƙorafe-ƙorafen sun haɗa da Safiyatul Islam of Nigeria, da Tijjaniya Youth Enlightenment Forum, da Interfaith Parties for Peace and Development, da Sairul Qalbi Foundation, da Habbullah Mateen Foundation, da Limaman Masallatan Juma’a ƙarƙashin Qadiriyya Movement, da Kwamitin Malaman Sunnah na Kano, da kuma Multaqa Ahbab Alsufiyya.
Sakataren Gwamnati, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ya ce gwamnatin jihar ta jajirce wajen tabbatar da zaman lafiya, da haɗin kai da mutunta juna tsakanin dukkan ƙungiyoyin addini, tare da kira ga jama’ar Kano da su kasance cikin kwanciyar hankali kuma su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba tare da tashin hankali ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Lawan Triumph
এছাড়াও পড়ুন:
Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
Hukumar Tsaro ta Sibil Difens a Jihar Kano, ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a Ƙaramar Hukumar Doguwa.
Hukumar ta miƙa su ga Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), domin ci gaba da bincike da gurfanar da su a kotu.
’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a BornoKwamandan hukumar na Jihar Kano, Bala Bawa Bodinga ne, ya bayyana hakan yayin da yake magana da ’yan jarida a hedikwatar hukumar a ranar Juma’a.
Ya ce an kama mutanen ne da sanyin safiyar ranar Talata, 7 ga watan Oktoba, 2025, bayan samun sahihin bayaai.
Jami’an hukumar daga sashen Doguwa sun tare su a ƙofar Riruwai da ke Doguwa yayin da suke ɗauke da manyan jakunkuna uku cike da tabar wiwi.
Babban wanda ake zargi shi ne Yusuf Alasan, mai shekara 25, tare da abokan aikinsa biyu; Muktar Musa da Musa Sani.
Kwamandan, ya ce hukumar ta kammala binciken farko kuma ta miƙa su tare da kayan da aka kama zuwa ofishin NDLEA na Jihar Kano don yin ƙarin bincike.
Bodinga, ya ƙara da cewa NSCDC za ta ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin kawar da laifuka da tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.