An gano yarinya da aka sayar ₦3.7m a Ondo
Published: 26th, September 2025 GMT
Jami’an ’yan sanda a Jihar Ondo sun kuɓutar da wata yarinya ’yar shekara huɗu da ta ɓace tare da gano wasu masu fataucin yara da ke gudanar da ayyukan su a yankunan Jihohin Ondo, Delta da Anambra.
An fara shari’ar ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2025, lokacin da Sunday Kingsley da ke yankin Alagbaka Extension a garin Akure, ya ruwaito cewa ’yarsa Jesinta, ta ɓace ne a lokacin da take tare da mahaifiyarta Sunday Happiness.
Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, Olusola Ayanlade ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar kuma aka sanarwa manema labarai a Akure ranar Alhamis.
Sanarwar wani ɓangare na cewa: An fara shari’ar ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2025, lokacin da wani Sunday Kingsley na yankin Alagbaka Extension, a Akure ya ruwaito cewa ’yarsa mai shekara huɗu, Jesinta Sunday wacce ke zaune da matarsa, mai suna Sunday Happiness ta ɓace.
“An mayar da shari’ar zuwa Sashin kulawa, na hedkwatar rundunar ’yan sandan jihar domin gudanar da bincike mai zurfi, a ci gaba da gudanar da shari’ar, da gabatar da ƙarar a gaban Kotun Majistare ta Iyali, wanda ya kai ga tsare mahaifiyar yarinyar mai suna Nneka Onah tare da Sunday Happiness a gidan gyaran hali na Ondo kafin daga bisani a ba su beli.
Ayanlade ya bayyana cewa, a ranar 9 ga watan Yuli, 2025, mai shigar da ƙara, wani Sunday Kingsley ya kai rahoto ga ’yan sanda cewa, an gano yarinyar da ta ɓace a Asaba, Jihar Delta.
Ya ce nan take, jami’an rundunar ’yan sanda suka fara aiki, inda suka yi nasarar ƙwato yarinyar tare da dawo da ita lafiya a Akure.
Sanarwar ta kuma bayyana yadda aka kame rukunin masu safarar yara:
“Haka kuma an kama wata mata mai suna Amaka Chukwuemeka mai shekara 30, wacce ta bayyana cewa ta sayi yarinyar a kan kuɗi Naira miliyan 3 da dubu 700.
“Ta kuma bayyana cewa ƙawarta mai suna Chinaza Owoh ’yar shekara 38 ce ta gabatar da ita ga wata mata mai suna Mabel Esimai mai shekara 58, wadda ta sakar mata yarinyar da sunan raino, inda ta samar da takardu na jabu a cikin shirin da suka yi.
“Wannan binciken ya sa aka ci gaba da bankaɗo, wanda ya kai ga kama Mabel Esimai, yayin da ake yi mata tambayoyi, ta bayyana cewa ta karɓi yarinyar daga wata mai suna Chioma Okechukwu ‘yar shekara 37, tare da umarnin a samo wanda zai saya.”
Kwamishinan ’yan sandan Jihar Ondo, Adebowale Lawal ya yaba wa Sashin kula da jinsi bisa nasarar gudanar da ayyukan. Ya kuma umurci rundunar da ta ci gaba da gudanar da bincike domin bankaɗo duk masu hannu da kuma gurfanar da waɗanda ake tuhuma a gaban kuliya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Anambara bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
Daga Bello Wakili
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan harkar tsaro a duk fadin kasar, sakamakon karuwar kalubalen tsaro da ake fuskanta.
Shugaban ya ce za a dauki sabbin jami’an tsaro nan ba da jimawa ba, wadanda suka hada da na sojiin, ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro — domin karfafa matakan tsaron kasa.
A karkashin sabon umarnin, an bai wa Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ikon daukar karin jami’aaidubu ashirin, wanda hakan zai kawo yawan sabbin jami’an da za a dauka bana zuwa dubu hamsin.
Shugaban kasar ya kuma amince a yi amfani da sansanonin horas da matasa masu yi wa kasa NYSC a matsayin wuraren horaswa na wucin gadi, sakamakon gyare-gyaren da ake yi a makarantun horar da ‘yan sanda a fadin kasar.
Haka zalika Jami’an da aka cire daga ayyukan tsaron manyan mutane za su samu horo na gaggawa kafin a tura su zuwa yankunan da ke da hadari.
Shugaban ya kuma bai wa Hukumar tsaro ta DSS umarnin gaggauta tura dakaru masu horo na musamman zuwa dazuka domin yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga. A don haka, hukumar ta DSS za ta dauki karin ma’aikata don karfafa wannan aiki.
Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya su bada hadin kai ga matakan tsaron da ake dauka.
Ya yaba wa jami’an tsaro bisa ceto daliban Jihar Kebbi 24 da aka yi garkuwa da su, da masu ibada 38 a Jihar Kwara, tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da kokarin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su a Jihar Niger da sauran wadanda ke tsare.
Shugaban ya umurci Rundunar Soji ta kara zafafa ayyuka a dukkan yankunan da ake rikici, tare da jaddada muhimmancin ladabi, gaskiya da kin amincewa da cin hanci ko sakaci.
Ya mika ta’aziyya ga iyalan wadanda aka kashe a hare-haren da suka faru a Kebbi, Borno, Zamfara, Niger, Yobe da Kwara, tare da karrama jaruman sojojin da suka rasa rayukansu, ciki har da Birgediya-Janar Musa Uba.
Shugaba Tinubu ya sake tabbatar da goyon bayansa ga jami’an saro na jihohi, tare da kira ga Majalisar Dokoki ta Kasa da ta fara nazarin dokokin da za su bai wa jihohin da ke son kafa ‘yan sandan jiha damar yin hakan.
Ya shawarci gwamnatocin jihohi su sake duba tsarin kafa makarantun kwana a wuraren da ke da nisa ba tare da wadatattun matakan tsaro ba, sannan ya yi kira ga cibiyoyin addini su kara inganta tsaron wuraren ibada.
Dangane da rikice-rikicen manoma da makiyaya, Shugaban ya bukaci kungiyoyin makiyaya da su rungumi tsarin kiwo na zamani (ranching) tare da yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya ta hannun sabuwar Ma’aikatar Raya Kiwo.