An gano yarinya da aka sayar ₦3.7m a Ondo
Published: 26th, September 2025 GMT
Jami’an ’yan sanda a Jihar Ondo sun kuɓutar da wata yarinya ’yar shekara huɗu da ta ɓace tare da gano wasu masu fataucin yara da ke gudanar da ayyukan su a yankunan Jihohin Ondo, Delta da Anambra.
An fara shari’ar ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2025, lokacin da Sunday Kingsley da ke yankin Alagbaka Extension a garin Akure, ya ruwaito cewa ’yarsa Jesinta, ta ɓace ne a lokacin da take tare da mahaifiyarta Sunday Happiness.
Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, Olusola Ayanlade ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar kuma aka sanarwa manema labarai a Akure ranar Alhamis.
Sanarwar wani ɓangare na cewa: An fara shari’ar ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2025, lokacin da wani Sunday Kingsley na yankin Alagbaka Extension, a Akure ya ruwaito cewa ’yarsa mai shekara huɗu, Jesinta Sunday wacce ke zaune da matarsa, mai suna Sunday Happiness ta ɓace.
“An mayar da shari’ar zuwa Sashin kulawa, na hedkwatar rundunar ’yan sandan jihar domin gudanar da bincike mai zurfi, a ci gaba da gudanar da shari’ar, da gabatar da ƙarar a gaban Kotun Majistare ta Iyali, wanda ya kai ga tsare mahaifiyar yarinyar mai suna Nneka Onah tare da Sunday Happiness a gidan gyaran hali na Ondo kafin daga bisani a ba su beli.
Ayanlade ya bayyana cewa, a ranar 9 ga watan Yuli, 2025, mai shigar da ƙara, wani Sunday Kingsley ya kai rahoto ga ’yan sanda cewa, an gano yarinyar da ta ɓace a Asaba, Jihar Delta.
Ya ce nan take, jami’an rundunar ’yan sanda suka fara aiki, inda suka yi nasarar ƙwato yarinyar tare da dawo da ita lafiya a Akure.
Sanarwar ta kuma bayyana yadda aka kame rukunin masu safarar yara:
“Haka kuma an kama wata mata mai suna Amaka Chukwuemeka mai shekara 30, wacce ta bayyana cewa ta sayi yarinyar a kan kuɗi Naira miliyan 3 da dubu 700.
“Ta kuma bayyana cewa ƙawarta mai suna Chinaza Owoh ’yar shekara 38 ce ta gabatar da ita ga wata mata mai suna Mabel Esimai mai shekara 58, wadda ta sakar mata yarinyar da sunan raino, inda ta samar da takardu na jabu a cikin shirin da suka yi.
“Wannan binciken ya sa aka ci gaba da bankaɗo, wanda ya kai ga kama Mabel Esimai, yayin da ake yi mata tambayoyi, ta bayyana cewa ta karɓi yarinyar daga wata mai suna Chioma Okechukwu ‘yar shekara 37, tare da umarnin a samo wanda zai saya.”
Kwamishinan ’yan sandan Jihar Ondo, Adebowale Lawal ya yaba wa Sashin kula da jinsi bisa nasarar gudanar da ayyukan. Ya kuma umurci rundunar da ta ci gaba da gudanar da bincike domin bankaɗo duk masu hannu da kuma gurfanar da waɗanda ake tuhuma a gaban kuliya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Anambara bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta
Majiyar asbitoci a yankin gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye ta bada labarin cewa HKI ta kashe falasdinawa 19 a safiyar yau Asabar duk tare da cewa an fara tsagaita budewa juna wuta a yankin.
Tashar talabian ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar asbitoci a gaza na cewa bayan janyewar sojojin HKI daga wasu yankuna a Gazar sun zakulo gawakin falasdinawa 155 daga burbushin gine-gine wadanda HKI ta rusa a bayan.
Banda haka an kawo masu sabbin gawaki 19 wadanda sojojin HKI suka kashe a safiyar yau duk tare da cewa an fara yarjeniyar dakatar da budewa juna wuta.
Labarin ya kara da cewa gawaki 135 daga cikin 155 da aka kawo na kashe-kashen baya ne. Labarin ya kara da cewa an kashe mutane 16 a lokacinda wani jirgin yakin HKI ya kai hari kanwani gida a Khan Yunus a safiyar yau Asabar. Wadanda suka mutun dangi guda ne.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza October 11, 2025 Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci